Tsohon ministan Isra'ila ya zargi Netanyahu da kisan gilla a Gaza
Tsohon ministan tsaron Isra'ila, Moshe Ya’alon, ya ce gwamnatin Benjamin Netanyahu ta kama hanyar aiwatar da kisan gilla a arewacin Gaza.
Ya ce hakan zai iya kawo rugujewar ƙasar.
Kalaman nasa da suka zo da ba zata sun janyo suka daga ministocin gwamnatin Mr Netanyahu, waɗanda suka nemi ya janye kalaman nasa.
Mr Ya’alon dai ya yi fice wajen sukar firaiministan Isra'ila.
Isra'ila wadda ta umarci dubban Falasɗinawa su koma arewacin Gaza, ta kuma riƙa yin luguden wuta ta sama a yankin, ta musanta zargin da ake mata na kisan gilla.
Rahotannin da ke fitowa daga yankin sun ce wani sabon harin Isra'ila ya kashe mutane da dama tare kuma da jikkata wasu.
Isra'ila dai ta ce za ta yi bincike a kan lamarin.

















