Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce sojojin Amurka sun kai hari tsibirin Kharg na Iran mai ɗimbin arzikin makamashi.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaba Trump ya ce ''Dakarun Amurka sun ƙaddamar da wani babban harin bom a tarihinsu na yaƙi a Gabas ta Tsakiya in da suka shafe duk wani kayan sojin Iran da ke tsibirin Kharg, mai ɗimbin arziki''.
"Na zaɓi kada na lalata cibiyoyin man fetur da ke tsibirin. Amma idan Iran ko wani suka yi wani abu da zai kawo tsaikon wucewar jiragen dakon man fetur ta mashigar Hormuz, zan yi gaggawar duba shawarar kai wa cibiyoyin man fetur da ke tsibirin hari,'' in ji shugaban na Amurka.
Masu shairhi na cewa kashi 90 cikin 100 na man da Iran ke fitarwa zuwa kasuwannin duniya daga tsibirin yake.
To sai dai a martanin da ta mayar, rundunar sojin Iran ta ce za ta mayar - da duka cibiyoyin mai da na makamashi mallakin kamfanonin da ke aiki da Amurka - zuwa toka, idan ahr Amurka ta kuskura ta kai hari kan cibiyoyin manta da ke tsibirin, kamar yadda kafofin yaɗa labaran Iran suka ruwaito.