Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 14/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 14/03/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Labarai da dumi-dumi, An ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami zuwa Iara'ila - IDF

    Rundunar sojin Ira'ila ta ce Iran ta harba mata sabbin hare-haren makamai masu linzami.

    Wannan dai shi ne hari na farko cikin sa'o'i 10.

    Sojojin na Isra'ila tabbatar da cewa an bai wa mutane damar ci gba da zama a wurare masu tsaro, amma ta buƙaci al'umma su ci gaba da bin shawarwarin kariya.

  2. Hotunan yadda hayaƙi ke tashi a faɗin Gabas ta Tsakiya

    Yaƙin Iran na ƙera jefa wasu sassan yankin Gabas ta tsakiya cikin matsala da fargaba yayin da kae ganin hayaƙi na tashi a wasu biranen sassan sakamakon jerin hare-hare.

    A ƙasar Haɗaɗdiyar Daular Larabawa an ga hayaƙi na tashi a saman tahar jiragen ruwa ta Fujairah, ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin ajiyar man fetur a yankin Gabas ta Tsakiya, bayan da jirgi maras matuƙi ya kai hari kan tashar.

    Can ma a kudancin Lebanon wani gini ya kama da wuta a unguwar Haret Saida na Sidon, a kudancin, bayan harin Isra'ila.

    Haka hare-hare sun lalata wasu gidaje a Isra'ila.

    Rufin wani gini a Shoham da ke tsakiyar Isra'ila ya ruguje bayan hare-hare.

    Sojojin Isra'ila sun ce sun gano makamai masu linzami da aka harba cikin ƙasar cikin dare

  3. Isra'ila ta kai hari cibiyar adana makamai a kudancin Lebanon

    Sojojin Isra'ila sun ce sun kai hari cibiyar adana makamai a kudancin Lebanon.

    Sojojin Ira'ila sun ce sun kashe mayaƙan Hezbollah da ke jigilar makamai zuwa cibiyar.

    Cikin wata sanarwa da suka wallafa a shafinta na sada zumunta, sojojin na Isra'ila sun ce ''Sojojin saman Isra'ila sunlalata cibiyar tare da kashe mayaƙan Hezbollah''.

  4. Hamas ta nemi Iran da daina kai wa maƙabtan ƙasashe hari

    Ƙungiyar Hamas ta Falasɗinawa ta yi kira ga Iran ta dakatar da ka hare-hare makbatan ƙasashen.

    Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta jaddada cewa Iran na da ƴancin kare kanta daga hare-haren Isra'ila da Amurka.

    ''Kuna da ƴancin kare kanku ta dukla hanyar da kuke da ita, bida dokokin duniya, amma muna kira ga ƴan'uwanmu na IRan du daina kai hare-hare zuwa makwabtan ƙasashe'', a cewar sanarwar.

    Tun bayan fara yaƙin Isra'ila da Amurka kuma Iran a gefe guda, Tehran ta riƙa kai hare-hare kan wasu ƙasashen yankin Gabas ta Tsakiya da kuma sansanonin sojin Amurka da ke ƙasashen.

  5. An kai hari ofishin jakadancin Amurka a Bagadaza

    Wani hariin makami mai linzami ya faɗa kan ofishin jakadancin Amurka a Bagadaza, babban birnin Iraƙi.

    Kamfanin dillacin labarai na Reuters ya ambato wasu majiyoyi na cewa ginin ya kama da hayaƙi, sai dai bai yi ƙarin bayani ba.

    Kamfanin dillacin labarai na AP ya bayar da rahoton cewa harin makami mai linzami ya faɗa ne kan filin da jirage masu saukar ungulu ke sauka da tashi a harabar ofishin jakadancin.

    To amma kamfanin AFP ya ce jirgi maras matuƙi ya kai hari ofishin.

    Harin ya auku ne jim kaɗan bayan an kashe wasu maya ƙa biyu masu goyon bayan Iran a wasu hare-hare a binrin na Bagadaza, kamar yadda AFP ya ambato wasu majiyoyi na cewa.

    Za mu kawo muku ƙarin bayani game da harin idan mun samu

  6. Amurka ta kai hari tsibirin Kharg na Iran, mai ɗimbin arziki

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce sojojin Amurka sun kai hari tsibirin Kharg na Iran mai ɗimbin arzikin makamashi.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaba Trump ya ce ''Dakarun Amurka sun ƙaddamar da wani babban harin bom a tarihinsu na yaƙi a Gabas ta Tsakiya in da suka shafe duk wani kayan sojin Iran da ke tsibirin Kharg, mai ɗimbin arziki''.

    "Na zaɓi kada na lalata cibiyoyin man fetur da ke tsibirin. Amma idan Iran ko wani suka yi wani abu da zai kawo tsaikon wucewar jiragen dakon man fetur ta mashigar Hormuz, zan yi gaggawar duba shawarar kai wa cibiyoyin man fetur da ke tsibirin hari,'' in ji shugaban na Amurka.

    Masu shairhi na cewa kashi 90 cikin 100 na man da Iran ke fitarwa zuwa kasuwannin duniya daga tsibirin yake.

    To sai dai a martanin da ta mayar, rundunar sojin Iran ta ce za ta mayar - da duka cibiyoyin mai da na makamashi mallakin kamfanonin da ke aiki da Amurka - zuwa toka, idan ahr Amurka ta kuskura ta kai hari kan cibiyoyin manta da ke tsibirin, kamar yadda kafofin yaɗa labaran Iran suka ruwaito.

  7. Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Isra'ila

    Rundunar dakarun juyin juya hali na Iran sun ta ce ta ƙaddamar da hare-hare karo na 48 kan Isra'ila, kamar yadda kafofin yaɗa labaran Iran suka bayyana.

    Kamfanin dillancin labarai na Jamhuriyar Musulunci ya ce an ƙaddamar da jerin hare-haren tare da na ƙungiyar Hezbollah da ke Lebanon.

    Yaƙi tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka a gefe guda ya ɓarke ne mako biyu da suka gabata bayan da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar da hare-hare kan Iran, lamarin da ya yi sanadin kisan jagoran addini a Iran.

    A matsayin martani Iran ta ƙaddamar da jerin hare-hare kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya.

  8. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu an sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.