Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya, Juma'a, 28/02/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sassan duniya kai tsaye, na Juma'a, 28/02/2025

Taƙaitattu

  • Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗin 2025
  • An ga watan Ramadan a Najeriya
  • An yi cacar baki tsakanin Donald Trump da Zelensky
  • An ga watan azumin Ramadan na 2025 a Saudiyya
  • Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Annur Muhammad da Isiyaku Muhammed

  1. Shugabannin Turai sun nuna goyon bayansu ga Ukraine

    Shugabannin ƙasashen Turai sun yi ta wallafa saƙonnin goyon bayansu ga Mista Zelensky bayan cacar-bakinsa da Mista Trump.

    Shugaba Macron na Faransa - wanda ya gana da Mista Trump a farkon makon nan - ya ce a bayyane take Rasha ce ta tsokani Ukraine kuma yana da kyau a mutunta mutanen da suka riƙa faɗa don kare kansu.

    Shi ma shugaban Poland, Donald Tusk, ya gaya wa Ukraine cewa 'Muna tare da ku.'

    A Amurka, 'yan jam'iyyar Democrat a majalisar dokokin ƙasar sun zargi Mista Trump da mataimakinsa JD Vance da yi wa shugaban Rasha Vladimir Putin aiki.

    Wakilin BBC a ma'aikatar harkokin wajen Amurka, ya ce wannan ya zama taɓarbarewar dangantaka tsakanin Amurka da Ukraine da masu mara mata baya a Turai, kuma da wuya a sake gina su a nan kusa.

  2. Zelensky ya gode wa Trump da Amurka

    Zelensky

    Asalin hoton, EPA

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya gode wa takwaransa na Amurka har sau da yawa bayan ganawarsu a fadar gwamnatin Amurka.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, jim kaɗan bayan barinsa fadar White House, shugaban na Ukraine ya ce ''Na gode Amurka, na gode da goyon bayan da kuka ba mu, na kuma gode muku bisa ziyarar da na kawo.

    (A lokacin ganawar wadda aka yi ta cacar-vaki, Mista Trump ya faɗa wa Zelensky cewa ya kamata ya zama mai ''godiya'' kan goyon bayan da Amurka ke bai wa ƙasarsa, yayin da mataimakina, JD Vance ya zargi shugaban na Ukraine da rashin furta kalmar 'ma gode' a lokacin ganawar.)

    Cikin saƙon nasa Shugaba Zelensky ya ce Ukraine na buƙatar kawo ƙarshen yaƙin domin samun zaman lafiya, ya kuma ƙasarsa na aiki domin cimma hakan.

  3. Zelensky ya fice daga fadar White House a fusace

    Zelensky

    Shugaba Zelensky na Ukraine ya bar fadar White House bayan da tattaunawar kawo ƙarshen yaƙi da Rasha ta watse a fusace.

    A wata tattaunawa ta ban mamaki a gaban kafafen yaɗa labaran duniya, shugaban na Amurka ya faɗa wa takwaransa na Ukraine cewa yana caca da abin da ya kira 'yaƙinn duniya na uku'.

    Ya ce Volodymyr Zelensky bai nuna godiya kan goyon bayan da Amurka ke bai wa Ukraine, kuma ya kamata ya ƙulla yarjejeniya da Rasha "ko kuma mu cire hannunmu".

  4. An faɗa wa Zelensky ya fice daga fadar White House

    Zelesnky

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanai na cewa wasu daga cikin jami'an gwamnatin Amurka sun buƙaci shugaban Ukraine ya fice daga fadar, bayan acar bakinsa da shugaba Trump.

    Kafar yaɗa labarai ta CBS, abokiyar ƙawancen BBC ta ruwaito cewa, wakilan Ukraine sun bar Ofishin shugaban ƙasar zuwa “ɗaki da aka ware”.

    A can ne mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mike Waltz da sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio suka ce wakilan na Ukraine su bar fadar shugaban ƙasar.

    An dai soke taron manema labarai da aka shirya yi tare da Zelensky da Trump jim kaɗan bayan taron ganawar tasu.

  5. Me ke faruwa idan intanet ɗinku ta katse?

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Ko kun san me ya ke faruwa idan sabis ɗin wayarku ya ɗauke? Hakan na iya samun asali daga wani aiki da ake yi a tsakiyar teku.

    BBC ta bi wani jirgin ruwa da ke irin wannan aiki, domin ganin yadda na'urorinku ke samun sabis.

  6. Trump zai mayar da turancin Ingilishi harshen hukuma a Amurka

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Kafofin yaɗa labaran Amurka sun ce shugaban ƙasar Donald Trump zai sanya hannu kan dokar da za ta mayar da turancin Ingilishi a matsayin harshen hukuma a faɗin Amurka.

    Yayin da turancin Ingilin ya kasance harshen da aka fi magana da shi a ƙasar, Amurkawa na amfani da wasu harasan, yayin da miliyoyi ke magana da harshen Sifaniyanci a gidajensu.

    A lokacin yaƙin neman zaɓensa a shekarar da ta gabata, Mista Trump ya soki yadda ake amfani da harasa daban-daban a ƙasar.

    Idan shugaban ya sanya wa dokar hannu, zai kasance karo na farko da Amurka ta ayyana harshen gudanar da gwamnati a hukumance a matakin tarayya.

    Kuma dokar za ta kawo ƙarshen wani tsari da ƙasar ta ɗauka a shekarun 1990 - wanda tsohon shugaban ƙasar, Bill Clinton tya ɓullo da shi - na buƙatar da hukumomin gwamnatin tarayya su tallafawa waɗanda ke magana harasan da ba Ingilishi ba.

  7. Gwamnatin Senegal za ta gurfanar da Macky Sall a gaban kotun

    Macky Sall

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Senegal ta ce za ta gurfanar da tsohon shugaban ƙasar, Macky Sall bayan da ofishin babban mai binciken kuɗi na ƙasar ya ce ya gano wasu kura-kurai a takrdun ajiyar kuɗin ƙasar lokacin da yake kan mulki.

    Kakakin gwamnatin ƙasar ya ce Mista Salla ne ke da hannu dumu-dumu wajen aikata kura-kuran, don haka dole ya fuskanci hukunci.

    Macky Sall dai na zaune a ƙasar Morocco tun bayan da ya sauka daga karagar mulkin ƙasar da ya shafe shekara 12 yana kai.

  8. Jikin fafaroma ya tsananta - Fadar Vatican

    Fafaroma Fransis

    Fadar Vatican ta ce jikin Fafaroma Fransis - wanda aka kwantar a asibiti makonni biyu da suka wuce saboda cutar sanyin haƙarƙari ta nemoniya - ya sake tsananta.

    Fadar Vatican ɗin ta ce fafaroman mai shekara 88 na fama da wahalar numfashi.

    Sai dai ta ce ana taimaka masa, wajen yin numfashin.

  9. An ga watan Ramadan a Najeriya

    Sarkin Mausumin Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar mai alfarma sarkin Musulmin Najeriya, ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan da maraicen ranar Juma'a.

    Cikin wata sanarwa da Sarkin Musulmin, Sa'ad Abubakar lll ya karanta a fadarsa, ya ce an ga watan a sassan ƙasar daban-daban.

    Don haka ne ya ayyana ranar Asabar 1 ga watan Maris a matsayin 1 ga watan Ramadan 1446.

    Tuni dai hukumomin Saudiyya suka sanar da ganin watan a ƙasar, inda suka ayyana gobe Asabar a matsayin ɗaya ga watan Ramadan a Saudiyya.

  10. Vance ya ce Zelensky ba ya 'girmama mutane'

    Trump da Zelensky

    An ci gaba da cacar baki tsakanin shugaba Trump da takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelensky da kuma mataimakin shugaban Amurka, JD Vance a fadar White House.

    Yayin da mayar wa JD Vance martani Shugaban Zelensky ya ce akwai 'abubuwa da dama'' da suka faru bayan fara yaƙi tsakanin Rasha da Ukraine a 2014.

    "Na sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a 2019'', a cewar Zelensky, inda ya ƙara da cewa yana da yakinin aiwatar da yarjejeniyar, amma sai Putin ya wargazata, inda ya ƙaddamar da mayaya kan Ukraien a 2022.

    "Bai kamata ya yi haka ba, wace irin diplomasiyya ce wannan? Kai, JD [Vance], kana magana a kan wannan?

    Daga nan sai Vance ya mayar da martani da ce: "Amma sai nake ganin ba girmamawa ka zo fadar shugaban ƙasa sannan ka yi ƙoƙarin yanke hukunci a gaban kafofin yaɗa labaran Amurka.

  11. An yi cacar baki tsakanin Donald Trump da Zelensky

    Trump da Zelenky

    Cacar-baki ta kaure tsakanin shugaban Amurka, Donald Trump da takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelensky a fadar White House, inda shugaban Amurkan ya fada wa takwaransa na Ukraine cewa ya ƙulla yarjejeniya da Rasha "ko kuma mu fita".

    Cikin fushi Shugaba Trump ya ce Zelensky bai gode wa Amurka kan tallafin soji da na siyasa ba da ta bai wa Ukraine ɗin ba.

    Mista Trump ya kuma zargi Zelensky da yin 'caca da yaƙin duniya na uku'.

    Ana sa ran shugabannin biyu za su rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta bai wa Washington damar mallakar mai da iskar gas da wasu ma'adinan Ukraine, wadda Donald Trump ya bayyana a matsayin mai kyau ga Amurka.

    Tun da farko, Mista Zelensky ya ce yana da matuƙar muhimmanci Amurka ta ba da garantin tsaro ko goyon baya, domin dakarun wanzar da zaman lafiya su sami damar tabbatar da tsaro.

  12. Zelensky ya isa Amurka domin ganawa da shugaba Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya tarbi takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelensky a fadar White House

    Zelensky na ziyarar ne domin buƙatar Amurka ta goyi bayan ƙasarsa kan mamayar Rasha.

    Shugabannin za su tattauna batun ko Amurka za ta bai wa Ukraine tabbacin tsaro, kamar tsaron sojin sama, don tabbatar da yiwuwar yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Ukraine da Rasha

    Ana kuma sa ran shugabannin biyu za su sanya hannu kan yarjejeniyar da za ta bai wa Amurka damar haƙar man fetur da gas ɗin Ukraine.

    A ranar Alhamis Shugaban Amurka ya bayyana Zelensky a matsayin jarumi, bayan ya kira shi mai kama karya.

  13. Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗin 2025

    Shugaba Tinubu

    Asalin hoton, Bayo Onanuga/X

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗin ƙasar na 2025 da ya kama naira tiriliyan 54.99

    Kasafin kuɗin na wannan shekara ya zarta na shekarar da ta gabata - wanda aka yi a kan naira tiriliyan 27.5 - da kashi 99.96 cikin 100.

    Shugaban ya sanya hannu kan kasafin ranar Juma'a a fadarsa da ke Abuja.

    An dai ƙara yawan kasafin na farko da shugaan ya aikewa majalisa na naira tiriliyan 49.7.

    A ranar 13 ga watan Fabrairun da muke ciki ne majalisar dokokin ƙasar ta amince da kasafin, bayan muhawara a kansa.

    An dai tsara kashe naira tiriliyan 14.32 wajen biyan bashi, inda manyan ayyuka za su laƙume naira tiriliyan 23.96.

  14. Amurka ta dakatar wasu kuɗaɗen tallafi da take ba mu - UNICEF

    talafi

    Asalin hoton, Unicef

    Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya ce Amurka ta dakatar da wasu kuɗaɗen tallafin ayyukan jin ƙai da ci gaban al'umma da Unicef ɗin ke yi a wasu sassan duniya.

    UNICEF, ya yi gargaɗin cewa dakatarwar da zai yi ya shafi kashi 90 cikin 100 na kuɗaɗen tallafin da Amurka ke bai wa Asusun wajen gudanar da ayyukansa, wanda kuma yin hakan zai shafi huldar yara da kuma janyo mutuwarsu da dama.

    Asusun ya ce tuni matakin gwamnatin Trump na dakatar da ayyukan jin kai a ƙasashen waje ya shafi ayyukansa da dama ciki har da rufe asibitoci a Haiti da kuma rage kashe kuɗi a ɓangaren ilimi da asusun ke yi ga yara a Lebanon.

    Amurka dai na samar da kusan kashi 47 cikin 100 na kuɗaɗen agaji ga ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a 2024.

  15. Isra'ila na buƙatar tsawaita kashin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta - Rahotonni

    Wata majiya daga jami'an tsaron Masar ta ce wakilan Isra'ila da ke halartar tattaunawar mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wata a Gaza na ƙoƙarin tsawaita matakin farkon na yarjejeniyar da mako shida.

    Wakilai daga Isra'ila da Hamas da Qatar da kuma Amurka sun haɗu a yau Jumma'a domin fara tattaunawa a kan kashi na biyu na yarjejeniyar - wadda ake kyautata tsammanin za ta kawo ƙarshen yaƙin Isra'ila da Hamas gaba ɗaya.

    Bayanai sun ce Hamas ba ta goyon bayan tsawaita kashin farko na yarjejeniyar inda ta buƙaci aje ga zagaye na biyu na yarjejeniyar.

  16. An ga watan azumin Ramadan na 2025 a Saudiyya

    Saudiyya

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni na cewa an ga jinjirin watan azumin Ramadan a ƙasar Saudiyya, a yau Juma'a, 28 da watan Fabrairu.

    Shafin Inside the Haramain ne ya ruwaito hakan, inda ya ruwaito cewa, "an ga jinjirin watan Ramadan na shekarar 1446 wato shekarar 2025 a Saudiyya."

    Sanarwar ta ƙara da cewa gobe Asabar, 1 ga watan Maris ne za a fara azumin bana.

  17. Halin da ƴan kasuwar Masaka ke ciki bayan gobarar da ta ƙone kasuwa

    Masaka

    Kasuwar Masaka da ke ƙaramar hukumar Karu a jihar ta Nasarawa, na daya daga cikin kasuwar da ta fuskanci gobara a baya-bayan nan.

    Tun bayan da aka samu if'tila'in gobara da ya cinye kusan kashi 90 na kasuwar Masaka da ke Karu a jihar ta Nasarawa, yan kasuwar ke fuskantar tsananin matsin tattalin arziki wanda yawancinsu ƙananan ƴan kasuwa ne masu naman na sawa a baka.

    A yanzu dai a rana suke kasa hajarsu kana suna masu jiran mataki na gaba da gwamnatin jihar ta Nasarawa za ta ɗauka kan kasuwar, kasancewar kimanin watanni biyu kenan ba a ji daga gwamnatin ba.

    To sai dai mai taimaka wa gwamnan jihar kan ahrkokin yaɗa labarai, Malam Ibrahim Addra ya ce suna sane da yanayin kuma gwamnati na yin iya bakin ƙoƙarinta wajen goge musu hawayensu.

    Masaka
    Masaka
    Masaka
    Masaka
    Masaka
  18. Yadda Firaministan Burtaniya ya yi wa Kemi Badenoch wankin babban bargo

    Burtaniya

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaiministan Birtaniya Keir Starmer ya yi wa jagorar ƴan adawan Burtaniya, Kemi Badenoch wankin babban bargo a cikin raha, inda ya bayyana ta da mai neman suna da ɗaukaka ta ƙarfi da yaji.

    Lamarin ya faru ne a lokacin da firaministan ke bayyana kasafin kuɗi, inda yake amsa tambayoyi daga ƴan majalisa.

    A game da kuɗaɗen da Burtaniya ke kashewa wajen agaji a ƙasashen waje ne Kemi ta ce ta ji daɗin yadda ya yi amfani da shawarar da ta aika masa.

  19. Manyan kifaye sun kashe masu ninƙaya, 'yan Rasha biyu a tekun Philippines

    Manyan kifaye a ruwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu masu ninƙaya biyu 'yan ƙasar Rasha sun mutu a Philippines, inda aka ƙwato gawar ɗaya daga cikinsu daga tarin wasu manyan kifaye na shak da ke cin gawarsa.

    Mutanen biyu na tare ne da wasu 'yan yawon buɗe idanu biyu da kuma jagoransu inda suka je ninƙaya a ɗan ƙaramin tsibirin Verde.

    Igiyar ruwa mai ƙarfi ce ta raba mutanen a lokacin da suke ninƙaya. Ruawa ya ci ɗaya daga cikin mutanen, yayin da ɗayan aka same shi a tsakanin manyan kifayen na shak suna cin jikinsa.

    Sun cicci hannun mutumin ɗaya. Ba a sani ba ko ya mutu ne kafin ko kuma bayan sun kaimasa hari.

  20. Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

    Fubara

    Asalin hoton, RIVERS STATE GOVERNMENT PRESS

    Kotun Ƙolin Najeriya ta umarci babban akanta da babban bankin ƙasar wato CBN na Najeriya da su dakatar da kason kuɗin jihar Rivers, har sai gwamnan jihar ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban halastacciyar majalisar jihar.

    Alƙalan kotun su biyar ne suka yanke wannan hukuncin, inda kotun ta ce Martins Amaewhule ne sahihin shugaban majajlisar.

    Wannan ya kawo ƙarshen lokaci mai tsawo da aka ɗauka ana shari'a tsakanin ɓangarorin biyu kan rikita-rikitar siyasa a jihar.

    Haka kuma ana ganin wannan matakin a matsayin wata nasara ga ɓangaren Ministan Abuja, Nyesome Wike, kan Gwamnan jihar, Sim Fubara.

    Mai shari'a Emmanuel Agim ne ya karanta hukuncin, inda ya ce, "muna umartar Babban Bankin Najeriya CBN da Babban Akanta na Najeriya da su dakata da tura kuɗin kason jihar Rivers har sai gwamnan ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban majalisar jihar ƙarƙashin Martin Amaewhule," kamar yadda ya bayyana.

    A gefe guda kuma, a wata shari'ar daban, kotun ƙolin ta soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka yi a ranar 5 ga Oktoban 2024.

    Mai shari'a Jamilu Tukur, ya ce zaɓen wanda hukumar zaɓen Rivers mai zaman kanta ta shirya, ya saɓa da sashe na 150 na kundin tsarin zaɓe na ƙasar.