Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni na musamman dangane da muhimman abubuwan da ke wakana a Najeriya da sassan duniya a ranar 26/12/2025.

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR

  1. Muna maraba da duk haɗin gwiwa da zai kawo ƙarshen matsalar tsaro - Gwamnatin Sokoto

    Ahmed Aliyu

    Asalin hoton, Ahmed Aliyu

    Gwamnatin jihar Sokoto ta tabbatar da harin da aka kai a wasu sassan ƙananan hukumomin jihar, wanda Amurka ta ce ta kai kan mayaƙan IS.

    Gwamnatin ta ce an kai harin ne a jiya Alhamis, inda ta ce an yi haɗin gwiwa ne tsakanin sojojin Amurka da na Najeriya wajen ƙaddamar da harin, wanda ta ce ba a rasa rai ba.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Abubakar Bawa ya fitar, ya ce, "Ba za iya tantance haƙiƙanin sakamakon harin ba a cikin ƙanƙanin lokaci, saboda har yanzu muna jiran cikakken rahoton aikin na musamman," in ji sanarwar.

    Sai dai sanarwar ta bayyana cewa babu fararen hula da harin na garin Jabo ya kashe ko ya jikkata.

    "Gwamnatin Sokoto na maraba da duk wani aikin haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da wata ƙasa ko wasu masu ruwa da tsakiya domin magance matalolin tsaro da sauran laifuka a jihar."

    Sanarwar ta ƙara da cewa a shekara biyu da suka gabata, gwamntin jihar ta yi ƙoƙarinta wajen magance matsalar ta hanyar ba jami'an tsaro duk goyon bayan da suke buƙata domin su gudanar da aikinsu da kyau."

    A ƙarshe gwamnatin jihar ta yi kira ga mazauna yankunan da abin ya shafa da su ci gaba da ba gwamnatin tarayya da ta jiha hadin kai ta hanyar fitar da bayanan sirri ga jami'an tsaro, "domin hakan ne zai taimaka wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa. Sannan mu ci gaba da addu'ar neman agajin Allah wajen magance matsalar."

  2. Mun kusa samun tabbacin tsaro daga Amurka - Ukraine

    Ukraine

    Asalin hoton, EPA

    Shugaba Zelensky na Ukraine ya ce akwai kashi 99 cikin 100 na yarjejeniyar kawo karshen yaki tsakanin kasar da Ukraine wadda Amurka ta gabatar.

    Da yake jawabi bayan sanar da ganawar da za su yi da shugaba Trump na Amurka nan ba da jimawa ba, Mr Zelensky ya ce an kusan kammala batun bai wa Ukraine tabbacin tsaro, wanda hakan na daga cikin bukatun da Ukraine ta gabatar kan tsoron Rasha ka iya takewa.

    Shugaban na Ukraine ya kara da cewa, ya na son a matsawa Moscow lamba a lokacin tattaunawar da tabbatar da ta mutunta daftarin yarjejeniyar.

    Sai dai kawo yanzu babu tabbacin Rasha za ta amince da wata yarjejeniya, duk da jami'anta na cewa har yanzu su na tattaunawa da Amurka.

  3. Gwamnatin Najeriya ce ta fi dacewa da jan ragamar tsaron ƙasar - Shehu Sani

    ShehuSani

    Asalin hoton, @ShehuSani

    Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani ya ce dole Najeriya ta ɗauki alhaki tare da jan ragamar harkokin tsaron ƙasar da kanta.

    Shehu Sani ya bayyana haka ne a matsayin martani kan hare-haren da Amurka ta ƙaddamar a sassan jihar Sokoto da Kwara a Najeriya.

    A wani rubutun da ya yi a X, Shehu Sani ya kuma sake nanata cewa matsalolin tsaron Najeriya ba su da wata alaƙa da addini.

    A cewarsa, "idan har da gaske hare-haren Amurka a Najeriya akwai amincewar gwamnatin ƙasar, to babu matsala," in ji shi, sannan ya ƙara da cewa ƴanbindiga daɗi na ƙasar sun zama barazana ga tsaron ƙasar.

    "Amma maganar cewa ƴan ta'addan nan suna harin wani addini ne guda ɗaya ne kawai ba gaskiya ba ce. Amma duk da haka, tsaron ƙasarmu ya rataya ne a kanmu, ba a hannun Amurka ba ko wata ƙasa daban ba. Za su iya taimaka mana, amma ba za su iya magance mana matsalarmu ba."

  4. Isra'ila ta ba sojoji umarni kai samame a Yamma da Kodin Jordin

    Netanyahu

    Asalin hoton, EPA

    Ministan tsaron Isra'ila, Israel Katz ya ce ya bai wa sojoji umarnin kai samammen gaggawa kauyen Qabatiya da ke yamma da gabar kogin Jordan, bayan abin da ya kira harin ta'addanci.

    'Yansanda a arewacin Isra'ila sun ce wani Bafalasdine ya kashe mutum biyu a harin da suka kira na ta'addanci.

    Maharin ya makure wani dattijo mai shekara 68, tare da banke shi da mota kafin daga bisani ya farwa wata yarinya mai shekara 19 inda ya daba mata wuka.

    Sanarwar da ofishin ministan tsaron Isra'ilar ta fitar, ta ce jami'an tsaro na aiki tukuru domin dakile duk wata barazana, za kuma su yi mai yiwuwa wajen murkushe duk wani dan ta'adda, da kai hari kan ababen more rayuwa da ke kauyen na Qabatiyya da ake kyautata zaton maharin mazaunin can ne.

  5. Ƙaramar hukumar Offa ta tabbatar da fashewar bam

    Offa

    Asalin hoton, BBC grab

    Ƙaramar hukumar Offa ta jihar Kwara da ke arewa ta tsakiyar Najeriya ta tabbatar da fashewar wani bam a garin na Offa a safiyar yau Juma'a.

    A wata sanarwa da sakataren watsa labaran shugaban ƙaramar hukumar, Abiola Azeez Babatunde ya fitar, ya ce wani abu ne da ake tunanin bam ya fashe a garin.

    "Mun samu labarin fashewar wani abu mai kama da bam a kusa da filin idin Offa a ranar 25 ga watan Disamna. Tuni jami'an tsaro suka rufe yankin."

    Sanarwar ta ƙara da cewa shugaban ƙaramar hukumar Suleiman Olatunji Omituntan da mai ba gwamnan shawara kan harkokin siyasa Femi Agbaje Whyte da shugaban ofishin ƴansanda na yankin suka ziyarci wurin domin gane wa idonsu abin da ya faru.

    Shugaban ƙaramar hukumar ya yi kira ga al'umma su kwantar da hankalinsu, "sannan muna kira ga al'umma da su riƙa tantance bayanai domin su guji yaɗa labaran ƙarya."

    A ƙarshe sanarwar ta ce da zarar an kammala bincike, za a fitar da cikakken bayani.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake tafka muhawara kan hare-haren da Amurka ta ƙaddamar a Sokoto da Kwara.

  6. Harin ƙunar baki-waje a masallaci a Syria ya kashe mutum 5

    Syria

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutum biyar sun mutu wasu sama da 20 sun jikkata a harin bam din da aka kai wani wani masallaci lokacin da ake sallar Juma'a a birnin Homs da ke kusa da Wadi al-Dhahab na kasar Syria.

    Wakiliyar BBC ta ce harin ya faru ne ana tsaka da sallar juma'a lokacin da masallacin ya cika makil, kuma bam din ya fashe ne daga wani lungun masallacin.

    Hotunan da aka yada a intanet sun nuna yadda masallacin ya yi kaca-kaca bangon shi ya lalace. Jami'ai a yankin sun ce watakil dan kunar bakin wake ne ya tashi bam din.

    A 'yan makwannin nan ana samun karuwar tashin hankali da kashe mutane a hare-haren da ake kai wa birnin Homs, inda mazauna ke kiran a tsaurara matakan tsaro.

  7. Isra'ila ta amince da ƙasar Somaliland

    Netanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce ƙasarsa ta amince da Somaliland a hukumance a matsayin ƙasa ƴantacciya.

    Netanyahu ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Juma'a 26 ga watan Disamba, inda ya ce ya sanya hannu a daftarin amincewar.

    Netanyahu ya sanya hannun ne tare da ministan harkokin wajen Isra'ila, Gideon Sa'ar da shugaban ƙasar Somaliland, Abdirahman Mohamed Abdullahi.

    Ya ce ya amince da ƙasar ne domin ci gaba da ɗabbaƙa tanade-tanaden yarjejeniyar Abraham, sannan ya ce zai ƙarfafa alaƙa da ƙasar a ɓangarorin kiwon lafiya da noma da tattalin arziki da kimiyya da fasaha.

  8. Zelensky ya gana da wakilin Trump kan sabuwar daftarin tsagaita wuta a Ukraine

    Ukraine

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce ya yi wata doguwar tattauna da Steve Witkoff, wakilin Trump na musamman da kuma surukinsa Jared Kushner kan yadda za a kawo karshen yaki da Rasha.

    A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Telegram, Mr Zelensky ya bayyana tattaunawar a matsayin mai ma'ana inda ya ce sun tattauna wasu sabbin manufofi.

    Tun da farko rundunar sojin Ukraine ta ce ta kai wa daya daga cikin matatun man Rasha harin makami mai linzami a yankin Rostov da ke kusa da kan iyaka da Ukraine.

    Ta ce matatar ce ke ba motocin yaki na sojojin Rasha mai a yankin gabashin Ukraine da Rasha ta mamaye

  9. Yadda Amurka ta ƙaddamar da harin makami mai linzami a kan IS a Najeriya

    Bayanan bidiyo, Latsa alamar da ke sama domin kallo
  10. Yadda harin Amurka ya ruguza gidaje a jihar Kwara

    Kwara

    Asalin hoton, Abdganiy Saad.

    Bayan harin da Amurka ta ƙaddamar a jihar Sokoto, rahotanni sun nuna cewa an kai wani harin a garin Offa da ke ƙaramar hukumar Offa a jihar Kwara.

    Kwara jiha ce a arewa ta tsakiya a Najeriya.

    Majiyoyi da suka haɗa da na gwamnatin jihar Kwara sun tabbatar da cewa an kai harin a wani ƙauye da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Offa, inda a ƴan kwanaki wasu ƴan bindiga suka kai hari a coci wanda ya yi sanadiyya rasa ran mutum biyu sannan suka yi awon gaba da dama.

    Kwara

    Asalin hoton, Abdganiy Saad.

    Kwara

    Asalin hoton, Abdganiy Saad

    Kwara

    Asalin hoton, Abdganiy Saad.

    Kwara

    Asalin hoton, Abdganiy Saad.

  11. 'Daga ƙasar Ghana Amurka ta kai hari a Najeriya'

    Amurka

    Asalin hoton, US Department of Defense

    Rahotanni suna nuna cewa daga sansanin sojojin Amurka de ke ƙasar Ghana a Afirka ta Yamma ne Trump ya sa aka ƙaddamar da harin da sojojinsa suka kai a jihar Sokoto.

    Kafar PRNigeria ce ta ruwaito hakan daga majiyoyi, inda ta ce Amurka ta yi amfani da makami mai cin dogon zango ne, "a kan ƴan ta'adda da ke arewacin Najeriya."

    Kafar ta ruwaito cewa harin ya biyo musayar bayanan sirri tsakanin Amurka da Ghana da ma ƙasar Najeriya da aka ƙaddamar da harin.

    Shugaban Amurka Donald Trump ne ya sanar da cewa sojojin ƙasarsa sun kai hari a arewa maso yammacin Najeriya kan mayaƙan IS.

    Gwamnatin Najeriya dai ta ce tana sane da hari, kuma da sahalewarta Amurka ta kai harin.

  12. Ba ma tsoron kowa a wannan gasar- kyaftin din Super Eagles, Daga Ibrahim Yusuf Mohammed, Morocco.

    Super Eagles

    Kyaftin din twagar kwallon kafar Najeriya, Wilfred Ndidi ya yi cewa ƴanwasan Najeriya sun shirya tsaf domin ganin sun lashe gasar cin kofin Nahiyar Afrika ta bana.

    Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a taron manema labarai gabannin wasansu na biyu a matakin rukuni da za su fafata da Tunisia a birnin Fez, inda Ndidi ya yi nuni da cewa ƴan Najeriya na baƙin cikin rashin samun gurbi a gasar cin kofin duniya da za a yi a baɗi.

    Ya ƙara da cewa abin da za su iya yi don sharewa ƴan Najeriya hawaye shi ne lashe wannan gasar.

    Da yake tsokaci kan wasansu da Tunisia, kyaftin ɗin ya yi bayanin cewa ƴan wasan ba su tsoron kowace tawaga ya kuma bugi ƙirji cewa rashin nasarar da suka yi a lokacin da suka kara da Tunisia a gasar 2019 ba zai girgiza su a ƙoƙarin da suke yi na yin nasara a wannan sasan ba.

    Tun da farko dai kocin tawagar na Super Eagles ya amnice cewa Tunisia tawaga ce mai ƙarfi kuma ya kammala duk shirye-shiryen da suka kamata don tabbatar da cewa sun yi nasara.

    Najeriya da Tunisia duk sun lashe wasanninsu na farko a wannan gasa inda Najeriya ta doke Tanzania da ci biyu da daya, ita kuma Tunisia ta doke Uganda da ci uku da ɗaya.

    Wannan dai shi ne karo na tara da Najeriya za ta kece raini da Tunisia a dukkan gasa kuma a wasa takwas da aka fafata a baya kowace kasa ta yi nasara a wasa daya yayin da aka yi canjaras guda shida.

  13. Da amincewarmu Amurka ta ƙaddamar da hari - Gwamnatin Najeriya

    Tinubu

    Asalin hoton, STATE HOUSE NG

    Gwamnatin Najeriya ta ce sai da ta amince tare da bayar da izini kafin gwamnatin Amurka ta ƙaddamar da harin bam a ƙasar.

    Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ne ya bayyana haka a zantawarsa da tashar Channels, inda ya ce Shugaban Najeriya Bola Tinubu yana sane da harin kafin a ƙaddamar.

    Shugaban Amurka Donald Trump ne ya sanar da ƙaddamar da hari a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya, lamarin da ya ɗaga hankalin ƴan ƙasar.

    Da yake jawabi kan harin a safiyar Juma'a, Tuggar ya ce, "yanzu da Amurka ta fara ba mu haɗin kai, za mu ci gaba da aikin ne a tare, kuma kamar yadda shugaban ƙasa ya nanata a jiya kafin ya amince da harin, dole aikin ya zama aikin haɗin gwiwa, kuma dole ya zama babu wani addini da ake hari," in ji shi.

    Ya ce Najeriya ƙasa ce mai addinai da dama, sannan ya ƙara da cewa gwamnatin Najeriya ba ta ce amince a mata karan-tsaye a kan ƴancinta ba.

  14. Mun kai hari kan ƴan ƙungiyar IS a Najeriya - Trump

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Donald Trump ya ce Amurka ta ƙaddamar da wani mummunan hari kan mayakan IS a arewa maso yammacin Najeriya.

    "Dakarun Amurka sun ƙaddamar da hare-hare masu kyau," in ji Trump.

    Cibiyar sojin Amurka a Afrika daga baya ta ce an kai hare-haren ne a jihar Sokoto.

    Shugaban ya zargi ƙungiyar da kai hari tare da kashe Kiristocin da ba su ji ba su gani ba a ƙasar.

    A shafinsa na Social Truth, Trump ya wallafa da yammacin Alhamis cewa "a ƙaƙashin shugabancina, ƙasarmu ba za ta bar masu tsattsauran ra'ayin Musulunci sun girmama ba."

  15. Buɗewa

    Masu bibiyar shafin kai tsaye na BBC Hausa barka da safiyar ranar Juma'a. Kamar kullum yau ma mun dawo da labarai da rahotanni dangane da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Al'ummar Najeriya sun tashi da babban labarin hari da Amurka ta ce ta kai kan ƴan ƙungiyar IS a jihar Sokoto da Kwara.