"Majalisar Ɗinkin Duniya a shirye take ta yi aiki da Zamfara"
Mataimakiyar sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Amina Mohammed ta ce yanzzu akwai tituna a Zamfara dan haka hukumomin duniya za su iya aiki da gwamnatin jihar.
Ta bayyana hakan ne yayin wata ziyarar aiki da ta kai a ƙaramar hukumar Maru inda daga nan kuma aka yi tattaunawa da ta musamman.
"A yau Zamfara na da hanyoyi. Kuma nan gaba sai tafi zama wurin da za a shiga ko ina saboda titunan da ake ci gama da ginawa," in ji ta.
Tace samar da ababan more rayuwa za su ƙara haɓɓaka tattalin arziƙin jihar, tana mai cewa, "yayin da aka kammala ayyukan baki ɗaya, za su farfaɗo da lasuwanci da kuma kasuwannin da ke maƙwabtaka, shi ne fatanmu, sannan za a samu ƙarin zaman lafiya."
Hajiya Amina ta ce ayyukan da ke tafiya a yanzu sun ƙarawa MDD kwarin gwiwa kan Zamfara.
Ta kuma jaddada buƙatar sauya tunani kan jihar zuwa na zaman lafiya.