Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 09/10/2025.

Taƙaitattu

  • Latsa nan ku shiga tasharmu ta WhatsApp
  • Rundunar sojin Najeriya ta musanta yunƙurin juyin mulki
  • Sojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 21 daga hannun 'yanbindiga a jihar Kwara
  • Shugaba Tinubu ya koma Najeriya bayan taron Italiya
  • 'An kashe Falasɗinawa 11 a Gaza'
  • Ba zan yi takarar shugaban ƙasa da Tinubu ba - Wike
  • An gano hanyar gwajin cutar kansa a matakin farko

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Trump zai sake kakabawa China takunkumi

    Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar kakabawa China haraji fiye da na baya, bayan hana kasar fitar da wani ma'adini na musamman.

    Mr Trump ya kuma ce watakila ya soke shirin ganawa da shugaba Xi Jingping na China kamar yadda aka tsara a makonni biyu ma su zuwa.

    China dai ita ce sahun gaba a duniya da ke samar da nau'uka daban daban na ma'adinai masu daraja a duniya.

    Ana amfani da ma'adinan ne wajen yin motoci masu aiki da latironi da wayar oba-oba da sojoji ke amfani da ita.

    A farkon shekarar nan Amurka ta takaitawa China samun kayayyakin hada na'urar kwamfuta da ake amfani da su a kirkirarriyar basirar AI.

  2. Fararen hular Habasha na iya faɗawa mummunan yanayi - Red Cross

    Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta yi gargaɗin cewa ƙazancewar tashin hankali a arewacin yankin Amhara na kasar Habasha, na kara janyowa farar hula shiga mummunann yanayi.

    A wata sanarwa da ta fitar, Red Cross ta ce ɓarkewar faɗa tsakanin sojojin gwamnati da ƙabilar Fano na Amhara ya jikkata mutane da dama da kuma tsananin buƙatar kayan agaji.

    A ranar Alhamis mayaƙan ƙabilar Fano suka yi iƙirarin kashe sama da sojin gwamnati takwas a arewacin yankin Wollo.

    Tun bayan ɓarkewar faɗa tsakanin ɓangarorin biyu shekaru biyu da suka gabata ake ci gaba da samun taho-mu-gama tsakaninsu.

  3. Najeriya ta doke Lesotho 2-1, Afirka ta Kudu ta tashi babu ci

    Najeriya ta samu nasarar doke Lesotho 2-1 a wasan neman gurbin zuwa Gasar Kofin Duniya ta 2026.

    William Troost-Ekong ne ya jefa wa Najeriya ƙwallon farko a bugun fenareti bayan komawa hutun rabin lokaci, kafin ɗanwasan gaban Sevilla, Akor Adams ya zura ta biyu a minti na 80.

    Sai dai jim kaɗan bayan haka Lesotho ta zare ƙwallo ɗaya ta hannun Hlompho Kalake a minti na 83.

    Ita kuwa Afirka ta Kudu da suke rukuni ɗaya da Najeriya ta tashi wasanta babu ci tsakaninta da Zimbabwe.

    To sai dai wani abu, da ba zai yi wa ƴan Najeriyar daɗi ba shi ne nasarar da Benin ta samu da ci 1-0 a wasanta da Rwanda.

    Abin da sakamakon ke nufi a yanzu shi ne Benin ta ci gaba da kasancewa ta farko a rukunin da maki 17, sai Afirka ta Kudu ta biyu da maki 15, yayin da Najeriya ke matsayi na uku da maki 14.

    A yanzu dama ɗaya da ta rage wa Najeriya domin samun damar zuwa gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce samun nasara a wasan ƙarshe da ya rage mata da zura ƙwallaye masu yawa.

    Haka nan sai Benin ta yi rashin nasara, ita ma Afirka da kudu ta kasa samun nasara, wani abu da wasu ke ganin da kamar wuya.

  4. 'Yan bindiga sun kashe mutum takwas a Zamfara

    ‘Yan Sanda sun tabbatar da mutuwar mutum takwas sakamakon harin kwantan bauna da ‘yan bindiga suka kai a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya.

    Wadanda lamarin ya rutsa da su, jami’an tsaron sa-kai ne da ke aikin sintiri a kauyen ‘Yandoto.

    Bayanai na cewa wannan yanki yana fama da matsalar ‘yan bindiga wadanda suke aukawa mutane, inda ko makonni biyu ma da suka gabata sai da aka kashe mutane da dama.

    Rahotanni sun ce jami’an tsaron sun rasa rayukansu ne lokacin da suka yi yunkurin kai dauki, kasancewar an shaida musu cewa yan bindiga za su kai hari garin.

    Wani mazaunin Yandoto ya shaida wa BBC cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis tsakanin karfe goma zuwa goma sha daya na dare.

    Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da aukuwar wannan hari.

    Duk da irin kokari da hukumomi ke cewa suna yi na kakkabe matsalar tsaro a jihar Zamfara, ga alama har yanzu da sauran rina a kaba, saboda ko makonni biyu da suka gabata sai da 'yan bindigar suka aukawa mutanen garin na Yandoto lokacin da suke sallar asuba, inda suka kashe mutane da dama ciki har da limamin masallacin sannan suka kuma yi garkuwa da ƙarin wasu mutane.

    Bayanai na cewa mutanen garin na Yandoto suna yawan kai wa hukumomi koken cewa a kai musu karin jami’an tsaro, saboda sun yi iyaka da wani yanki na jihar Katsina, inda ‘yan bindiga ke tsallakawa suna kai musu farmaki, saboda sulhun da suka yi a wancan bagaren.

  5. Musayar yawu ta barke tsakanin Taliban da Pakistan

    Gwamnatin Taliban ta zargi Pakistan da karya doka ta hanyar amfani da sararin samaniyarta bayan jin karar ababen fashewa har biyu a daren Alhamis a babban birnin kasar Kabul.

    Ma'aikatar tsaron Afghanistan ta ce an kuma kai wani harin kan wata kasuwa a kusa da iyakar kasar da Pakistan wadda kawo yanzu ba a tabbatar da harin ba.

    A wani taron manema labarai, mai magana da yawun sojin Pakistan Laftanal Janar Ahmed Sharif Chaudhry, ya ce Afghanistan ta zama sansanin 'yan ta'adda da ke yakar kasarsa, wani zargi da Taliban ta musanta.

    Ministan harkokin wajen Taliban Amir Khan Muttaqi, ya gargadi Islamabad da kar ta maimaita wannan kuskuren, kamata ya yi ayi sulhu maimakon yaki.

  6. Jagorar adawar Venezuela ta lashe kyautar Nobel ta zaman lafiya

    An bai wa jagorar 'yan adawa a Venezuelan Maria Corina Machado, kyautar Nobel ta zaman lafiya.

    Kwamitin bada kyautar ya ce Mis Machado na aiki kan jiki kan karfi ba tare da gajiya wa ba domin karfafa 'yancin dimokradiyya ga 'yan kasar.

    Mis Machado ta yi kokarin hada kan 'yan adawa a Venezuela domin mara mata baya gabannin zaben shugaban kasa na shekarar da ta 2024, amma sai aka haramta mata shiga zaben baki daya.

    Rahotanni sun ce a lokacin da shugaba Nicolas Maduro, ya yi ikirarin nasara a zaben, duk da shaidu sun nuna Edmundo Gonzalez mutane ke so, Mis Machado ba ta karaya ba ta ci gaba da gangamin da kin tserewa daga kasar duk da cewa gwamnatin Maduro na yi wa rayuwarta barazana.

    Tuni dai fadar gwamnatin Amurka ta soki matakin kwamitin Nobel kan siyasantar da kyautar inda ta ce shugaba Trump ne ya cancanci wannan kyauta ta zaman lafiyar.

  7. An kori manyan jami'an soji daga aiki a Mali

    Gwamnatin mulkin sojin Mali, ta kori manyan jami'an sojin kasar 11 ciki har da masu mukamin Janar kan zargin makarkashiyar janyo rashin zaman lafiya.

    Matakin na zuwa ne a dai-dai lokacin da mutane ke cewa akwai rashin jituwa a gwamnatin sojin da Kanar Assimi Goïta ke jagoranta

    Wata dokar soji da Kanar Goïta ya sanya wa hannu ta tabbatar da korar a matsayin wani mataki na horo.

    Korar ta biyo bayan kama kusan sojoji 30 da aka yi a watan Agusta bisa zargin cewa suna shirya makarkashiyar hambarar da gwamnati.

    Wadanda aka kora sun hada da Janar Abass Dembélé, tsohon gwamnan jihar Mopti, da Janar Néma Sagara daya daga cikin mata ‘yan kalilan da suka kai matsayin Janar a rundunar sojin sama ta kasar ta Mali.

    Tasahar talabijin ta kasar, ORTM, ta nuna hotunan wasu hafsoshin soji da aka tsare, ana ikirarin cewa an dakile wani yunkuri na juyin mulki.To amma wasu kafofi na tsaro a Bamako sun ce korar ta nuna irin sabanin da ke ta karuwa a tsakanin gwamnatin sojin kasar , kuma korar za ta iya kara rarrabuwar kai a tsakanin sojojin.

    A bangare guda kuma, rahotanni na nuna cewa akwai alamun hukumomin sojin Malin suna tattaunawa ta sirri da masu tayar da kayar baya yayin da rikicin ke kara tsanani.

    Tun shekara ta 2012 Mali ke fama da tashin hankali inda kungiyoyi masu alaka da al-Qaeda da kuma IS ke ci gaba da kai hare-hare.

  8. Yadda Falasɗinawa ke komawa rusassun gidajensu a Gaza bayan janyewar sojin Isra'ila

    Dubban Falasɗinawa sun fara kama hanyar komawa gidajensu da hare-haren Isra'ila suka ɗaiɗaita a arewacin Zirin Gaza bayan janyewar dakarun sojin IDF.

    Akasarin gidajen yankin sun rushe, yayin da aka dinga korar mazauna yankin zuwa kudanci fiye da sau ɗaya.

    Rundunar sojin ta Isra'ila ta ce tana fatan kammala janye sojojinta zuwa gefunan birnin, kamar yadda yarjejeniyar tagaita wutar ta tanada.

    Nan gaba kuma Hamas za ta fara shirin miƙa Isra'ilawa aƙalla 20 da ake tunanin suna raye waɗanda ta yi garkuwa da su yayin harinta na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

    A madadin haka, Isra'ila za ta sako ɗaruruwan Falasɗinawa da take tsare da su a gidajen yarinta, 250 daga cikinsu waɗanda aka yanke wa hukuncin ɗaurin rai da rai.

  9. Ghana ta ce ba za ta karɓi Garcia da Amurka za ta koro ba

    Ma'aikatar Harkokin Wajen Ghana ta yi watsi da shirin Amurka na kai ɗan ƙasar El Salvador, Abrego Garcia ƙasar bayan ta koro shi.

    Lauyoyin Mista Garcia sun ce Ma'aikatar Tsaron Cikin Gida ta Amurka (DHS) ta faɗa musu shirinta na tasa ƙeyarsa zuwa Ghana.

    Sai dai, a cewar Ministan Harkokin Waje na Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ba zai yiwu a kai Garcia Ghana ba.

    "Ghana ba za ta karɓi Abrego Garcia ba...Mun shaida wa hukumomin Amurka hakan ƙarara," a cewar Mista Ablakwa.

    "A tattaunawata da jami'an Amurka, mun ƙudiri aniyar karɓar wasu daga cikin korarru amma ba masu laifi ba daga Amurka ne saboda ɗabi'armu ta tarɓar mutane a Afirka da kuma jin ƙai, kuma ba za mu ƙara a kan hakan ba," in ji shi.

    A yau Juma'a lauyoyinsa za su koma kotu domin ci gaba da sauraron shaidun gwamnati game da yunƙurin tasa ƙeyarsa zuwa Eswatini ko kuma wani wuri daban.

  10. Dakarun Isra'ila sun janye daga sassan Gaza

    Mazauna Gaza sun faɗa wa wakilin BBC cewa dakarun Isra'ila sun janye daga arewa maso yammacin Birnin Gaza zuwa gabashi.

    Mai magana da yawun firaministan Isra'ila ya ce dakarun sojin ƙasar za su janye zuwa wuraren da aka amince da su domin samun damar iko da kashi 53 cikin 100 na zirin.

    Shi ma Shugaban Amurka Donald Trump ya ce dakarun za su koma "wurin da aka amince da shi" a yarjejeniyar tsagaita wuta.

    Datarin da Amurka ta gabatar wa Hamas da Isra'ila ya nuna cewa wannan ne matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar da za ta kai ga sakin Isra'ilawa daga hannun Hamas, da Falasɗinawa daga gidajen yarin Isra'ila, da kuma kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya.

  11. Sarkin Kano Sanusi ya jagoranci jana'izar Malami na Madabo

  12. 'Yansanda sun kama mutum 12 da zargin kisan 'yarjaridar Arise TV a Abuja

    Kwana 10 bayan mutuwar 'yarjaridar gidan talabijin Arise TV, Somtochukwu Maduagwu, rundunar 'yansandna Najeriya ta ce ta kama mutum 12 da ake zargi da kisan nata.

    Somtochukwu da aka fi sani Sommie, ta mutu ne ranar 29 ga watan satumba da tsakar dare lokacin da wasu 'yanfashi suka haura gidanta da ke yankin Katampe da ke Abuja babban birnin ƙasar.

    Baya ga Sommie, wani mai gadin gidan ma ya rasa ransa yayin fashin.

    Wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Alhamis ta ce waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu.

    A cewar sanarwar, an kama huɗu daga cikin mutanen ne jim kaɗan bayan aikata fashin ta hanyar bin diddigin wayarsu ta salula.

    "Bincike ya kuma tabbatar da cewa wani mai suna Shamsudeen Hassan ne ya harbe mai gadin mai suna Barnabas Danlami," in ji sanarwar.

  13. Labarai da dumi-dumi, Jagorar adawa a Venezuela Maria Machado ta lashe Kyautar Nobel ta Zaman Lafiya

    Kwamatin bayar da Kyautar Nobel ta Zaman Lafiya ya zaɓi jagorar adawa a Venezuela, Maria Corina Machado, a matsayin wadda ta lashe kyautar ta 2025.

    Cikin wani saƙo a dandalin X, kwamatin ya ce an ba ta kyautar ne "saboda jajircewarta kan kare dimokuradiyya a Venezuela da kuma gwagwarmayar sauya mulkin kama-karya da dimokuradiyya".

    Ya ƙara da cewa ta samu kyautar saboda "kasancewarta ɗaya daga cikin ababen misali" a yankin Latin Amurka a shekarun nan.

  14. Rundunar haɗin gwiwa za ta saka ido kan tsagaita wuta a Gaza, in ji Amurka

    Jami'an Amurka sun ce za a tura wata babbar tawaga ta jami'an soji 200 zuwa Gabas Ta tsakiya domin sa ido kan tabbatar da tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas.

    Rundunar za ta taimaka wajen bayar da tsaro da tsare-tsare da kuma sufuri.

    Jami'an sun ce za ta kunshi mambobi daga ƙasashen Masar da Qatar da Turkiyya, amma sun ce babu wani sojan Amurka da zai shiga Gaza.

    Waklin BBC ya ce Mista Trump ya ce yana fatan zuwaa yankin a ranar Litinin kuma zai tafi Masa domin bikin sa hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta.

  15. Za a yi jana'izar Malami na Madabo a fadar sarkin Kano

    Za a yi jana'izar Malam Kabiru Ibrahim na Madabo, shahararren malamin addinin Musulunci a jihar Kano, a fadar sarkin Kano a safiyar yau Juma'a.

    A jiya Alhamis da yamma ne malamin ya rasu, kamar yadda Sheikh Anas Mahmud Madabo ya bayyana a shafinsa na Facebook.

    "Za a yi sallar jana'aiza gobe [Juma'a] da ƙarfe 10:00 na safe a gidan mai martaba sarkin Kano, sannan za a kai shi maƙabartar kusa da Masaukin Alhazai," a cewar saƙon da ya wallafa.

    Malamin da ake yi wa laƙabi da Babban Malami na Madabo, ya shahara sosai a fannin koyar da addini, wanda ya rayu a unguwar Madabo da ke ƙaramar hukumar Dala a ƙwaryar birnin Kano.

  16. Gwamnatin Isra'ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

    Gwamnatin Isra'ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninta da Hamas, wadda Amurka ta jagoranta.

    Yarjejeniyar za ta kai ga sakin dukkanin yan Isra'ila da aka yi garkuwa da su lokaci guda tare da janye wani ɓangare na sojojinta daga Gaza. A madadin haka, Isra'ial za ta saki Falasɗinawa kusan 2,000.

    Yarjejeniyar na zuwa ne bayan shafe shekara biyu ana yaƙi. Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana matakin a matsayin wani muhimmin cigaba.

    "Mun samar da ci gaba domin dawo da dukkanin wadanda aka yi garkuwa da su," in ji shi.

    Tun da farko, Shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas ya ce yana fatan yarjejeniyar za ta zama sanadin samar da dawwamammen zaman lafiya tare da tabbatar da kafuwar ƙasar Falasdinu.

  17. Barka

    Maraba da sake haɗuwa a shafin labarai kai-tsaye na ranar Juma'a.

    Shafin zai fi mayar da hankali kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya, da Nijar, da maƙwabtansu.

    Umar Mikail ne zai kawo rahotonnin har zuwa 4:00 bisa kulawar Usman Minjibir.