KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed da Abdullahi Diginza

  1. Afghanistan ta gargarɗi Pakistan kan hare-haren da ta kai kan ƴan ƙasarta

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Ana ci gaba da nune-nunen yatsa tsakanin Pakistan da Afghanistan bayan da Islamabad ta kai munanan hare-hare ta sama kan maboyar ƴan ta'adda a ƙasar ta Afghanistan.

    Pakistan ta ce ta kai hari kan irin waɗannan sansanoni guda bakwai a ranar Asabar ɗin da ta gabata, tana mai cewa mazaunansu sun aikata ta'asa na baya-bayan nan a Pakistan tare da zargin hukumomin Taliban na Afghanistan da ba su mafaka.

    Ƙungiyar Taliban a Kabul ta yi alla-wadai da hare-haren.

    Ta ce an kashe ko jikkata fararen hula da dama kuma ta sha alwashin mayar da martani.

    Cikin makonni da suka gabata an samu ƙaruwar hare-haren ƴan bindiga a Pakistan ciki har da wanda aka kai a wani masallacin ƴan Shi’a a Islamabad, inda aka kashe sama da mutane 30.

  2. Sama da fursunonin siyasar Venezuela 1,500 sun nemi a yi musu afuwa

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Shugabar riƙo Delcy Rodriguez da shugaban majalisar dokoki Jorge Rodríguez

    Fursunonin siyasa 1,557 a Venezuela ne suka nemi a yi musu afuwa a ƙarƙashin wata sabuwar dokar da aka kafa ranar Alhamis, in ji shugaban majalisar dokokin ƙasar.

    Jorge Rodríguez, ɗan uwan shugaban rikon ƙwarya na Venezuela Delcy Rodríguez kuma na hannun daman tsohon shugaban ƙasar Nicolás Maduro, ya kuma ce an riga an saki "ɗaruruwan" fursunoni.

    Daga cikin su har da ɗan siyasa Juan Pablo Guanipa, ɗaya daga cikin ƴan adawa da dama da suka soki dokar kan ware wasu fursunoni.

    Amurka ta buƙaci Venezuela da ta gaggauta sakin fursunonin siyasa tun bayan da sojojin Amurka suka sace Maduro a wani samame da suka kai a ranar 3 ga watan Janairu.

    Gwamnatin Venezuela dai ta daɗe ta na musanta cewa ta na tsare fursunonin siyasa.

  3. Ya kamata Birtaniya ta ƙara aikewa da sojoji zuwa Ukraine - Boris Johnson

    Boris Johnson

    Asalin hoton, Reuters

    Tsohon Firaministan Birtaniya Boris Johnson ya ce kamata ya yi Birtaniya da ƙawayenta su tura dakarun soji da ba na yaƙi ba zuwa Ukraine, don yin abin da ya kira ''sauya tunanin" shugaban Rasha Vladimir Putin.

    A wata hira da ya yi da BBC ranar Lahadi, Johnson ya ce ya kamata a tura sojoji zuwa yankunan da ake zaman lafiya domin gudanar da ayyukan da ba na faɗa ba.

    A halin yanzu dai gwamnatin Birtaniya tana aiki ne tare da ƙawayenta don haɗa wata "gamayyar masu niyya" don samar da dakaru da za su tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Ukraine, amma sai dai idan an cimma yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin.

    Yayin da yake magana kwanaki kaɗan gabanin cika shekaru huɗu da fara yaƙin, Johnson, wanda ya kasance firaminista a lokacin da aka fara rikicin, ya kuma ce tun da farko akwai yiwuwar iya daƙile rikicin da ƙawancen ƙasashen Yammacin duniya sun mai da hankali kan karuwar cin zalin da Putin ke yi tun bayan da ya mamaye yankin Crimea a shekara ta 2014.

  4. Ɗaliban jami'a sun sake yin zanga-zangar adawa da gwamnatin Iran

    ...

    Dalibai a jami'o'i da dama da ke faɗin kasar Iran sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da gwamnati, wanda hakan ne gangami na farko tun bayan wanda aka gudanar a watan da ya gabata da hukumomi suka yi.

    BBC ta tantance bidiyon masu zanga-zangar da suka yi tattaki a harabar jami'ar fasaha ta Sharif da ke Tehran babban birnin ƙasar a ranar Asabar inda daga baya aka ga an yi arangama tsakanin su da magoya bayan gwamnati.

    An gudanar da zaman dirshan a wata jami'ar Tehran, kuma an yi wani gangami a yankin arewa maso gabashin ƙasar inda ɗalibai ke karrama dubban mutanen aka kashe a zanga-zangar da aka yi a watan Janairu.

    Amurka dai na ci gaba da ƙara yawan sojojinta da ke jibge a kusa da Iran, kuma shugaba Donald Trump ya ce yana tunanin kai wa Iran takaitaccen harin soji.

    Amurka da ƙawayenta na Turai na zargin cewa Iran na yunkurin ƙera makamin nukiliya, lamarin da Iran ta daɗe ta na musantawa.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa-kai tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Lahadi, da fatan kun wayi gari lafiya.

    Ku ci gaba da biyo domin samun labarai da rahotonnin abubuwan da ke faruwa a faɗin duniya.