Labaran abubuwan da ke faruwa dangane da wasanni

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman labaran wasanni a faɗin duniya na ranakun 31 ga watan Mayu zuwa 7 ga watan Yunin 2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Ban ji haushi da PSG ta lashe UCL ba - Mbappe

    Mbappe

    Asalin hoton, Getty Images

    Kylian Mbappe ya ce bai ji haushin nasarar da Paris St-Germain ta yi wajen lashe Champions League ba, shekara ɗaya bayan barin ƙungiyar zuwa Real Madrid.

    Ɗan wasan gaban ya bar PSG a matsayin wanda ya fi ci mata kwallaye, sai dai ya ƙasa cin gasar Champions League a kaka bakwai da ya shafe a ƙungiyar - inda ya koma Madrid kyauta a watan Yulin bara.

    PSG ta samu nasara ne bayan lallasa Inter Milan da 5-0, a ranar 31 ga watan Mayu a filin wasa na Munich Arena da ke Jamus.

    "Ban bar ƙungiyar da wuri ba, tarihin rayuwata a PSG ya kare. Ba na jin haushi, saboda zama na a PSG ya kare," in ji kyaftin ɗin tawagar Faransa, wanda ya ci wa PSG kwallo 256.

    Da yake magana da manema labarai gabanin karawar Faransa da Jamus a neman matsayi na uku a gasar Nation League, Mbappe ya ƙara da cewa: "Na yi iyakar ƙoƙarina, kuma haka Allah ya kaddara cewa za su ci Champions League ba tare da ni ba.

    "Lashe Champions League ba tare da ni ba da PSG ta yi ba zai dame ni ba. Ina cikin farin ciki - Ina ganin sun cancanci lashe gasar.

    "Sun shafe tsawon shekaru suna fuskantar kalubale. Tare da ni aka fuskanci hakan; na buga wasa a kowane mataki a Paris in ban da wanda suka yi nasara.

    "Su ne ƙungiyar da ta fi hazaka a Turai. Ban taɓa ganin ƙungiyar da ta ci kwallo 5-0 a wasan karshe ba gaskiya."

    Lokaci na karshe da Mbappe ya kusan lashe Champions League shi ne wasan karshe da suka buga da Bayern Munich a 2020, inda suka sha kashi da 1-0.

  2. Ba zan buga Club World Cup ba - Ronaldo

    Ronaldo

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan Al-Nassr Cristiano Ronaldo ya ce ba zai buga gasar Club World Cup ba duk da cewa wasu ƙungiyoyin da za su buga gasar sun yi ta zawarcinsa.

    "Ba zan buga Club World Cup ba. Wasu ƙungiyoyi sun tuntuɓe ni, sun yi min tayi mai tsoka - wasu kuma maras kyau, amma ba komai ne mutum zai iya yi ba," in ji Ronaldo yayin tattaunawa da manema labarai.

    A watan Mayu ne shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA, Gianni Infantino ya ce yana so Ronaldo ya buga gasar duk da cewa Al-Nassr ba ta samu gurbin zuwa gasar ba.

    Kwantiraginsa a Al-Nassr za ta ƙare a watan Yuni, amma majiyoyi sun tabbatar wa BBC cewa ƙungiyar na da ƙwarin gwiwar cewa zai saka hannu kan sabuwar yarjejeniya.

  3. Tottenham ta kori kociyanta Postecoglou bayan lashe kofin Europa

    Ange Postecoglou

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham ta sanar da sallamar kociyanta, Ange Postecoglou kwana 16 bayan ya jagoranci ƙungiyar wajen lashe kofin Europa.

    Matakin na zuwa ne bayan da ƙungiyar ta ƙare a mataki mafi muni kan teburin Premier, inda ta ƙare a mataki na 17 bayan yin rashin nasara a wasa 22.

    Kocin ɗan Australia ya fuskanci mummunan sakamako a kaka uku da ya yi a ƙungiyar kodayake bana ta fi bara saboda aƙalal ya ɗauki kofin Europa.

    A shekarar 2023 ne ƙungiyar ta ɗauke shi daga Celtic a matsayin shekara huɗu.

  4. Chelsea na tattaunawa da AC Milan kan Mike Maignan

    Mike Maignan

    Asalin hoton, Getty Images

    Chelsea ta fara tattaunawa da AC Milan domin neman sayen mai tsaron ragarta Mike Maignan.

    Ƙungiyar ta Italiya na neman fam miliyan 25 ne domin barin ɗan wasan ya tafi, amma Chelsea ta ce ya yi tsada, don haka tana neman ragi.

    Maignan shi ne mai tsaron ragar Faransa kuma ya buga mata wasanni 30 daga 2020 zuwa yanzu. Shi ne kuma golan da Faransa ta fi amfani da tun bayan da Hugu lloris ya yi ritaya a 2023.

    BBC ta samu bayanan cewa ɗan wasan na da ra'ayin komawa Chelsea.

    Chelsea dai ta jima tana neman mai tsaron ragar da za ta yi dace da.

  5. Luis Diaza ba na sayar ba ne - Liverpool

    Luis Diaz

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool ta sanar wa Barcelona cewa Luis Diaz ba na sayarwa ba ne, kuma ta ƙi ba ta damar tattaunawa da shi.

    Dama dai daraktan wasannin Barcelona, Deco ya sha nanata sha'awar sayen ɗan wasan gaban Liverpool Luis Diaz domin ƙarfafa ƙungiyarsa.

    Sai dai hukumomin Liverpool sun shaida wa BBC cewa ba zai yiwu su rabu da Luis Diaz a halin yanzu ba.

    Luis Diaz ya zura ƙwallo 13 a kakar bana kuma ya taka muhimmiyar rawa yayin da Liverpool ta lashe Premier League, Lamarin ya sa ƙungiyoyi kamar Barca da kuma saura daga Saudiyya ke sha'awarsa.

    Kwantiraginsa zai ƙare a 2027.

  6. Super Eagles na shirin fafatawa da Rasha a wasan sada zumunta

    Super Eagles

    Asalin hoton, Super Eagles

    Tawagar Super Eagles na shirin fafatawa da Rasha a wasan sada zumunta a filin Luznikhi da ke birnin Moscow ranar Juma'a.

    Wannan ne karon farko da ƙasashen biyu za su fafata da juna, kuma ƴanwasan Super Eagles kamar Victor Osimhen da Ademola Lookman da Ola Aina ba za su buga wasan ba.

    Najeriya za ta je Moscow ne bayan lashe kofin sada zumunta na 'Unity Cup' a ranar Asabar.

    Super Eagles ta lallasa abokan hamayyarta na Ghana 2-1 a ranar Laraba sannan ta doke Jamaica 5-4 a bugun fanareti bayan an kai ƙarshen lokaci ana 2-2 a wasan ƙarshe.

    Har yanzu akwai haramcin shiga gasannin duniya a kan Rasha bayan mamayen da ta ƙaddamar kan Ukraine a watan Fabarairun 2022, amma duk da haka kocin Najeriya Eric Chelle na sa ran karawar za ta yi zafi yayin da yake shirin ci gaba da karawa a wasannin neman gurbin gasar cin kofin duniya ta 2026 a watan Satumba.

    Karawar da Najeriya za ta yi a gida da Rwanda da kuma ziyartar Afirka ta Kudu, na da muhimmanci sosai yayin da Najeriyar ke neman cike giɓin maki shida da ke tsakaninta da Afirka ta Kudu da ke ta ɗaya a rukunin C.

    "Rasha babbar ƙasar ƙwallon ƙafa ce," in ji Chelle.

    "Suna buƙatar buga wasanni da ƙasashen duniya kasancewar yaƙin ya sa abubuwa sun yi musu tsauri. Suna da ƙwararrun ƴan wasa a gasar ƙungiyoyi ta cikin gida.

    "Ina ganin mutane da yawa za su zo su kalli wasan.

    "Abin da ke faruwa shi ne muna shiri ne kafin Satumba, lokacin da za a sake karawa a wasannin neman gurbin gasar cin kofin duniya. Wannan ne abin da muke hari."

  7. Wasan yaƙin neman lashe Ballon d'Or - Yamal da Dembele a Nations League

    Yamal, Dembele

    Asalin hoton, Getty Images

    Faransa da Sifaniya za su fafata a wasan kusa da na ƙarshe a gasar Nations League a yau Alhamis, inda mutane ke ganin cewa wasan na da muhimmanci ga waɗanda ake ganin sun fi damar lashe Ballon d'Or, Lamine Yamal da Ousmane Dembele.

    Baya ga rawar da suka taka wa ƙungiyoyinsu, duk sun zura ƙwallo a wasan kwata final ɗin ƙasashensu a gasar Nations League.

    Yadda ƴan wasan suka taka rawa a kakar bana:

    Ƙwallo: Yamal 18, Dembele 33. Bayarwa a ci: Yamal 21, Dembele 13

  8. Ronaldo ya yi nasara a kan Jamus karon farko a tarihinsa

    Ronaldo

    Asalin hoton, Getty Images

    Ronaldo ya cimma nasarar da ya daɗe yana nema a rayuwarsa bayan da ya zura ƙwallo a wasan kusa da na ƙarshe a gasar Nations League inda Portugal ta doke Jamus da ci 2-1 - karon farko a tarihinsa.

    Kafin wasan wanda aka buga ranar Laraba, Ronaldo ya fafata da Jamus sau biyar kuma ya yi rashin nasara a duka, amma yanzu ya samu nasara ɗaya a kan Jamus.

    Ronaldo ya zura ƙwallonsa na 137 wa Portugal, kuma ya ƙara ɗaya ke nan a yunƙurinsa na cika burin zura ƙwallo 1,000, a yanzu saura masa ƙwallo 63.

    Portugal dai na jiran sanin wadda za ta fafata da ita yayin da Sifaniya da Faransa za su kara a wasan kusa da na ƙarshe a yau Alhamis.

  9. Ƴanwasa 10 mafiya daraja a duniyar ƙwallon ƙafa

    Yamal

    Asalin hoton, Getty Images

    Matashin ɗanwasan Barcelona, Lamine Yamal ka iya kai darajar kusan fam miliyan 340, idan za a sayar da shi, a cewar wata ƙungiya a ƙasar Switzerland mai nazari kan darajar ƴan wasa.

    A wata ƙididdiga ta daban, cibiyar sanya idanu kan ƴanwasa ta CIES, ta ƙiyasta cewa ɗan wasan mai shekara 17 zai kai darajar euro miliyan 400 - kusan ninkin abin da aka sayar da Barcelona ta sayar da Neymar - euro miliyan 222 - ga PSG a 2017, mafi tsada a lokacin.

    Matashin ɗan Sifaniya ya kasance na biyar cikin jerin matasan ƴanƙwallo da suka haska a kakarsu ta farko a gasar La Liga, a lokacin yana da shekara 15 da wata tara.

    Ya zarta Messi- da ya lashe kyautar Ballon d'Or har sau takwas - da ƙwallo 23 a daidai waɗannan shekaru.

    Ga jerin ƴan wasan 10 da suka fi daraja:

    1. Lamine Yamal (Barcelona) £340m.

    2. Erling Haaland (Man City) £200m.

    3. Jude Bellingham (Real Madrid) £197m.

    4. Kylian Mbappe (Real Madrid) £162m.

    5. Jamal Musiala (Bayern Munich) £130m.

    6. Pedri (Barcelona) £121m.

    7.Vinicius Junior (Real Madrid) £109.7m.

    8. Cole Palmer (Chelsea) £106.5m.

    9. Julian Alvarez (Atletico Madrid) £106m.

    10. Florian Wirtz (Bayer Leverkusen) £103m.

  10. Fulham ta sanar da korar William da Carlos Vinicius

    Fulham

    Asalin hoton, Getty Images

    Fulham ta sanar cewar Willian da Carlos Vinicius za su bar kungiyar bayan da yarjejeniyarsu za ta kare a karshen watan Yuni.

    Willian, wanda ya sake komawa Fulham a farkon shekarar nan ya buga wasa 79 tun bayan da ya fara buga mata tamaula a 2022 a karon farko.Shi kuwa Vinicius zai yi ban kwana da Fulham, bayan da suke su uku a gurbin da yake bugawa, idan ka hada da Raul Jimenez da Rodrigo Muniz.

    Fulham ta yi wa kyaftin dinta Tom Cairney tayin karin kwantiragi, wanda ake alakanta shi da zai koma Wrexham, wadda za ta buga Championship a badi.

    Sauran da aka yi wa tayin tsawaita kwantiragi a Fulham sun hada da Kenny Tete da matashi Luc De Fougerolles da Callum Osmand da kuma Lemar.

  11. Super Eagles

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗaya daga cikin masu hannun jari a Crystal Palace, John Textor, wanda shi ke da ƙungiyar Faransa ta Lyon, na shirin sayar da kaso mai yawa na hannun jarinsa. (Mail)

    Mai tsaron raga a Ingila, Aaron Ramsdale ya tattauna kan yiwuwar tafiya West Ham daga Southampton. (Talksport)

    Ɗan wasan tsakiya a Croatia, Luka Modric mai shekara 39, ya amince ya koma AC Milan idan ya bar Real Madrid. (Gianluca di Marzio, via Football Italia)

  12. Fabregas ya mayar da hankali kan horar da Como

    Cesc Fabregas ya ce hankalinsa gabaki daya yana Como, bayan da ake alakanta shi da zai karbi aikin kociyan Inter Milan, sakamakon da Simone Inzaghi ya ajiye aikin bayan da Paris St Germain ta doke su 5-0 ranar Asabar ta lashe Champions Legue a Jamus.

    Kungiyoyi da dama na son zawarcin Febregas, tsohon dan wasan Arsenal da Barcelona da Chelsea, bayan da ya kare a mataki na 10 a teburin Serie A da Como a Serie A da aka kammala.

    Wasu rahotanni daga Italiya na cewa Inter za ta maye gurbin Inzaghi da Fabregas, domin tunkarar Club World Cup da za a yi a Amurka daga ranar 14 ga watan Yuni.

  13. Wasannin da za a buga ranar Alhamis

    UEFA Nations League karawar daf da karsheSpain da France

    FIFA World Cup bangaren AsiaGroup A

    • Korea DPR da Kyrgyz Republic
    • Qatar da Iran
    • United Arab Emirates da Uzbekistan

    Group B

    • Iraq da South Korea
    • Kuwait da Palestine
    • Oman da Jordan

    Group C

    • Australia da Japan
    • Bahrain da Saudi Arabia
    • Indonesia da China PR
  14. Middlesbrough ta kori kociyanta Michael Carrick

    Carrick

    Asalin hoton, Getty Images

    Middlesbrough ta kori Michael Carrick, bayan kaka biyu da rabi yana jan ragama.

    Tsohon dan wasan tawagar Ingila, mai shekara 43 ya karbi aiki a kungiyar dake buga Championship a Oktoban 2022 a karon farko da ya fara aikin kociya.

    Ya ja ragamar kungiyar ta buga wasan cike gurbin shiga Premier League a 2022-23, wadda ba ta samu gurbin ba, daga nan ta kasa shiga cikin yan shidan farko a kaka biyu da ta wuce.

    Mataimakin Carrick, Jonathan Woodgate da dan uwansa Graeme Carrick duk sun bar kungiyar.

    Bayan da aka kori Carrick, kenan kungiya 17 daga 24 masu buga Championship sun sauya mai horar da tamaula tun daga Agustan bara.

  15. Sifaniya za ta kara da Faransa a wasan daf da karshe na Uefa Nations League

    Lamine Yamal

    Asalin hoton, Getty Images

    Tawagar Sifaniya ta yi atisaye ranar Laraba a sansaninta, Las Rozas ahead a shirin wasan daf da karshe da Faransa a UEFA Nations League.

    A yammaci ne Sifaniya za ta je Stuttgart inda koci, Luis de la Fuente da Pedri za su tattauna da yan jarida.

    Sifaniya da Faransa za su kece ranar Alhamis, domin samun wadda za ta buga wasan karshe a Uefa Nations League.

    Ranar Laraba za a fara wasan daf da karshe tsakanin Jamus da Portugal.

  16. Live Page

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai buga gaba a Brentford da Kamaru, Bryan Mbeumo, ɗan shekara 25 na fatan samun albashin £250,000 a kowanne mako - ninki har sau biyar kan abin da ake ba shi yanzu - idan ya koma Manchester United. (Times - subscription required)

    Inter Milan ta tuntubi kocin Como kan ko tsohon ɗan wasan tsakiya a Sifaniya, Cesc Fabregas zai maye gurbin mai horas da su Simone Inzaghi, da ya tafi. (Sky Sports Italia - in Italian)

    Chelsea tayi tuntuba kan ɗan wasan Faransa mai shekara 29, Mike Maignan, wanda yake da sauran kwantiragin shekara guda a AC Milan. (Talksport)

  17. Tottenham za ta sayar da Son idan an taya da tsoka

    Son Hueng min

    Asalin hoton, Getty Images

    Tottenham ta ce za ta iya sayar da Son Heung-min ga duk kungiyar da ta yi tayi mai tsoka.

    Ana alanta son da kungiyar Saudiyya, wadan da suka taya shi da tsoka a kaka biyu da ta wuce, wanda ya zabi taka leda karkashin sabon koci Ange Postecoglou.

    A watan jiya kyaftin Son ya ja ragamar Tottenham ta lashe Europa League, bayan cin Manchester United 1-0 a Sifaniya.Ana ta tantama kan makomar Son, wanda zai shiga kakar karshe a yarjejeniya da Tottenham.

    A watan Yuli Son zai cika shekara 33 da haihuwa, wanda ke fama da jinya a kakar da ta wuce, amma Tottenham ta ce tana jiran tayi mai tsoka.

    Tottenham na shirin ziyara Koriya ta Kudu, domin yin atisayen tunkarar kakar badi, karo na uku a kaka hudu da kungiyar da ke buga Premier ke zuwa kasar.

    Son, wanda ya je buga wa kasarsa tamaula ya ci kwallo 11 a Tottenham a kakar da ta wuce, wannan shi ne karon farko da bai zura kwallaye ba da yawa a raga tun bayan da ya koma kungiyar da taka leda.

    Bayan son da ake tantama kan makomarsa, haka shima koci, Ange Postecoglou na fuskantar matsi, bayan da Tottenham ta kare a kaka mafi muni a tarihi a Premier League.

  18. Jorginho da Tierney suna daga cikin 20 da Arsenal ta kora

    Arsenal

    Asalin hoton, Getty Images

    Jorginho da Kieran Tierney za su bar Arsenal, bayan da kwantiraginsu ya kare ranar 30 ga watan Yuni, kamar yadda Gunners ta fitar da sunayen yan wasan da ta kora.

    Jorginho dan wasan tawagar Italiya, wanda ke daf da rattaba hannu a Flamengo ta Brazil, ya koma Emirates daga Chelsea a Janairu 2023, wanda ya yi mata wasa 79.

    Shi kuwa Tierney dan kwallon tawagar Scotland, ya koma Arsenal daga Celtic kaka shida da ta wuce, ya buga wasa 170 daga baya ya je aro a Real Sociedad a kakar 2023-24.

    Bayan da ya koma Emirates ya buga wasa 13 a Premier League, zai sake komawa Celtic.

    Shima yarjejeniyar Thomas Partey za ta kare a karshen watan Yuni, amma Arsenal na tattaunawa da shi don tsawaita zamansa a Emirates.

    Shi kuwa Raheem Sterling, wanda ya buga wasannin aro 28 a Arsenal, zai sake komawa Chelsea da taka leda.

    Cikin wadanda Arsenal ta kora har da matasan kungiyar yan kasa da shekara 18 da 21 da wasu daga matan dake yiwa kungiyar wasanni.

  19. Messi ya yi atisaye a tawagar Argentina

    Lionel Messi

    Asalin hoton, Getty Images

    Lionel Messi ya yi atisaye a tawagar Argentina, wadda ke shirin buga wasan neman shiga gasar kofin duniya da Chile.

    Argentina mai rike da kofin duniya karkashin koci, Lionel Scaloni, za ta fuskanci wasa biyu masu zafi a shirin da take na kare kofinta a Amurka da Mexico da Canada a 2024

    Argentina za ta fafata da Chile a Santigo ranar Alhamis daga nan ta karbi bakuncin Colombia a Buenos Aires a Monumental ranar 10 ga watan Yuni.

    Argentina ce ta daya a rukunin Kudancin Amurka da maki 31 a wasa 14 da cin wasa 10 da canjaras daya aka doke ta uku daga ciki.

  20. Cagliari ta kori kociyanta, Davide Nicola

    Davide Nicola

    Asalin hoton, Getty Images

    Cagliari ta sallami kociyanta, Davide Nicola wanda ya hana kungiyar barin Serie A a kakar da aka kammala kamar yadda kungiyar ta sanar ranar Laraba.

    Nicola ya karbi aiki a cikin watan Yuli, bayan maye gurbin Claudio Ranieri, ya kuma sa hannu kan yarjejeniyar kaka biyu da ta kare a mataki na 15 a kasan teburin Serie A da tazarar maki biyar tsakani da yan karshen teburi.

    Nicola ya yi suna wajen ceto kungiya daga faduwa daga gasa, cikinsu har da Empoli da Salernitana da Torino da kuma Genoa dukkansu kungiyoyin Italiya.