Labarin wasanni daga 12 zuwa 16 ga watan Janairun 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Litinin 12 zuwa 16 ga Janairun 2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Simeone ya ce bai ƙyauta ba kan abin da ya yiwa Vinicius, Spanish Super Cup

    Spanish Super Cup

    Asalin hoton, Getty Images

    Kocin Atletico Madrid, Diego Simeone, ya bayar da uzuri kan halayen da ya nuna a gefen fili, yayin da ƙungiyarsa ta sha kashi a wasan daf da ƙarshe a Spanish Super Cup a hannun Real Madrid a Saudiyya. Ya ce yana baƙin ciki kan yadda ya tsokani Vinícius Jr., amma bai bukaci a yafe masa ba.

    Wata ƙyamara ce ta nuna kocin ɗan Argentina yana ta tsokanar ɗan ƙwallon tawagar Brazil, Vinícius Jr., a tsawon wasan.

    Rahotanni sun ce yana ta faɗawa ɗan wasan Real Madrid: “Florentino zai kore ka — ka tuna abin da nake gaya maka,” yana nufin rade-radin makomar Vinícius kan mika masa sabuwar yarjejeniya, bayan da wadda yake da ita a Real Madrid wa’adinta ke gab da ƙarewa.

    Real Madrid ta yi nasara da ci 2–1, inda ta samu gurbin buga wasan ƙarshe, amma daga bisani ta sha kashi da ci 3–2 a hannun abokan hamayya Barcelona.

    Atletico Madrid na matsayi na huɗu a teburin La Liga da tazarar maki 11 tsakanin da Barcelona.

  2. Bentancur na Tottenham na bukatar tiyata, Tottenham

    Bentacur

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan Tottenham, Rodrigo Bentancur, zai bukaci a yi masa tiyata sakamakon raunin da ya ji.

    Bentancur ya ji ciwo ne a wasan da Tottenham ta sha kashi da ci 3–2 a hannun Bournemouth a ranar Laraba, kuma koci Thomas Frank ya tabbatar washegari cewa raunin “babba ne” kafin Aston Villa ta fitar da Tottenham daga FA Cup ranar Asabar.

    Tuni Tottenham ke fama da wasu muhimman ƴan wasanta da ke jinya, kuma ana sa ran Bentancur zai yi jinyar akalla wata uku, bayan da aka yanke shawarar tiyata ita ce mafita mafi dacewa.

    Rashin Bentancur da Lucas Bergvall a wasan ranar Asabar ya sa Frank bai da ɗan wasan tsakiya ko ɗaya a benci, yayin da Pape Sarr da Yves Bissouma ba su koma ba, saboda halartar gasar AFCON.

    Watakila Tottenham ta ɗauki ɗan wasa a watan Janairu mai buga gurbin tsakiya, koda yake ana sa ran Bissouma zai koma Tottenham a wannan makon bayan fitar Mali daga gasar cin kofin nahiyar Afirka.

  3. Watakila Salah zai gama halartar Afcon da zarar an kammala ta Morocco, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Watakila wannan ce gasar Afcon ta karshe da Mohamed Salah yake halarta, bai kuma taba daukar kofin ba.

    Ɗan wasan Liverpool, wanda ya lashe manyan kofunan gasar Turai ya kai zagayen karshe a 2017, inda Kamaru ta ɗauka da a 2019 da Senegal ta zama gwarzuwa a karon farko a tarihi, yayin da bai je wadda aka yi a Ivory Coast ba a 2023 sakamakon jinya.

    Filayen da za a buga daf da karshe a ranar Laraba sun hada da na Tangier da na Prince Moulay Abdellah a birnin Rabat.

    Kuma wasan daf da karshe za a yi ne tsakanin Senegal da Masar da na Najeriya da Morocco.

  4. Guardiola zai so wasansa da Newcastle a yi falan ɗaya a Carabao Cup, Carabao Cup

    Guardiola

    Asalin hoton, Getty Images

    Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya ce zai fi son wasan daf da ƙarshe a League Cup da zai buga da Newcastle United a yi shi falan ɗaya, saboda yadda masu riƙe da kofin ke yawan cin kwallaye a mintuna na ƙarshe a tashi wasa.

    Anthony Gordon ya ci Bournemouth a bugun fenariti a karin lokacin a FA Cup ranar Asabar, kafin Newcastle ta yi nasara a bugun fanareti.

    Haka kuma ta ci ƙwallo biyu a ƙarin lokaci da suka taimaka wa Newcastle ta doke Leeds United da cin 4–3 a gasar Premier League a ranar Laraba.

    A watan Nuwamba, Harvey Barnes na Newcastle ya ci kwallo a minti na 70 wanda ya ba su nasarar 2–1 a kan City a wasan Premier.

    Manchester City tana matsayi na biyu a Premier League da maki shida tsakani da Arsenal mai jan ragama, Guardiola ya ce zai yi taka-tsantsan kada ya jefa ƴan wasansa cikin haɗarin rauni a gasar League Cup ranar Laraba.

  5. Afcon ta kawo zagayen daf da karshe da tawaga huɗu ta rage, Afcon Morocco 2025/26

    Brahimi

    Asalin hoton, Getty Images

    Kawo yanzu saura wasa huɗu suka rage nan gaba a rufe labulen wasannin cin kofin Afirka a Morocco, bayan da aka yi fafatawa 48.

    An kuma sharara kwallo 119 a raga, Najeriya ta ci 12 ita ce kan gaba a wannan ƙwazon.

    Brahim Diaz na Morocco ne kan gaba mai ƙwallaye da yawa mai biyar a raga da ƴan wasa biyu masu hurhudu kowanne da ya hada da Mohamed Salah na Masar da kuma ɗan ƙwallon Najeriya, Victor Osimhen.

    Haka kuma ƴan wasa huɗu ne suka ci gida - an bayar da jan kati tara da kuma mai ruwan ɗorawa 25 jimilla.

  6. Chelsea za ta auna koshin lafiyar James da Palmer kan fuskantar Arsenal, Chelsea

    Rosenior

    Asalin hoton, Getty Images

    Kociyan Chelsea, Liam Rosenior, zai yanke shawara kan koshin lafiyar Reece James da Cole Palmer kafin wasan daf da ƙarshe a gasar Carabao Cup zagayen farko da za su fafata da Arsenal a ranar Laraba.

    Kyaftin ɗin ƙungiyar, James da Palmer ba su buga wasan farko da sabon kociya, Rosenior ya jagoranta, inda Chelsea ta doke Charlton da ci 5–1 a FA Cup a ranar Asabar.

    Mai tsaron baya Malo Gusto ma bai buga wasan ba, kuma shi ma za a auna koshin lafiyarsa.

    A halin yanzu Moises Caicedo na hukuncin dakatarwa, bayan karɓar katin gargaɗi biyar jimilla.

  7. Masu horarwa daga Afirca huɗu ne suka kai daf da karshe a Afcon, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    A karon farko a tarihin gasar cin kofin Afirka dukkan tawaga huɗun da ta kai daf da karshe tana da kociya ne daga nahiyar - kenan ɗaya daga ciki zai lashe kofin bana.

    Mai masaukin baki Morocco tana da mai horarwa Walid Regragui da Hossan Hasan na Masar da Pepe Thiaw na Senegal da Erik Chelle ɗan Mali mai jan ragamar Super Eagles.

    Wata kididdiga ta nuna cewa a Afcon na bana, koci 15 daga 24 masu horarwarsu ƴan Afirka ne - kuma 11 daga ciki sun haura zagayen cikin rukuni da lashe wasa kaso 75 cikin 100.

    Kociyan Afirka, Djamel Belmadi ya sa Algeriya ta dauki Afcon a 2019, Aliou Cissé ya lashe kofin tare da Senegal a 2021 da kuma wanda Ivory Coast ta ci tare da Émerse Fae a 2023.

    An kuma samu masu horarwa daga Afirka da suka kafa tarihin lashe kofin nahiyar Afirka a matakin dan wasa da kuma koci da ya hada da Mahmoud El-Gohary da kuma Stephen Keshi.

    Yanzu haka Hossam Hasan, wanda ya lashe Afcon a matakin ɗan wasa shi ne ke jan ragamar Masar mai Afcon bakwai jimilla wadda za ta kece raini da Senegal a daf da karshe ranar Laraba.

    A kuma ranar za a fafata tsakanin Najeriya da Morocco.

  8. Za a ci gaba da wasan daf da karshe a Afcon ranar Laraba, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Tawaga hudu ce ta kai zagayen daf da karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake tata burza a Morocco.

    Da ya haɗa da Senegal da Masar da Najeriya da mai masaukin baki Morocco - kuma tsakaninsu sun lashe Afcon 12 jimilla daga ciki Morocco da Senegal da Masar za su wakilci Afirka a gasar cin kofin duniya a bana da za a yi a Amurka da Canada da kuma Mexico.

    Masar tana da Afcon ɗaya, Super Eagles tana da uku da Senegal mai ɗaya da kuma Masar mai bakwai jimilla, ita ce kan gaba a yawan lashe kofin babbar gasar tamaula ta Afirka.

  9. , Daga Jaridu

    Bentacur

    Asalin hoton, Getty Images

    Matashin dan bayan Como Jacobo Ramon ya burge Liverpool da Chelsea, kuma kungiyoyin Firmiya da dama na tura masu yi musu farautar 'yan wasa domin su je su ga yadda dan wasan mai shekara 21 ke taka leda. (CaughtOffside)

    Paris FC na daga cikin kungiyoyin da ke son aron dan gaba Faransa na gefe Mathys Tel a watan nan, amma kuma Tottenham na son dan wasan mai shekara 20 ya tsaya kar ya tafi. (Fabrizio Romano)

    Darektan wasanni na Tottenham Fabio Paratici na dab da barin kungiyar domin tafiya kungiyar Serie A, Fiorentina bayan kasuwar saye da sayar da 'yan wasa ta Janairu. (Athletic)

    Dan bayan Farans, Dayot Upamecano, mai shekara 27, zai ci gaba da zama a Bayern Munich har zuwa 2031 bayan da ya kawar da yuwuwar damar tafiya Real Madrid a matsayin kyauta - dan wasan da ba shi da wani kwantiragi a kansa a bazarar nan. (Fichajes)

  10. West Bromwich ta naɗa Ramsey sabon kociyanta, West Brom

    Ramsey

    Asalin hoton, Getty Images

    West Bromwich Albion ta nada tsohon kocin Manchester United, Eric Ramsay a matakin sabon wanda zai horar da ita.

    Mai shekara 33, wanda ya bar aiki a Minnesota United mai buga babbar gasar tamaula ta Amurka ta Major League Soccer ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka biyu da rabi ya maye gurbin Ryan Mason.

    A makon jiya aka sallami Mason, bayan da West Brom ke mataki na 18 a kasan teburin Championship a gasa mai daraja ta biyu a Ingila.

  11. Liverpool za ta kara da Barnsley a FA Cup ranar Litinin, FA Cup zagaye na huɗu

    Arne Slot

    Asalin hoton, Getty Images

    Kociyan Liverpool, Arne Slot ya ce zai buga wasan FA Cup ranar Litinin da fitattun ƴan wasansa da mai buga League One, Barnsley.

    Slot na tsoron kada a kwata abin da ya faru a bara da karamar kungiya, Playmouth ta yi waje da ita sakamakon rashin fita kwai da ƙwarkwata.

    Kociyan ya fayyace mahimmacin FA Cup a wajensa, bayan da aka yi waje road da Liverpool a League Cup a kakar nan.

    Ita kanta Barnsley ta taɓa fitar da Liverpool daga FA Cup da cin 2-1 a Anfield a 2008

  12. Boulter ta shiga cikin ƴan wasan da za a raba jadawalin Australia Open, Ƙwallon tennis

    Boulter

    Asalin hoton, Getty Images

    Katie Boulter ta samu shiga cikin yan wasan da za a raba jadawali a Australian Open awanni tsakani kafin ta kara a zagayen ƴan cike gurbi.

    Sauran ƴan Burtaniya mata da za su buga Grand Slam na farko a bana da za a fara ranar Lahadi a birnin Melbourne, sun haɗa da Emma Raducanu, Fran Jones da kuma Sonay Kartal.

  13. Bradley na Liverpool ya gama buga wasannin bana, Liverpool

    Bradley

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai tsaron bayan Liverpool, Conor Bradley zai yi jinya har karshen kakar bana.

    Mai shekara 22 ya ji rauni a wasan da Liverpool ta tashi ba ci da Arsenal ranar Alhamis a gasar Premier League.

    Haka kuma ana cewa da ƙyar ne idan zai iya buga wa Ireland ta Arewa gasar kofin duniya koda ta samu gurbin, wadda za ta fafata a wasannin cike gurbi ranar 26 ga watan Maris.

    Tawagar Ireland ta Arewa za ta kara a wasan cike gurbin shiga gasar kofin duniya da za a yi a bana a Amurka da Canada da Mexico.

  14. , Daga Jaridu

    Bellingham

    Asalin hoton, Getty Images

    Everton na harin sayen dan bayan Arsenal Ben White, na Ingila mai shekara 28, domin shawo kan matsalar da suke fuskanta a bagaren dama na baya. (Football Insider)

    Borussia Dortmund na sa ido ta ga yadda za ta kaya a kan dan wasan tsakiya na Manchester City Oscar Bobb, dan Norway mai shekara 22, bayan zuwa Antoine Semenyo na Ghana mai shekara 26. (Florian Plettenberg)

    Har yanzu Tottenham na sha'awar sayen dan wasan tsakiya na Atletico Madrid da Ingila, Conor Gallagher, duk da cewa Aston Villa ake ganin ita ta fi damar samun dan wasan mai shekara 25. (Teamtalk)

    Haka kuma Aston Villa na nuna sha'awarta a kan dan gaban Newcastle United, William Osula na Denmark mai shekara 22, bayan da kungiyar ta kasa samun matashin dan gaban Real Madrid Gonzalo Garcia, mai shekara 2, wanda ke tawagar Sifaniya ta 'yan kasa da shekara 21. (Talksport)

  15. Sabalenka ta lashe Brisbane International, Ƙwallon tennis

    Sabalenka

    Asalin hoton, Getty Images

    Wadda take ta daya a duniya, Aryna Sabalenka ta lashe Brisbane International karo na uku, bayan da ta doke Marta Kostyuk.

    Sabalenka ta yi nasara cin 6-4 6-3 kuma cikin minti 79.

    Kawo yanzu ƴar kasar Belarusian ta mayar da hankali kan yadda za ta taka rawar gani a Grand Slam na farko a bana Australian Open da za a fara a Melbourn daga 18 ga watan nan.

  16. Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na 16 jimilla, Spanish Super Cup

    Raphinha

    Asalin hoton, Getty Images

    Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na biyu a jere na 16 jimilla, bayan doke Real Madrid 3-2 a wasan El Clasico na farko a bana da suka kara a Saudiya ranar Lahadi.

    Kenan ƙungiyar Camp Nou ta lashe wasa na 10 a jere a dukkan fafata, rabon da a doke ta tun cikin watan Nuwamba da Chelsea ta samu nasara a Champions League.

    Wasan El Clasico na hudu da a jere da Hansi Flick ya doke Real Madrid - biyu a Super Cup da kuma Copa del Rey -

    Haka kuma Barcelona ce kan gaba a teburin La Liga da tazarar maki hudu tsakani da Real Madrid bayan wasan mako na 19.

  17. Martinelli ya ci ƙwallo uku rigis a karon farko a Arsenal, FA Cup

    Martinelli

    Asalin hoton, Getty Images

    Gabriel Martinelli ya ci kwallo uku rigis a karon farko a wasan da Arsenal ta caskara Portsmouth 4-1 a zagaye na hudu a FA Cup ranar Lahadi.

    Ɗan wasan ya zura na uku da kai, kenan karo na 17 da Gunners mai FA Cup 14 take cin kwallo daga bugun kwana a kakar nan.

    Haka kuma an yi waje road da Manchester United a FA Cup, bayan da Brighton ta yi nasarar cin 2-1 a Old Trafford.

    Wasu daga sakamakon wasannin da aka buga ranar Lahadi - Hull City ta fitar da Blackburn Rovers da cin 4-3 a bugun fenariti bayan da suka tashi ba ci.

    West Ham 2-1 ta doke Quens Park Rangers, Swansea ma ta kai bante da cin West Bromwich 6-5 a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan tashi 2-2.

  18. Man United za ta bai wa Carrick aikin riƙon kwarya, Manchester United

    Carrick

    Asalin hoton, Getty Images

    Michael Carrick na sawun gaba gaba daga cikin wanda Manchester United za ta bai wa aikin rikon kwarya zuwa karshen kakar bana.

    Kawo yanzu ba a kai ga kiransa tattaunawa ba, amma ana cewa tsohon ɗan wasan United mai shekara 44, shi ne za a damkawa aikin horar da kungiyar.

    Carrick ya taɓa jan ragamar wasa uku a United a matakin rikon kwarya, bayan korar Ole Gunnar Solskjaer a 2021.

    Daga ciki ya ci wasa daya da canjaras daya, daga nan Ralf Rangnick ya maye gurbinsa.

  19. Barkanmu da shiga sharhi da bayanan wasanni

    Jama'a barkanmu da shiga shirin sharhi da bayanan wasanni kai tsaye tare da ni Mohammed Abdu Mamman Skipper Tw.

    Za ku iya tafka muhawara a shirin ko bayar da gudunmuwa a BBCHausa Facebook.