Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 18/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba18 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Isra'ila ta gindaya tsauraran sharuɗɗa kan Falasɗinawa masu son yin ibada a Al-Aqsa

    Masallacin Qudus

    Asalin hoton, Getty Images

    Isra'ila ta sake gindaya tsauraran sharudɗa kan Falasɗinawa daga gaɓar Yamma da kogin Jordan da ta mamaye, waɗanda za su halarci sallar Juma'a a massalacin Qudus a wannan wata na Ramadana.

    Falasɗinawa 10,000 ne kawai za a bari su shiga massallacin, kuma wajibi ne su samu takardar izini.

    Hakazalika maza da suka wuce shekara hamsin da biyar, da mata da suka wuce shekara hamsin, da kuma yara yan ƙasa da shekara 13 ne za a bari su shiga.

    Kafin harin da Hamas ta kai na watan Oktoban 2023, dubban ɗaruruwan Falasdinawa ne ke zuwa sallar Juma'a a massalacin na al-Aqsa a watan Ramadan.

  2. Mark Zuckerberg zai gurfana a gaban kotu a Amurka

    Mark Zuckerberg

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaban kamfanin Meta, Mark Zuckerberg

    Shugaban kamfanin Meta, Mark Zuckerberg, zai gurfana a gaban kotu nan ba da jimawa ba a wata shari'a da ake yi a birnin Los Angeles da ke ƙasar Amurka, wadda ta ɗauki hankali, kan yadda amfani da shafukan sada zumuta ke zame wa mutane alakakai.

    Wannan ne karon farko da hamshaƙin mai kuɗin wanda ya ƙirƙiro Facebook zai amsa tambayoyi a wata kotun Amurka, kan yadda shafin Instagram, mallakin Meta ke shafar lafiyar ƙwaƙwalwar matasa da ke amfani da shi.

    Rashin nasara a shari'ar zai zama babbar matsala ga kamfanin, wanda ake ganin hakan zai bayar da damar ɗimbin mutane su yi ta tururuwar shigar da shari'u makamantanta.

    Mai shigar da ƙarar na iƙirarin cewa ta samu matsalar ƙwaƙwalwa ne sakamakon yadda ta jarabtu da amfani da Instagram, da kuma YouTube mallakin google a lokacin da take yarinya.

  3. Tinubu ya sanya hannu kan dokar zaɓen Najeriya ta 2026

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Asalin hoton, X/Bayo Onanuga

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanya hannu kan dokar zaɓen ƙasar ta 2022 da aka yi wa gyaran fuska.

    Hakan na zuwa ne kwana ɗaya bayan majalisar dokokin ƙasar ta amince da dokar bayan kwashe watanni ana tafka muhawara.

    Gyaran dokar ya haifar da zazzafar muhawara a makon da ya gabata bayan wasu al'ummar ƙasar da kuma ƴan majalisa na jam'iyyar adawa sun nuna ƙin amincewa da ɓangaren dokar da ya yi magana kan tura sakamakon zaɓe.

    An riƙa taƙaddama kan matsayar da majalisar ta ɗauka na cewa za a iya amfani da takardar tura sakamakon zaɓe idan aka samu tangarɗar tura sakamakon ta laturoni.

    A ranar Talata majalisar dattijai ta sanya hannu kan dokar duk da hargitsi da aka samu a azauren majalisar.

  4. Mutane 30 sun mutu a Filato bayan shaƙar 'guba'

    Gwamnan jihar Filato Caleb Muftwang

    Asalin hoton, FB/Plateau State Government

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Filato Caleb Muftwang

    Masu haƙar ma'adanai aƙalla 30 ne suka mutu yayin da wasu guda 20 ke kwance a asibiti bayan shaƙar wata iska mai guba da ake zargin 'carbon monoxide' a wani wurin haƙar ma'adanai da ke jihar Filato ta arewa maso tsakiyar Najeriya.

    Lamarin ya faru ne a ranar Talata wurin haƙar ma'adanai a ƙauyen Zuruk a ƙaramar hukumar Wase, kamar yadda mazauna yankin suka shaida wa BBC.

    Ɗaya daga cikin mutanen ƙauyen ya ce masu haƙar ma'adanan na cikin rami a lokacin da hayaƙin gubar ya turnuƙe su.

    "Suna ciki a lokacin da gubar ta turnuƙe, da yawa daga cikin su ba su iya fitowa ba," in ji shi.

    An binne mamatan, waɗanda shekarunsu suka kama daga 20 zuwa 40, jim kada bayan faruwar lamarin.

    Amma an iya ceto mutum 20 waɗanda aka garzaya da su asibiti, sai dai babu ƙarin bayani game da halin da suke ciki.

    Bayanai sun ce jami'an ƙaramar hukumar Wase na shirin zuwa yankin domin tantance abin da ke faruwa.

    Sai dai ayyukan kai ɗauki na fuskantar cikas sanadiyyar matsalar tsaro da ake fama da ita a yankin.

    Har yanzu hukumomi ba su fitar da bayani kan abin da ya haddasa matsalar ba ko kuma adadin mutanen da suka rasu.

  5. Za a binciki shafin Temu kan yadda yake amfani da bayanan ƴan Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kare bayanan sirrin al'umma ta Najeriya ta buɗe bincike kan kamfanin kasuwancin intanet na China wato Temu bisa zargin sayar da bayanan masu amfani da shafin wanda hakan ke nufin karya dokokin sarrafa bayanai mutane .

    Hukumar ta ce damuwa kan yadda kamfanin ke sarrafa bayanai ne ya haifar da binciken, ciki har da sa ido ta intanet da rashin bayyana yadda ake amfani da bayanai, da yada ake tura su ƙetare, da dai sauransu.

    Shugaban hukumar, Vincent Olatunji, shi ne ya bayar da umarnin fara binciken tare da gargaɗin cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.

    Wani mai magana da yawun kamfanin, ya ce za su ci gaba da tattaunawa da hukumar domin warware duk wata damuwa da ta taso.

    A bara ma dai hukumar ta ci tarar kamfanin Multichoice Nigeria naira miliyan 766 bisa karya dokokin kare bayanai, abin da ke nuna tsauraran matakan da take ɗauka kan kamfanoni masu sarrafa bayanan jama’a.

    Hukumar ta ce Temu na sarrafa bayanan kusan mutum miliyan 12.7 a Najeriya, yayin da masu amfani da dandalin a duniya suka kai kai kusan miliyan 70 a kullum.

  6. Haɗewar azumin Musulmi da na Kirista lokaci ɗaya dama ce gare mu - Tinubu

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Asalin hoton, FB/Bola Tinubu

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga Musulmi da Kiristoci su ƙarfafa haɗin kai yayin da lokutan azumin Ramadan da na Kirista wato Lent suka zo a lokaci guda a bana, yana mai cewa hakan wata dama ce ta ƙarfafa zumunci tsakanin mabiya addinai.

    A cikin sanarwar da fadar shugaban ƙasa ta fitar, Tinubu ya bayyana cewa ba kasafai ake samun haɗuwar lokutan ibadar biyu ba, kuma hakan na tunatar da ƴan Najeriya cewa "su al'umma ɗaya ce a wurin ubangiji duk da bambancin addinai".

    Ya ce "ga Kiristoci, lokacin azumi lokaci ne na tuba da kuma koyi da misalin sadaukarwa, yayin da ga Musulmi kuma Ramadan watan ibada ne mai daraja da ke nuna biyayya ga Allah ta hanyar sadaukarwa da ibada da hidima da taimakon juna."

    Shugaban ya buƙaci al'ummar Najeriya “su yi amfani da wannan lokaci wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai da kwanciyar hankali, tare da yi wa ƙasa addu’ar samun ci gaba da tsaro.”

    Ya kuma ja hankalin jama’a su rayu bisa kyawawan koyarwar addinansu.

  7. Tattaunawar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine ta ƙare ba tare da cimma matsaya ba

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Tattaunawar da aka shirya domin kawo ƙarshen yaƙin Rasha a Ukraine ta ƙare ba tare da an samu wata babbar nasara ba, bayan ganawar wakilan ƙasashen biyu tare da Amurka a birnin Geneva.

    Ganawar ta fara ne da dare ranar Talata sannan ta ci gaba na kusan sa’o’i biyu kacal a ranar Laraba.

    Duk da cewa wakilin Amurka Steve Witkoff ya nuna kwarin gwiwa tun farko, bangarorin Rasha da Ukraine sun bayyana tattaunawar a matsayin mai wahala.

    Har yanzu akwai babban giɓi tsakanin Moscow da Kyiv kan muhimman batutuwa kamar yankuna da kuma sharuddan tsagaita wuta a rikicin da ya shafe shekaru huɗu yana gudana.

    Mai shiga tsakani daga ɓangaren Kremlin, Vladimir Medinsky, ya ce duk da wahalar tattaunawar, an gudanar da ita cikin tsari kuma ana sa ran za a sake wata ganawa nan ba da jimawa ba.

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce shawarwarin ba sauƙi saboda bambancin matsaya tsakanin ɓangarorin biyu.

  8. Shugaban Turkiyya ya yi watsi da matakin Isra'ila na amincewa da Somaliland

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan ya ƙi amincewa da matakin Isra’ila na amincewa da Somaliland, yana mai gargadin cewa hakan ba zai amfani Afirka ko yankin ba.

    Ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai tare da firaministan Habasha, Abiy Ahmed, a ranar 17 ga Fabrairu 2026.

    Erdoğan ya jaddada cewa yankin ƙahon Afrika bai kamata ya zama filin fafatawar ƙasashen waje ba, yana mai cewa ƙasashen yankin su ne ya kamata su warware matsalolinsu da kansu.

    A nasa ɓangaren, Firaminista Abiy ya buƙaci Turkiyya ta mara wa ƙasarsa baya wajen neman samun hanyar shiga teku, yana mai cewa bai dace ba ƙasa mai yawan jama’a sama da miliyan 130 ta ci gaba da kasancewa ba ta da mashigar ruwa ba.

    Ya ce Habasha na kira ga Turkiyya ta yi amfani da tasirinta na diflomasiyya domin taimaka mata cikin lumana wajen samun damar shiga teku, yana mai ƙara da cewa sun yi tattaunawa mai zurfi da shugaban Turkiyya kan wannan batu kuma suna godiya da goyon bayan da ya nuna.

  9. Ana samun ɓaraka a jam'iyyar APC a Kano

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani taron hada kan jam’iyyar APC da aka gudanar a jihar Kano a jiya ya bar baya da ƙura.

    An gudanar da taron ne da shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da kuma manyan jiga-jigar jam’iyyar na jihar, inda aka tattauna abubuwa da dama.

    A wajen taron ne shugaban jam’iyyar na ƙasa ya tabbatar da cewa, “za a yi aiki da tsarin rabon shugabanci kashi 60 da kashi 40,” inda ya ce rabon zai kasance tsakanin sababbin masu shigowa jam’iyyar da kuma waɗanda aka tarar tun farko.

    Bayan haka ne wani bidiyo ya bazu a shafukan sada zumunta inda aka ga Alhassan Ado Doguwa cikin fushi yana cewa Sanata Kawu Sumaila da Abdullahi Tijjaniya Muhammad Gwarzo “ba za su juya siyasar Doguwa da Tudun Wada yadda suke so ba.”

    Na baya-bayan nan shi ne wanda ya ta so bayan wani zama da jiga-jigan jam'iyyar suka yi da gwamnan Abba kwana guda kafin a ba shi tutar jam'iyyar.

    Bayan kammala taron mikawa gwamnan tutar jam'iyyar APC sai ga Sanata Kawu a wani bidiyo yana bai wa Hon Doguwa shawara a wani salon jirwaye mai kamar wanka. ‎

    Masu lura sun ce wannan musayar saƙonni ta bidiyo na nuna cewa har yanzu rikicin bai lafa ba.

    Masu sharhin siyasa na cewa siyasar Kano, wadda ake yi wa lakabi da “siyasar Kano sai Kano,” na iya shiga mawuyacin hali idan shugabannin jam’iyyar ba su haɗa kai ba.

  10. Jiragen saman Turai sun fara jigila zuwa Venezuela tun bayan hamɓatar da gwamnatin Maduro

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    A karon farko tun bayan da Amurka ta hambarar da gwamnatin shugaba Nicolas Maduro, Jiragen saman kasashen Turai sun koma zirga zirga a Venezuela.

    A jiya Talata jirgi daga Madrid ya sauka a Caracas.

    Hakan dai ya biyo bayan matakin da hukumar kare haduran jiragen sama ta tarayyar Turai ta dauka na ci gaba da zirga zirgar jiragen a sararin samaniyar Venezuela.

    Jiragen saman kasashen Turai da dama sun soka bi ta sararin samaniyar Venezuela tun a karshen shekarar data gabata bayan matakin da Trump ya dauka akan shugaba Maduro.

  11. Ƙarfa-ƙarfa aka mana wajen amincewa da sassan dokar zaɓe - Tambuwal

    ...

    Asalin hoton, Aminu Waziri Tambuwal/Facebook

    Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya zargi shugabancin Majalisar Dattawan Najeriya da yin ƙarfa-ƙarfa wajen amincewa da wani sashe na dokar zaɓe ba tare da yin gyara ba, yana mai cewa an yi hakan ne duk da adawar ɓangaren marasa rinjaye.

    A hirarsa da BBC, Tambuwal ya ce hatsaniya ta ɓarke ne a zauren majalisa sakamakon yadda aka ƙi amincewa da buƙatar ‘yan adawa na a sake duba sashen dokar.

    A cewarsa, abin da aka fara gabatarwa shi ne buƙatar hukumar zaɓe ta sauya kwanakin bayar da sanarwa daga kwana 360 zuwa 300 domin daidaita jadawalin da ya faɗo a lokacin azumin shekara mai zuwa.

    Ya ƙara da cewa, “Karfa-karfa aka mana wajen amincewa da wani sashe na dokar zaɓe,” yana mai cewa bayanan da suka samu sun nuna shugabannin majalisun biyu da kwamitocin daidaito sun zauna tare da cimma matsaya inda aka fi karkata ga abin da majalisar dattawa ta amince da shi.

    Tambuwal ya ce "a lokacin ne muka nuna rashin amincewa" inda ya ce dole ne a bari a yi zaɓe a fili domin kowa ya bayyana matsayinsa."

    Ya kuma jaddada cewa " Kuma muna ganin hakan hakan zai ba da wata hanya ta yadda za a iya yin magudin zabe wanda shi ake kokarin a kaucewa

    Ce-ce-ku-ce kan dokar zaɓe a Najeriya na ci gaba da ɗaukar hankali, musamman bayan hatsaniyar da ta taso a zaman haɗin gwiwar majalisun biyu kan batun bayyana sakamakon zaɓe ta rubutu a wuraren da babu intanet, lamarin da ya ƙara rarraba kawuna tsakanin ɓangarorin siyasa.

  12. Neman mu miƙa wuya ga shirin zaman lafiya na Trump ba daidai ba ne – Zelensky

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky, ya ce nanata cewa kasarsa ta mika wuya ga batun zaman lafiya da Donald Trump, ke yi ba daidai ba ne.

    Mr Zelensky, ya shaida wa wata kafar yada labarai cewa yana fatan dai duk dabara ce hakan da Trump din ke yi.

    A baya bayannan sau biyu shugaban na Amurka na cewa ya ragewa Ukraine ta tabbatar da an samu nasara a tattaunawar zaman lafiyar da ake a Geneva ba tare da ambaton Rasha ba.

  13. MDD ta ƙaddamar da neman tallafin dala biliyan 1.6 domin taimakon 'yan Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya tare da ƙungiyoyi abokan hulɗa 123 sun ƙaddamar da neman gudummawar dala biliyan 1.6 domin taimaka wa miliyoyin yan ƙasar Sudan da suka tsere daga ƙasarsu domin tsira da rayukansu.

    Wannan na da nufin kai agajin gaggawa ga kusan ‘yan Sudan miliyan 5.9 da ke gudun hijira a ƙasashe bakwai makwabta da suka hada da Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya da Chadi da Masar da Habasha da Libyia da Sudan ta Kudu da Uganda.

    Daraktan yankin Gabas da Kudancin Afirka na hukumar, Mamadou Dian Balde, ya shaida wa manema labarai a Geneva cewa rikicin Sudan shi ne mafi girma da ya raba jama’a da muhallansu a duniya a yanzu,.

    Ya kuma ce shine mafi muni a fannin jin ƙai, yana kuma faruwa ne a lokacin da ake fama da ƙarancin kuɗaɗen tallafi a duniya fiye da kowane lokaci cikin shekaru da dama.

    Ya buƙaci ƙasashen duniya su ƙara tallafin kuɗi domin hana ƙara tabarbarewar rayuwar iyalan da rikicin ya raba da muhallansu.

  14. Mun gano China ta yi gwajin makamin nukiliya - Amurka

    Nukiliya

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani babban jami'in Amurka ya gabatar da wasu bayanai da ke tabbatar da cewa China ta gudanar gwajin makamin nukiliya a asirce.

    Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka, Christopher Yeaw, ya ce Chinan ta gudanar da gwajin ne a wata cibiya a Kazakhstan kusan shekara shida da suka gabata kamar yadda bincike ya nuna.

    Wakilin BBC ya ce a watan Oktoban shekarar da ta gabata shugaba Trump ya yi wani rubutu yana mai ikirarin cewa saboda wasu kasashen na gwajin makamin nukiliya ya bayar da umarnin fara gwajin makaman nukiliya na Amurka. Kasar China wacce a baya ta rattaba hannu kan yerjejeniyar hana gwajin makaman nukiliya, ta yi watsi da ikirarin cewa ta gudanar da gwajin makamin nukiliya tare da zargin Amurka da kokarin fara nata gwajin.

  15. Gargaɗin da Najeriya ta yi wa 'yan kasarta kan shiga yaƙe-yaƙe a ƙasashen waje

    ...

    Asalin hoton, Anadolu Agency via Getty Images

    Najeriya ta gargadi 'yan ƙasarta a kan shiga yake-yake a wasu kasashen bayan wani rahoto da ya fito da ke cewa an yaudari wasu 'yan kasar inda suka shiga yakin da Rasha ta ke yi a Ukraine.

    Cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta bayyana matukar damuwarta a kan yadda ake kara samun 'yan Najeriya da ake dauka aiki ba bisa ka'ida ba domin su je su yi yaƙi a wasu kasashen.

    Rahoton wanda aka wallafa a makon da ya gabata wanda wasu masu bincike suka gudanar kan sojojin haya na Rasha, ya ce rundunar sojin Rasha ta dauki 'yan Najerya akalla 36 aiki domin su yi yaki a Ukraine inda aka kashe mutum biyar daga cikinsu.

    Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce,"Yawancin 'yan Najeriyar da aka dauka irin wannan aiki an tura su fagen daga bayan an yaudaresu da cewa za a ba su aiki a rundunar sojin Rasha."

  16. Australia ta hana ɗan ƙasarta da ke da alaƙa da ƙungiyar IS shiga ƙasar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Australia ta hana wani ɗan ƙasarta da ake dangantawa da ƙungiyar IS shiga ƙasar na tsawon har shekaru biyu.

    Mutumin na cikin mutane 34 mata da yara ‘yan Australia da suka yi ƙoƙarin komawa gida bayan an sake su daga wani sansani a Syria a farkon makon da ya gabata, amma jami’an Syria suka dakatar da su saboda abin da suka kira dalilan fasaha.

    Ministan harkokin cikin gida, Tony Burke, ya ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar hukumomin tsaro, yana mai cewa sauran mutane 33 ba su kai matakin doka da zai sa a hana su shiga kasar ba.

    Gwamnatin da ke Canberra ta ƙi taimaka musu su dawo, inda ake zaton su matan aure ne, zawarawa da kuma ‘ya’yan mayaƙan IS. A cikinsu akwai yara 23.

    Firaministan ƙasar, Anthony Albanese, ya jaddada cewa waɗannan iyalai ba za su samu tallafin gwamnati domin dawowa kasar ba.

    Ya ce waɗannan mutane su ne suka zaɓi tafiya ƙasashen waje domin haɗa kansu da wata akida mai tsauri wadda ke ƙoƙarin rusa tsarin rayuwar ƙasar.

    Sai dai masana shari’a sun gargadi gwamnati cewa tana da alhakin bai wa ‘yan ƙasarta damar komawa gida.

    Mutanen sun kasance suna cikin sansanin al-Roj camp da ke arewacin Syria, ɗaya daga cikin sansanoni da dama da aka tsare ‘yan Australia tun 2019 bayan an kori mayaƙan IS daga sansaninsu na ƙarshe a ƙasar.

  17. Ghana ta gayyaci jakadan Rasha kan zargin yaɗa bidiyon batsa

    .....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar harkokin wajen Ghana ta gayyaci jakadan Rasha da ke Accra, Sergei Berdnikov, domin yin bayani kan zargin wallafa hotuna da bidiyoyin batsa na matan Ghana ba tare da yardarsu ba.

    A cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar ranar Talata 17 ga Fabrairu, ta ce an gayyaci jakadan ne bisa umarnin ministan harkokin wajen ƙasar domin ya yi bayani kan halayen wani “da ake zargin ɗan Rasha ne” da ake dangantawa da wallafa bidiyoyin da suka bazu.

    Gwamnatin ta bayyana matuƙar ɓacin ranta kan abin da ta kira “mummunan hali” na mutumin, tana mai cewa hakan ya karya dokokin Ghana.

    Ta kuma ce hukumomi na neman haɗin kan Rasha domin ganin an yi wa waɗanda abin ya shafa adalci.

    Sanarwar ta ce jakadan ya amince cewa an take sirri da mutuncin waɗanda abin ya shafa, kuma ya yi nuni da cewa lamarin na da alaƙa da manyan batutuwan laifukan intanet.

    Ya kuma bayyana shirye-shiryen Moscow na ba da haɗin kai a binciken.

  18. Wane horo sojojin Najeriya za su samu daga dakarun Amurka?

    ..

    Asalin hoton, getty images

    Karo biyu a cikin wannan wata na Fabarairun 2026 aka tabbatar da isar dakarun Amurka a Najeriya.

    A farkon watan ne shugaban dakarun Amurka da ke a nahiyar Afirka (Africom), Dagvin Anderson ya tabbatar da cewa Amurka ta tura wata kwarya-kwaryar tawagar sojin Amurka zuwa Najeriya.

    Sai kuma ga shi a ranar Litinin shalkwatar tsaro ta Najeriya ta tabbatar da isar sojojin Amurka 100 zuwa Najeriya.

    Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ƙasar ta fitar ta hannun daraktan yada labaranta Manjo Janar Samaila Uba, ta ce tuni rukunin farko na sojojin Amurkan da ya ƙunshi dakaru 100 suka sauka a filin jirgin sama da ke Bauchi a arewa maso gabashin ƙasar.

    A makon da ya gabata ne Amurka ta sanar da ahirin tura sojoji 200 zuwa Najeriya domin horas da dakarun ƙasar dabarun yaƙi da ƙungiyar masu tayar da ƙayar baya.

  19. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.