KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwaftan ƙasashe da kuma sauran sassan duniya na ranar Asabar 21 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Sakataren sojin kasan Amurka zai yi murabus

    Amurka

    Asalin hoton, Reuters

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito daga Mujallar Wall Street cewa ana sa ran Sakataren Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka, Dan Driscoll, zai yi murabus kafin ƙarshen shekara, bayan watanni ana samun takun-saka tsakaninsa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth.

    Mujallar Wall Street Journal ta wallafa rahoton ne bisa bayanan wasu mutane da ke da masaniya kan dambarwar.

    Sai dai Reuters ta ce har yanzu ba ta samu damar tabbatar da rahoton da kanta ba.

    Idan aka tabbatar da murabus ɗin Driscoll, hakan zai sa Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka ta kasance ba tare da shugaba da Majalisar Dattijan Amurka ta tabbatar da nadinsa ba, a daidai lokacin da Washington ke ci gaba da yaƙi da ta ƙaddamar tare da Isra’ila kan Iran, wanda yanzu ya shafe kusan wata shida.

  2. APC ta nada Abdulaziz Yari Darakta-Janar na yakin zaben Tinubu

    Yari

    Jam’iyyar APC ta kafa Kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa, inda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, ya kasance Darakta Janar (DG) na kwamitin.

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima za su kasance shugaba da mataimakin shugaban kwamitin, sannan Gwamna Hope Uzodimma kuma zai yi aiki a matsayin sakataren kwamitin.

    A cikin tsarin kwamitin, an haɗa manyan jami’an jam’iyyar da gwamnati domin jagorantar shirye-shiryen yaƙin neman zaɓen da ake tunkarar zaɓen Janairu 2027.

    Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin da su yi aiki tukuru domin ganin APC ta samu nasara a zaɓen.

  3. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Asabar a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.