Sojojin Sudan ta Kudu na ficewa daga babban birnin ƙasar Juba

Asalin hoton, Getty Images
Akwai rahotanni da ke nuna cewa sojojin gwamnatin Sudan ta Kudu na ficewa daga babban birnin ƙasar, Juba, suna nufar arewa zuwa Jihar Jonglei, inda aka shafe kwanaki ana fafatawa da dakarun ‘yan adawa.
A jiya, babban ƙungiyar ‘yan adawa masu ɗauke da makamai a ƙasar, wato SPLA-IO, ta bayyana cewa ta ƙwace wani muhimmin gari a wani sabon farmaki da take cewa an ƙaddamar da shi ne domin matsawa zuwa Juba.
Sai dai hukumomin yankin sun ce sun fatattaki ƴan ƙungiyar SPLA-IO.
Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya ƙara ƙamari ne bayan da aka tsare shugaban ƙungiyar ‘yan adawa, Riek Machar, a gidan yari tare da gurfanar da shi a gaban kotu a watan Maris na bara.
Ana tuhumar Machar da cin amanar ƙasa da wasu manyan laifuka, kuma har yanzu yana tsare a hannun gwamnati.









