KAI TSAYE, Afcon 2025/29: An je hutu Masar 0-0 Najeriya
Wasan neman mataki na uku tsakanin Masar da Najeriya a gasar cin kofin nahiyar Afirka da Morocco ke karɓar bakunci 2025/26
Taƙaitattu
- Wa zai yi na uku a Afcon tsakanin Masar da Najeriya ranar Asabar?
- Afcon: Za a buga wasan karshe ranar Lahadi tsakanin Senegal da Morocco
- Ko Osimhen ne ginshiƙin tawagar Najeriya?
- Morocco ce ta fitar da Najeriya a zagayen daf da karshe da 4-2 a bugun fenariti
- Sakamakon wasannin Gasar Kofin Nahiyar Afirka 2025
- Masar ta yi rashin nasara a hannun a hannun Senegal a daf da karshe 1-0
- Latsa nan domin samun labarin wasanni a tasharmu ta WhatsApp
- Brahim Diaz na Morocco ne kan gaba a cin ƙwallaye mai biyar a raga
- Za ku iya tafka muhawara kai tsaye a BBCHausa Facebook
Rahoto kai-tsaye
Mohammed Abdu
, Masar 0-0 Najeriya

Asalin hoton, Getty Images
Ɗan wasan Masar, Emam Ashour yana taka leda duk inda ka duba shi zaka gani yana ta kai komo a wasan san.
, Masar 0-0 Najeriya
Mohamed Salah na Masar ya samu bugun tazara
Gooool Najeriya ta ci ƙwallo, Paul Onuachu

Asalin hoton, Getty Images
An soke ƙwallon da Onuachu ya ci bayan da aka duba VAR, kuma Akor ne ya buga shi ne ta bugi keyar Onuachu
, Masar 0-0 Najeriya
Masar ta kara kai kora daga ɓangaren dama an kuma bugo ƙwallon sama, amma ta yi yawa ta fita wajen filin. bugun falan ɗaya ga Nageriya.
, Masar 0-0 Najeriya
Har yanzu dai Masar ta fi riƙe ƙwallo fiye da Najeriya a wasan neman mataki na uku da na huɗu a Afcon, saura minti 15 a je hutu, banda karin lokaci.
, Masar 0-0 Najeriya
Masar ta bugo ƙwallo daga ɓangaren dama a lokacin da mai tsaron ragar Najeriya, Nwabble sai Mohamed Salah ya taɓa ƙwallo amma dai daga baya ba ta zama haɗari ba.
, Masar 0-0 Najeriya
Masar sun fi riƙe ƙwallon da rabawa a wasan nan na neman mataki na uku da na huɗu a Afcon
Senegal ce ta fitar da Masar da cin 1-0 a daf da karshe.
Mai masaukin baki Morocco ce ta yi waje da Najeriya a bugun fenriti 4-2, bayan da suka tashi 0-0.
, Masar 0-0 Najeriya
An yi minti 20 da take leda kuma Zizo na Masar ya ja ƙwallo daidai da fita waje daga Najeriya ya taɓa ta zama ƙwana, bai ji daɗin abinda ya faru ba, so ya yi ƙwalon ta faɗa ragar Super Eagles.
, Masar 0-0 Najeriya
Masar ta kai kora da ƙwallo a sama zuwa wajen Mostafa Mohamed, wanda ya yi kokarin tarewa da kirji amma sai ƙwallo ya taɓa hannusa, an kuma hura.
, Masar 0-0 Najeriya
Masar ta fara wasa tun daga mai tsaron gidanta zuwa yan baya ta kai ga Salah shi kuma ya buga zuwa cikin da'ira ta 18 ta Nageria, amma Nwaballi ya ankara ya yib sauri ya sa kafa ya buge ƙwallon.
, Masar 0-0 Najeriya
Akor Adams ya yi kokarin buga ƙwallo daga ɓangaren hagun fili, amma ba ta yi zafi ba an tare ta cikin ruwan sanyi.
, Masar 0-0 Najeriya
Har yanzu dai wasan bai ɗauki zafi ba, kuma ba a fara kai hare-hare masu zafi ba, an fi yin ƙwallon daga tsakiyar fili, tsakanin ƴan wasan Masar da na Najeriya.
, Masar 0-0 Najeriya
Ana gyaran tuta ta kusurwar fili, bayan Emam Ashour na Masar, wanda ya yi kokarin fitar da ƙwallo kada ta je kwana sai ya tuge tutar, amma yanzu an gyara za a ci gaba da wasan neman mataki na uku da na hudu a gasar cin kofin Afirka a Morocco.
, Masar 0-0 Najeriya
An buga kawana an kuma fitar da ƙwallon daga gidan Masar, amma yanzu dai Najeriya za ta yi fifa gidan Masar - har yanzu wasan bai ɗauki zafi ba.
, Masar 0-0 Najeriya
Chukwueze na Najeriya ya kai kora gidan Masar amma ƙwallo ta je kwana.
, Masar 0-0 Najeriya
Trezequet ya bugo kwallo amma mai tsaron raga ya kama daga gefen hagu ba wani haɗari.
An fara wasa Masar da Najeriya, Masar 0-0 Najeriya
An fara wasan neman mataki na uku da na huɗu a gasar cin kofin nahiyar Afirka tsakanin Masar da Najeriya da ake yi a Morocco.
, Masar 0-0 Najeriya
Ƴan wasa na daf da take leda suna cikin fili ana taken kasashen biyu daga nan kowa ya kama guri ya zauna a fara wasan neman mataki na uku a gasar cin kofin Afirka da ake yi a Morocco.
Karo na biyu tsakaninsu a gasar da Morocco ta shirya, Afcon Morocco 2025/26
Wannan ce haduwarsu ta biyu a gasar da Morocco ta dauki nauyin shiryawa, bayan ta farko a shekarar 1988.
Daga cikin haduwarsu tara a gasar AFCON, takwas sun kasance ne a matakin rukuni.
A shekarar 1976 sun hadu a zagaye na biyu na rukuni, yayin da sau bakwai suka kara a tsarin rukuni.
A shekarar 1963, Masar ta tsallaka zagaye, yayin da a shekarar 1988 da 1990 Najeriya ta samu nasarar wucewa zagayen gaba a kan Masar.
Gaba ɗaya, kasashen biyu sun hadu sau 20, inda Najeriya ta yi nasara takwas, Masar ta ci shida, yayin da shida suka kare da canjaras
