Labarin wasanni daga 13 zuwa 19 ga watan Satumbar 2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Asabar 13 zuwa 19 ga watan Satumbar 2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Zakarun Turai : Haalanda ya sake kafa tarihi bayan Man City ta doke Napoli 2-0

    Hwallon da Haaland ya ci

    Asalin hoton, Getty Images

    Erling Haaland ya sake kafa wani tarihin inda ya kasance danwasan da ya fi sauri wajen cin kwallo 50 a gasar Zakarun Turai, inda Manchester City ta doke Napoli da ci 2-0.

    Haaland ya kafa wannan tarihi ne da wasa 49, inda ya zura kwallon da ta ba shi wannan dama a minti na 56 bayan an koma daga hutun rabin lokaci, a wasan da aka zaku da ganin tsohon danwasan Man City Kevin de Bruyne wanda ya koma Napoli, sai dai an fitar da shi bayan minti na 26.

    De Bruyne wanda ya bar City a bazara ba tare da sonshi ba bayan ya dauki kofi 16 a cikin shekara goma, ya fita daga wasan ne kasancewar an ba wa dan bayansu kuma kyaftin, Giovanni di Lorenzo katin kora, saboda ya yi wa Haaland keta a matsayinsa na bango na karshe a baya a don haka kociyansu Antonio Conte ya fitar da shi ya shigo da dan baya domin karfafa bayan.

    Jeremy Doku ne ya ci wa Manchester City kwallon ta biyu a minti na 65 a karawar da ke zaman ta farko ta kungiyoyin biyu a gasar ta Zakarun Turai.

    A sauran wasannin na Alhamis Eintracht Frankfurt a gida ta ci bakinta Galatasaray 5-1, kamar yadda ita ma Sporting Lisbon ta lallasa bakinta Kairat Almaty 4-1.

  2. Zakarun Turai: Barcelona ta bi Newcastle har gida ta caskara ta 2-1

    'Yanwasan Barcelona

    Asalin hoton, Getty Images

    Barcelona ta bi Newcastle har gida ta casa ta da ci 2-1 a gasar Zakarun Turai matakin lig, inda Marcus Rashford ya ci duka kwallayen biyu na Barca.

    Da wannan bajinta danwasan da Man United ta ba Barcelona aro zuwan karshen kakar bana, da sharadin sayensa idan har ya yi kokari ya kasance na biyar a Barcelona da a tarihi ya ci kwallo sau biyu a wasansa na farko na gasar ta Zakarun Turai.

    Sauran da suka kafa wanna tarihi su ne Txiki Begiristain a 1993, da Cristian Tello a 2012, da Robert Lewandowski a 2022 da kuma Joao Felix a 2023.

    Anthony Gordon ne ya ci wa mai masaukin bakin kwallonta daya ana minti 90 da wasa.

  3. Zakarun Turai : Leverkusen ta yi canjaras 2-2 da Copenhagen

    'Yanwasan Bayer Leverkusen na mruna

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayer Leverkusen ta kwaci maki daya a wasanta na farko na gasar Zakarun Turai inda ta yi canjaras 2-2, 1-1 da Copenhagen mai masaukinta a karawar ranar Alhamis din nan.

    Copenhagen ta kama hanyar nasara a wasan na gidanta da ci 2-1, to amma sai kungiyar ta gamu da sammatsi inda danwasanta Pantelis Hatzidiakos ya ci kansu a minti na 91 ana dab da shirin nade tabarmar wasan, inda ya zama 2-2.

    Mai masaukin bakin ta dauka za ta yi nasara a karawar bayan da Robert Silva da ya shigo daga baya ya ci musu kwallo ta biyu a minti na 86.

    Tun da farko kungiyar kungiyar ce ta fara daga raga minti tara da shiga fili lokacin da Jordan Larsson - dan tsohon danwasan Celtic da Barcelona Henrik ya ci musu.

    A minti na 82 ne Leverkusen ta ci farko kwallon farko aka zama 1-1 ta hannun Alex Grimaldo.

    Bayer Leverkusen ta kai matakin kungiyoyi 16 a gasar ta Zakarun Turai a bara kafin ta sha kashi da ci 5-0, jimilla a hannun Bayern Munich.

    A wasannin gaba na rukuni na gasar ta Zakarun Turai Copenhagen za ta je Azerbaijan inda za ta kara da Qarabag ranar 1 ga wata mai zuwa Oktoba, yayin da ita kuwa Leverkusen za ta kasance a gida inda za ta karbi bakuncin PSV Eindhoven a wannan rana, ita ma.

  4. Club Brugge ta caskara Monaco 4-1 a gasar Zakarun Turai

    Hoton Hans Vanaken

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Hans Vanaken ya yi wa Club Brugge sama da wasa 500

    Kungiyar Club Brugge ta fara wasanninta na gasar Zakarun Turai ta kakar bana (2025-26), da sa'a bayan da ta caskara Monaco da ci 4-1.

    Kwallo uku da mai masaukin bakin ta zura wa bakin nata a tsakanin minti goma a yau Alhamis, sun karya lagon Monaco zuwa lokacin da aka tafi hutun rabin lokaci a filin na Jan Breydelstadion.

    Nicolo Tresoldi, da Raphael Onyedika da kuma Hans Vanaken su ne suka ci wa kungiyar ta Belgium kwallayen a zibin farko.

    Matashin danwasan Faransa Mamadou Diakhon ne ya kara ta hudu a minti na 75 kafin Ansu Fati, ya rama daya a wasan da ke zaman na farko da yake yi wa Monaco a daidai lokacin tashi.

    Minti 17 na farko na wasan sun kasanche masu daukar hankali kan tsohon mai tsaron ragar Liverpool Simon Mignolet, wanda ya koma Club Brugge, inda ya kare fanareti.

    Sannan an ba shi katin gargadi saboda ihu da ya yi wa alkalin wasa, sai kuma aka sauya shi saboda raunin da ya ji a matsatsinsa.

    Monaco, wadda tsohon dan bayan Tottenham Eric Dier, ya yi mata kyaftin ta dan farfado bayan hutun rabin lokaci amma ba ta iya razana Nordin Jackers, wanda ya maye gurbin Mignolet ba.

    Club Brugge da ta kai matakin 'yan 16 a gasar ta Zakarun Turai a bara za ta kara da Atalanta ranar 30 ga watan nan na Satumba, yayin da Monaco za ta karbi bakuncin Mancity a wasanta na gaba.

  5. Son ya ci kwallo uku rigis a wasan da sabuwar kungiyarsa LAFC ta yi nasara

    Denis Bouanga (a hagu) da Son (a dama)

    Asalin hoton, Getty Images

    Son Heung-min ya yi bajintar farko ta zura kwallo uku rigis a babbar gasar kwallon kafa ta Amurka (Major League Soccer), a wasan da sabuwar kungiyarsa ta Los Angeles FC ta lallasa Real Salt Lake 4-1 a ranar Laraba.

    Danwasan na Koriya ta Kudu ya ci kwallo biyu a cikin minti 16 na farkon wasan, kafin ya zura ta ukun, inda wasan ya kasance 3-1 a minti 82.

    Hakan ya sa zuwa yanzu danwasan mai shekara 33, ya zura jimillar kwallo biyar a wasa goma da ya yi wa sabuwar kungiyar tasa tun bayan da ya bar Tottenham bayan zaman shekara goma, inda koma Amurka a watan da ya gabata.

    Son ya bayyana yadda ya ji da wannan bajinta ta zura kwallo uku rigis a wasa daya, ''Babban abin farin ciki ne yin wannan bajinta- ta farko (cin kwallo uku rigis) a MLS, ina matukar farin ciki da godiya ga kowa.

    ''Ko da ban ci kwallo ba, ina jin dadin yi wa wannan kungiya wasa da samun sakamako mai kyau a wasan waje.

    "Ina jin dadin zamana a nan, da kowane atisaye da kuma kowane wasa." A cewar Son.

    Nasarar ta LAFC ta daga kungiyar zuwa ta hudu a tebur a gaban kungiyar Seattle Sounders, kuma suna da sauran wasa shida da suka rage musu a gasar.

  6. Ko De Bruyne zai rama wa Man City aniyarta a gasar Zakarun Turai?

    Kevin de Bruyne

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester City za ta karbi bakuncin wani daga cikin fitattun 'yan wasanta na baya wanda zai iya yi mata ta'annati a karawar da za ta fara ta gasar Zakarun Turai ranar Alhamis.

    Wannan dan wasa shi ne Kevin de Bruyne wanda ya ci kofi 16 a cikin shekara goma a City - dan wasan da City ke shirin martaba shi ta hanyar gina mutum-mutuminsa a wajen filin wasa na Etihad.

    Tauraron dan wasan na tawagar Belgium ya bar City lokacin da kwantiraginsa ya kare a watan Yuni, kuma kasancewar ya nuna karara cewa ba shi da niyyar tafiya, ana ganin a yanzu yana shirin kunyata City din a Napoli.

    An yaba da zuwan danwasan mai shekara 34 Naples har ma suna kwatanta shi da zuwan marigayi tauraron Argentina Diego Maradona, wanda har yanzu magoya bayan kungiyar ta Italiya ke martabawa.

    ''Tun bayan Maradona, Napoli ba ta dauki wani tauraron danwasa kamar De Bruyne ba, '' in ji danjarida Vincenzo Credendino da ke zaune a birnin Naples, a tattaunawarsa da BBC.

    ''Maradona ya zo a lokacin da yake kan ganiyarsa, amma shi De Bruyne ya zo ne yana shekara 34.''

    "Abu ne sananne matsayin Maradona a wajen shugaban kungiyar Corrado Ferlaino a shekarun 1980, De Bruyne shi ne irin abin da Maradona ya zama a lokacin a wannan shekarar a wajen mai kungiyar Aurelio de Laurentiis.'' In ji Credendino.

  7. Atletico da Uefa za su yi nazari kan rikicin Simeone a wasan Liverpool

    Ana fitar da kociyan Atletico Madrid Diego Simeone daga fili

    Asalin hoton, Getty Images

    Atletico Madrid za ta gudanar da bincike kan tashin-tashinar da aka yi a wasan Zakarun Turai da Liverpool ta doke ungiyar a Anfield da ci 3-2, inda ake zargin wani cikin jami'an Atletico ya tofa wa magoya bayan Liverpool yawu.

    Alkalin wasa ya bai wa kociyan Atletico Diego Simeone katin kora sakamakon sa-in-sa da wani mai goyon bayan Liverpool abin da ya sa kusa haddasa rikici a kusa da karshen wasan.

    Wani hoton bidiyo ya nuna alamun wani daga cikin jami'an kociyan kungiyar Atletico ya tofa yawu cikin magoya bayan Liverpool a lokacin rikicin wanda ya tashi bayan da kyaftin Virgil van Dijik ya ci wa Liverpool kwallo ta uku da ta yi nasara.

    Ita ma hukumar kwallon kafa ta Turai - Uefa, za ta iya daukar matakin hukunci idan ta kammala duba dukkanin rahotannin da suka kamata a kan rikicin.

    Ita ma Atletico ta gaya wa BBC cewa za ta gudanar da bincike kan lamarin amma ta ce ba za ta yi magana a bainar jama'a ba.

    Lamarin ya kai sai da aka janye kociyan Atletico kar ya yi rigima da wani mai goyon bayan Liverpool da ke yi masa ihu.

    A tattaunawa da shi bayan wasan kociyan na Atletico mai shekara 55 ya nuna nadamarsa kan rigima da magoya bayan na Liverpool - sai dai ya ce miyagun maganganun da suke furta wa ne suka harzuka shi.

  8. Benfica ta naɗa Jose Mourinho kociyanta zuwa 2027

    Jose Mourinho

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Mourinho ya fara aikin kociya shekara 25 baya a Benfica, kafin ya je Uniao de Leiria sannan Porto

    Mourinho, mai shekara 62, ya maye gurbin Bruno Lage, wanda ƙungiyar ta kora bayan da Qarabag ta ba Benfican mamaki da doke ta a gasar Zakarun Turai ranar Talata.

    Tsohon kociyan na Chelsea ya koma aiki ne ƙasa da wata ɗaya bayan da Fenerbahce ta kore shi sakamakon kashi da ƙungiyar ta sha a hannun sabuwar ƙungiyar tasa a wasan neman samun gurbin gasar ta Turai.

    Mourinho ya fara aikinsa na kociya da Benfica a 2000, to amma a lokacin ya jagorance ta ne a wasa goma kawai, ya bar aiki sakamakon saɓani da shugaban ƙungiyar.

    Sabon kwantiragin na Mourinho a Benfica ya haɗa da dama ga shi da ƙungiyar su yanke shawarar rabuwa tsawon wata kaka, har zuwa wa'adin kwana goma bayan kakar nan ta 2025-26.

    Benfica ta kori Lage duk da cewa wasa ɗaya kawai ya yi rashin nasara a dukkanin gasa a bana, kuma yanzu Mourinho ya gaji ƙungiyar da take ta shida a teburin babbar gasar Portugal (Primeira Liga), maki biyar tsakaninta da ta ɗaya, Porto, amma da kwantan wasa ɗaya.

    Wasansa na farko a ƙungiyar da ke birnin Lisbon, shi ne na ranar Asabar inda za su je su kara da AVS ta 17 a tebur.

  9. Chelsea ka iya fuskantar tuhuma kan Sterling da Disasi

    Sterlind da Dasisi

    Asalin hoton, getty

    Kungiyar kwararrun 'yan wasa ta Ingila (PFA) na tattaunawa da Chelsea, kan yadda Chelsea din ta yi wa Raheem Sterling da Axel Disasi, na ware su daga cikin tawagarta.

    A yanzu 'yanwasan biyu ba sa atisaye da tawagar ta Stamford Bridge bayan da kociyan kungiyar Enzo Maresca ya fito fili ya gaya musu cewa ba sa cikin tsarinsa.

    Sterling, mai shekara 30, yana da kasa da shekara biyu da ta rage a kwantiraginsa da Chelsea - a kan albashin kusan fan 325,000-a mako, yayin da kwantiragin dan baya Disasi mai shekara 27 zai kare a 2029.

    Kasancewar dukkanin 'yan wasan biyu sun tafi zaman aro a wasu kungiyoyin a kakar da ta gabata, an sa ran za su bar Chelsea a lokacin kasuwar 'yanwasa ta bazara.

    To amma kuma dukkanninsu suka ci gaba da zama a kungiyar ta Premier, kuma abu ne mawuyaci wani daga cikinsu ya samu shiga tawagar farko da kungiyar kafin watan Janairu lokacin da za a sake bude kasuwar saye da sayar da 'yanwasa.

    Kungiyar ta kwararrun 'yanwasa na son ganin ta tabbatar da Chelsea ta bai wa Sterling da Disasi damar atisaye da tawagarta ta farko - manyan 'yanwasanta duk da cewa ba za ta sa su a wasa ba saboda kar kwazonsu ya ja baya.

    Hukumar kwallon kafa ta duniya, Fifa tana da tsauraran dokoki a kan ware 'yanwasa daga cikin tawagar kungiya - wanda hakan zai iya kaiwa ga tuhumar kungiya da cin mutuncin danwasa, abin da zai iya sa danwasa ya soke kwantiraginsa a kan wannan dalili tare da samun hakkokinsa.

  10. Zakarun Turai: 'Newcastle za ta iya ba Barcelona mamaki'

    'Yanwasan Newcastle da Barcelona

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon danbayan Newcastle United John Anderson yana ganin damar shigar gasar Turai da kungiyar ta yi a baya-bayan nan za ta iya sa su samu nasara a wasansu na farko da za su yi na gasar ta bana ranar Alhamis din nan a filinsu St James' Park da Barcelona.

    A hirarsa da BBC Anderson ya ce : ''Kasancewar yawancin 'yan wasan sun taba taka leda a gasar ta Zakarun Turai a baya lalle wannan zai iya ba su nasara.''

    "Ba wai kamar a ce za su shiga gasar ba ne ba su san abin da ake tsammani daga gare su ba ne - yawancinsu sun san gasar sun taka rawa a wasanninta kuma sun san abin da ake sa rai daga wajensu,'' in ji shi.

    Ya kara da cewa: "Tuni sun yi babban gumurzu da Paris St-Germain a filinsu na St James' Park - inda suka yi nasara 4-1, wanda wannan babban abin karfafa gwiwa ne. Muna fatan abin da za mu sake gani kenan a karawarsu da Barcelona, wadda tana daya daga cikin manyan kungiyoyin Turai.

    "Idan aka kwatanta yadda kungiyar take a baya lokacin da ta kasance a gasar ta Zakarun Turai a karshe, yanzu tawagar ta kara karfi sosai akwai kuma tarin 'yanwasa da Eddie Howe zai zaba ya darje.

    "Nasarar da ta samu ta 1-0 a kan Wolves ita ma ta zo a daidai lokacin da za ta ba kungiyar ta Newcastle kwarin gwiwa." A cewar Anderson.

    Wannan shi ne karo na biyar da kungiyoyin biyu za su hadu a wasannin gasa, inda Newcastle ta yi nasara da ci 3-2 a karawarsu ta farko a watan Satumba na 1997, a lokacin da Faustino Asprilla ya ci kwallo uku gaba daya.

    To amma kuma Newcastle din ta yi rashin nasara a sauran wasanninsu uku na gaba, to amma magoya bayanta suna da kwarin gwiwa a wannan karon.

  11. Mourinho na daf da zama kociyan Benfica

    Mourinho

    Asalin hoton, Getty Images

    Jose Mourinho na daf zama kociyan Benfica, bayan da ta kori Bruno Lage ranar Talata, sakamakon da Qarabag ta yi nasara a kan ƙungiyar Portugal 3-2 a Champions League.

    Shugaban Benfica, Rui Costa ya ce suna fatan sanar da ɗaukar sabon kociya kafin ranar Asabar, inda ake ta alakanta aikin da Mourinho.

    An sanar da BBC cewar Mourinho na tattaunawa da Benfica kan batun komawa horar da tamaula a kasar bayan shekara 21 da ya koma Chelsea.

    Ranar 29 ga watan Agusta Fenerbahce ta kori tsohon kociyan Real Madrid da Inter Milan da Manchester United kwana biyu tsakani da Benfica ta yi waje da ƙungiyar Turkiya a wasan cike gurbin shiga Champions League.

  12. Yamal ba zai buga wasan da Barcelona za ta yi da Newcastle ba a Champions League

    Yamal

    Asalin hoton, Getty Images

    Lamine Yamal ba zai buga wa Barcelona Champions League ba da za ta kara da Newcastle United ranar Alhamis a wasan farko a cikin rukuni.

    Mai shekara 18 bai yiwa ƙungiyar wasan da ta caskara Valencia 6-0 ba a gasar La Liga ranar Lahadi, sakamakon raunin da ya ji lokacin da ya buga wa Sifaniya wasan shiga gasar kofin duniya.

    Yamal ya buga wa Sifaniya minti 79 a wasan da ta doke Bulgaria 3-0 ranar 4 ga watan Satumba, ya kuma yi minti 73 a karawar da suka caskara Turkey 6-0 kwana uku tsakani.

    Haka kuma shima Alejandro Balde da Gavi na jinya ba za su buga fafatawar ta St James Park ba.

    Frenkie de Jong bai yi wasan da Barcelona ta sharara ƙwallaye ba a ragar Valencia, sakamakon buga wa Netherlands tamaula, amma an je da shi Ingila domin fuskantar Newcastle.

    Barcelona ce ta lashe La Liga a bara da kai wa zagayen daf da karshe a Champions League, wadda Inter Milan ta yi waje da ita daga gasar.

  13. Partey bai amince da tuhamar zargin fyaɗe da ake masa ba

    Partey

    Asalin hoton, Reuters

    Tsohon ɗan wasan Arsenal, Thomas Partey bai amince da tuhumar zargin yiwa mata biyu fyaɗe ba da cin zarafin wata mata.

    Ɗan kasar Ghana bai amince da tuhumar zargin fyaɗe ga mata biyar ba da cin zarafin wata matar, bayan da ya gurfana a gaban wata kotu a Southwark.

    Ya aikata laifin da ake zarginsa tsakanin 2021 zuwa 2022 lokacin da mai shekara 32 ke buga Premier League.

    Kwana huɗu da barin Arsenal aka fara tuhumarsa, bayan da yarjejeniyarsa ya kare a ƙungiyar Arewacin Landan a karshen watan Yuni.

    An bayar da belin Partey, za kuma ci gaba da saurarar karar ranar 2 ga watan Nuwambar 2026.

    Partey yana taka leda a Villareal ta Sifaniya, ya kuma buga wa ƙungiyar Champions League a karawar da ta yi rashin nasara a hannun Tottenham da ci 1-0 ranar Talata.

  14. Ƙungiyar Barau FC ta ɗauki Kabiru Baita da Dominic Iorfa

    Barau FC

    Asalin hoton, Barau FC

    Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Barau FC ta ɗauki Dominic Iorfa da Alhaji Kabiru Baita, domin aiki cikin shugabanninta. President of Barau FC,

    A wata sanarwa da jami'in yaɗa labaran ƙungiyar Ahmad Hamisu Gwale ya fitar, Dominic Iorfa zai yi aiki a Barau FC a matakin General Manager, yayin da Alhaji Kabiru Baita zai yi mataimakin shugaban ƙungiyar.

    Barau FC tana matakin karshe a teburin Premier ta Najeriya da maki biyu daga wasa huɗu, har yanzu ba ta ci wasa ba, illa dai ta yi canjaras biyu.

    Ranar Lahadi Barau FC za ta karɓi bakuncin Rivers United a wasan mako na biyar a babbar gasar tamaula ta Najeriya.

    Rivers ce ta biyu a kan teburi da maki takwas bayan cin wasa da canjaras biyu.

  15. Gundogan ya godewa Pep Guardiola kan damar da ya bashi a tamaula

    Gundogan

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon kyaftin din Manchester City, Ilkay Gundogan ya godewa Pep Guardiola bayan da ya bashi duk wata damar da yake bukata a fannin tamaula.

    Dan kasar Jamus ya koma Galatasaray a cikin watan nan a matakin mara yarjejeniya, bayan kaka takwas a Etihad da lashe Premier League biyar da Champions League.

    Mai shekara 34 shi ne na farko da Guardiola ya fara saya a 2016 - ya ci kwallo 65 a wasa 358 a kungiyar Etihad.

  16. Watakila Isak ya fara buga wa Liverpool tamaula a Champions League

    Isak

    Asalin hoton, Getty Images

    Koci, Arne Slot ya sanar cewar dan wasan da ta dauka a bana mafi tsada daga Newcastle United, Alexander Isak yana daga cikin wadanda za su fuskanci Atletico Madrid a yammacin nan a Champions League.

    Isak, wanda ya koma Anfield, bai yi wa Liverpool wasan Premier League ba da ta yi nasara a kan Burnly 1-0 ranar Lahadi, inda Slot ya ce baya kan ganiya.

    Liverpool za ta so ta taka rawar gani a bana, bayan makudan kudin da ta kashe wajen sayen sabbin yan wasa, wadda Paris St Germain ta yi waje da ita a bara.

    To sai dai Atletico za ta buga fafatawar ba tare da Julian Alvarez ba, wanda ke jinya.

  17. Mbappe ya ci ƙwallo 50 a Real Madrid tun daga kakar bara

    Mbappe

    Asalin hoton, Getty Images

    Real Madrid ta doke Merseille 2-1 a wasan farko a cikin rukuni a Champions League ranar Talata.

    Kylian Mbappe ne ya ci wa Real ƙwallayen kuma dukka a bugun fenariti - kenan na 50 da ya zura a raga a ƙungiyar.

    Ya yi wannan ƙwazon bayan wasa 64 a Real Madrid, Ronaldo ne kan gabansa wanda ya zura 50 a raga a karawa 54 tun bayan da ya koma ƙungiyar daga Manchester United a 2009.

    Shi kuwa Karim Benzema a wasa 106 ya ci wa Real Madrid ƙwallo 50, yayin da Vinicius Jr a karawa 200 ya samu yin bajintar.

  18. Fifa za ta gwangwaje ƙungiyoyi da maƙudan kudi

    Infantino

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kwallon kafa ta duniya Fifa za ta raba ladan dalar Amurka miliyan 355, wani daga romon da kungiyoyi za su sharba da ya shafi gasar kofin duniya da za a yi a 2026.

    Wannan karon an samu karin kaso 70 cikin 100 daga dalar Amurka miliyan 209 da aka bai wa kungiyoyin, bayan kammala gasar cin kofin duniya da aka yi a Qatar a 2022.

    A karon farko duk kungiyar da ta bar ɗan wasanta ya je ya buga wa kasarsa wasannin neman shiga gasar kofin duniya, za a biya ta diyya mai tsoka.

    Za a fara gasar cin kofin duniya a badi daga 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yuli a Amurka da Mexico da kuma Canada

  19. Man United ta sanar da cin ribar kasuwanci duk da rashin kokarin da take yi a tamaula

    Manchester United ta samu kuɗin shiga da ya kai fam miliyan 666.5 a kakar da ta wuce, duk da rashin kokarin da take yi a fannin tamaula.

    United ta kare a mataki na 15 a teburin Premier League a bara, mataki mafi muni tun bayan 1973/74, wadda ta faɗi daga gasar a kakar.

    Sai dai hulɗar kasuwancin shekara biyar da United ta ƙulla da Snapdragon ya sa ta samu kuɗin shiga da ya kai fam miliyan 333.33, yayin da ta samu karin kuɗi ta kallon wasanninta da ya kai fam miliyan 160.3 zuwa ranar 30 ga watan Yunin 2025.

    Man United

    Asalin hoton, Getty Images

  20. Arsenal za ta taka rawar gani a Champions League a bana - Valverde

    Arsenal

    Asalin hoton, Getty Images

    Arsenal tana daga cikin ƙungiyoyin da za su iya lashe Champions League a bana, in ji kociyan Athletic Bilbao, Ernesto Valverde.

    Ƙungiyar da Mikel Arteta ke jan ragama za ta kara da Bilbao a filin wasa na San Mames a karawar farko a cikin rukuni a Champions League ranar Talata.

    Gunners ta kai zagayen daf da karshe a bara, wadda Paris St Germain ta yi waje da ita daga gasar ta zakarun Turai.

    Bilbao ta samu gurbin shiga Champions League a bana, bayan da ta kare a mataki na huɗu a teburin La Liga a kakar da ta wuce.