Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Harin Amurka da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, 26/04/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran harin Amurka da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, 26/04/2026

Taƙaitattu

  • An fitar da Trump daga ɗakin taro bayan wani ɗanbindiga ya buɗe wuta
  • Yadda jam'iyyun hamayya sama da goma ke neman yi wa Tinubu taron dangi
  • Abin da muka sani kan mutumin da ake zargi da kai wa Trump hari
  • 'Wanda ake zargi ya ce jami'an Trump ya yi niyyar kai wa hari'
  • Kalli bidiyon yadda aka kuɓutar da Trump a lokacin harin
  • Shugabannin duniya na aike wa saƙonnin jaje ga Trump

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Chelsea ta kai wasan ƙarshe a gasar FA

    Enzo Fernandez ne ya ci ƙwallo da Chelsea ta kai wasan karshe a FA Cup, bayan doke Leeds United 1-0 a Wembley ranar Lahadi.

    Ƙungiyar Stamford Bridge ta samu wannan damar kwana huɗu tsakani da korar kociya, Liam Rosenior, saboda kasa samun nasarorin da ake bukata.

    Chelsea, wadda ke fama da koma baya ta yi wannan namijin kokarin karkashin kociyan riƙon kwarya, Calum McFarlane da zai yi aiki zuwa karshen kakar bana.

    Leeds ta sa ran za ta yi wani abun, ganin wasa na uku da ta fuskanci Chelsea da yin nasara 3-1 cikin watan Disamba a Elland Road da yin 2-2 a karawa ta biyu a Stamford Bridge a Premier League a bana.

    Yanzu Dai Chelsea za ta sake komawa Wembley ranar 16 ga watan Mayu, domin buga wasan karshe da Manchester City, wadda ta yi waje da Southampton 2-1 ranar Asabar.

  2. Araqchi zai tattauna da Putin a Moscow

    Kamfanin dillancin labarai na Iran yace ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya nufi Rasha tare da wasu wakilan diflomasiyya domin tattaunawa da Vladimir Putin a birnin Moscow a gobe Litinin.

    Wannan na zuwa ne bayan ziyarar da ya kai wa Sarkin Oman, inda ministan na Iran ya tattauna da shi a Muscat da Sultan Haitham bin Tariq da kuma Ministan harkokin wajen ƙasar Badr Al Busaidi.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, kamfanin ya ce Araqchi ya taɓo batutuwa da dama ciki har da sabon tsarin da za su kawo kan mashigar Hormuz, da tabbatar da cewa ba za a sake kai harin soji ba a mashigar.

  3. Amurka ta kwace jirgin Iran da yakai dala milyan 380

    Wani shafin intanet da ya kware wajen bibiyar jiragen ruwan ƙasashen duniya, yace hotonan tauraron ɗan adam ya nuna yadda wani jirgi mai ɗauke da ɗanyen mai da ya kai darajar dala biliyan 1.05 da ke kan hanyar komawarsa Iran, sojin ruwan Amurka sun kwace shi.

    Masu bibiyar tankokin dakon mai a tekun, sun ƙara da wallafa cewa masu gadin teku sun kwace wani jirgin Iran mai ɗauke da man da ya kai darajar dala miliyan 380 a tekun India, kuma yanzu kamar an karkatar da shi Amurka.

    Har yanzu dai babu cikakkiyar hanyar safarar ɗanyen mai a cikin tekun Gulf, ko kuma babu wani tabbas cewa jirgi zai kai inda ya nufa kalau.

  4. Sojin Isra'ila sun ce an kashe jami'insu ɗaya a kudancin Lebanon

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce an kashe jami'inta a kudancin Lebanon a ranar Lahadi.

    Rundunar ta yi bayani cewa an kashe Sajan Aidan Fox 19, yayin wani faɗa a kudancin Lebanon, yayin da wani jami'i da wasu sojoji uku suka ji munanan raunuka.

    Akwai kuma wani soja ɗaya da ya ji ciwo madaidaici da kuma wani da ya ji ciwon da bai kai ya kawo ba.

  5. Ziyarar Sarki na nan ba fasawa

    An tambayi shugaba Trump ko ziyarar Sarki Charles III da Sarauniya Camilla zuwa Amurka har yanzu tana nan kamar yadda aka tsara.

    Trump ya amsa da cewa "Sarki na nan tafe".

    "Babban mutum ne, muna sa ran ganin shi lokacin ziyarar. mutum ne mai tasiri da ya isa wakilci, mai kuma kaifin kwakwalwa," in ji Trump.

    Sarkin ai magoyin bayansa ne tun da jimawa, in ji Trump.

    "Za mu samu lokaci mu tattauna, kuma zai wakilci ƙasarsa kamar babu wanda ya taɓa yin abin da ya yi," Trump ya ce.

  6. Araqchi ya isa Islamabad bayan barin binrin Muscat.

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqhchi ya isa birnin Islamabad daga ƙasar Oman.

    A cewar IRNA, kamfanin dillancin ƙasar Iran, ya ce Mista Araqhchi ya samu tarba mai kyau daga ministan cikin gidan Pakistan lokacin da ya sauka a filin jirgin sansanin sojin sama na Nur Khan.

    Bayanai na cewa Araqhchi ya koma Pakistan ne domin tattauna tuntuɓar da ya yi a yankin da ƙasar Pakistan.

    Mr. Araqhchi ya gana da sarkin Oman Haitham bin Tariq a birnin Muscat.

    Wannan ce ziyarar Mista Araqhchi ta biyu zuwa Islamabad cikin kwana biyu.

  7. Arahgchi ya tattauna da ministocin wajen Saudiyya da Qatar

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Arahgchi ya tattauna ta waya da takwarorinsa na ƙasashen Saudiyya, Faisal bin Farhan da na Qatar Mohammed bin Abdulrahman.

    Cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Iran ta fitar, ta ce Mistan Arahgchi ya bayyana wa takwarorin nasa matsayin Iran kan yunƙurin kawo ƙarshen yaƙin Iran.

    A lokacin yaƙin na baya-bayan nan, Iran ta sha kai wa Qatar hari da wasu sassa a Saudiyya, da kuma sansanonin sojin Amurka a waɗannan ƙasashe.

  8. An kama jagororin adawar Chadi

    Hukumomin Chadi sun kama jagororin adawar Chadi guda tara.

    Kakakin ƙawancen jam'iyyun hamayyar ƙasar GCAP ya ce an kama mutanen tare da tsare su ranar Asabar da safe.

    GCAP dai ta shirya wani gangamin abin da ta kira nuna fushi a N'Djamena, babban birnin ƙasar cikin mako mai zuwa kafin a dakatar da ita.

    Kotun ƙolin Chadi ta ayyana ƙawancen a matsayin haramtacce.

    Kakakin jam'iyyar MPS mai mulki, Abdel-Nasser Garboa ya ce an yi kamen ne domin hana tayar da yamutsi.

    Ƙasar Chadi da ke yankin tsakiyar Afirka na daga cikin ƙasashen duniya da ke fama da talauci.

  9. An fara shari'ar Bashar al-Assad a Siriya

    An fara shari'ar hamɓararren shugaban Siriya, Bashar al-Assad da wasu daga cikin abokansa - da aka zarga da keta haƙƙin bil'adama.

    Mafi yawan, waɗanda ake yi wa shari'a ciki har da Mista Assad da ɗan'uwansa ba sa ƙasar.

    Mutumin da aka fi sani cikin waɗanda suka je kotun yau shi ne Atef Najif, tsohon babban jami'in tsaro da aka zarga da aikata ''laifukan ƙasa''.

    Sashen da yake kula da shi ne aka zarga da muzguna wa matasa a birnin Deraa da ke kudancin ƙasar a 2011.

    Rikincin ne ya janyo yaƙin basasar Siriya.

  10. Shugaban jami'an tsaron farin kaya na Amurka ya yaba wa ma'aikatansa

    Daraktan hukumar tsaron farin kaya na Amurka, Sean Curran, ya jinjina wa ma'aikatansa kan ƙoƙarin da suka yi na daƙile harin bindiga a wurin liyafar cin abincin dare.

    "Mun ga irin ƙwazon da ma'aikatanmu suka nuna wajen kare mutane. Ba aiki ne mai sauƙi ba, don haka mun yaba musu da wannan namijin ƙoƙarin da suka yi'', in ji shi.

    Mista Curran ya ƙara da cewa an yi sa'a ɗaya daga cikin jami'an da ak harba yana raye.

    Ya kuma gode wa Shugaba Trump saboda tuntuɓarsa da ya yi kan harin

  11. Sabon faɗa ya ɓarke a yankin Kidal na Mali

    An sake samun sabon faɗa a yankin Kidal da ke arewacin Mali, kwana guda bayan wasu hare-haren haɗin gwiwa da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi suka kai sassan ƙasar ciki har da Bamako, babban birnin ƙasar.

    A ranar Asabar ƙungiyoyin Tuareg da FLA sun yi iƙirarin iko da yankin na Kidal.

    Rundunar Sojin Mali, wadda ta jima tana samun goyon bayan sojojin hayar Rasha , ta ce yanzu haka tana fafatawa da ƙungiyoyin a yankin.

    Kakakin ƙungiyar FLA, Mohamed Ramdane, ya ce sun cimma yarjejeniyar bai wa sojojin hayar Rasha damar janyewa daga yankin.

    Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniy, Antonio Guterres ya buƙaci ƙasashen duniya su haɗa kai wajen tallafa wa Mali.

    Ƙasar Mali na ƙarƙashin mulkin soji tun shekara 2020.

  12. Araqchi ya gana da sarkin Oman a birnin Muscat

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi ya gana da sarkin Oman, Haitham bin Tariq a birnin Muscat.

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce jagororin biyu sun tattauna halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma yadda za a kawo ƙarshen yaƙin Iran da ma yankin baki ɗaya.

    Shafin kafar yaɗa labaran Tabnak ta wallafa cewa ''bayan barin Pakistan an tsara Araqchi zai tafi Rasha ne, domin tattauna yunƙurin kawo ƙarshen yaƙin.

    To amma sai ma'aikatar harkokin wajen Iran ta sauya tsarin bulaguron nasa, inda ya fara zuwa Oman sannan zai sake komawa Pakistan kafin ya kama hanyar zuwa Rasha.

    Kamfanin dillancin labarai na IRNA na Iran ya ce wasu daga cikin wakilan da Araqchi ya halarci Islamabad da su jiya sun sake komawa Tehran, domin samo umarni kan tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin, kuma za su sake komawa Islamabad, su haɗu da Araqchi domin ci gaba da tattaunawa.

  13. Jami'an FBI sun kai samame gidan mutumin da ake zargi da yin harbi a Washington

    Jami'an FBI sun kai samamen gidan mutumin da ake zargi da buɗe wuta a taron da Trump ya halarta a Washington.

    Jami'an tsaron sun kai samame gidan mutumin da ke Torrance a birnin California.

    An ga hotunan motocin jami'an tsaro na ficewa daga gidan mutumin bayan bincikarsa.

    Tuni dai jami'an tsaro suka kama mutumin, inda suka ce za su gurfanar da mutumin a gaban kotu.

  14. Shugabannin duniya na aike wa saƙonnin jaje ga Trump

    Shugabannin ƙasashen duniya daban-daban na ci gaba da aikewa da saƙonninsu na jaje kan harin bindiga da aka kai wa Trump a Washington.

    Firaministan Birtaniya Keir Starmer ya ce ya yi matuƙar "kaduwa da harin da aka kai ɗakin taron a birnin Washington cikin dare".

    "Dole ne a yi Allah wadai da duk wani hari kan dimokradiyya ko ƴancin faɗin albarkacin baki'', in ji shi.

    Haka ma firministan Kanada, Mark Carney ya ce "ya ji daɗi" da ya samu labarin cewa Trump da mai ɗakinsa da sauran manyan baƙi kowa ya kuɓuta.

    ''Ina jajanta wa waɗanda lamarin ya tayar musu da hankali a wannan taro".

    Shi ma takwaransa na Australia, Anthony Albanese, ya ce ya samu nutsuwa da ya ji waɗanda ke halartar taron sun kuɓuta.

    ''Muna jinjina wa jami'an farin kaya da sauran jami'an tsaro, bisa ƙoƙarin da suka yi,'' in ji shi.

    Kaja Kallas, babbar jami'ar diplomasiyyar Tarayyar Turai, ta bayyana goyon bayanta ga Shugaba Trump da mai ɗakinsa.

    ''Dimokraɗiyya ba ta maraba da tashin hankalin siyasa'', in ji ta.

    Ita ma shugabar riƙo ta ƙasar Venezuela, Delcy Rodríguez ta yi "Allah wadai da yunƙurin harin'', sannan ta aike da saƙon fatan alkairi ga waɗanda suka halarci taron.

    Can a Pakistan Firaministan ƙasar, Shehbaz Sharif, ya ce ya yi matuƙar ''kaɗuwa da labarin harin.

    ''Muna alhini tare da yin addu'a ga Shugaba Trump'', kamar yadda ya bayyana.

    Shi ma firaministan Indiya, Narendra Modi ya ce yana aikewa da saƙon jaje ga Shugaba Trump da mai ɗakinsa da mataimakinsa da sauran mahalarta taron.

    Shugaban Mexico Claudia Sheinbaum ya aike da nasa saƙon jajen.

  15. Kalli bidiyon yadda aka kuɓutar da Trump a lokacin harin

    Shugaba Trump na tsaka da tattaunawa da manyan baƙi lokacin da maharin ya buɗe wuta.

    Nan da nan jami'an tsrao suka yi nasarar kuɓutar da shi tare da fitar da shi daga ɗakin taron.

  16. Labarai da dumi-dumi, 'Wanda ake zargi ya ce jami'an Trump ya yi niyyar kai wa hari'

    Kafar yaɗa labarai ta CBS, ƙawar hulɗar BBC a Amurka, ta ce mutumin da ake zargi da kai harin Washington ya faɗa wa hukumomi cewa wasu jami'ai masu alaƙa da Trump ya yi niyyar kai wa hari.

    CBS ta ambato wasu majiyoyi biyu da ba ta ambaci sunansu ba na cewa an ji ƙarar harbin bindiga a ɗakin taron har sau biyar zuwa takwas.

    Tuni dai jami'an tsaro suka samu nasarar kuɓutar da Trump da mai ɗakinsa da sauran manyan baƙi daga wurin da lamarin ya faru.

  17. Hotunan yadda yansanda suka cika birnin Carlifonia domin bincikar gidan maharin

  18. Abin da muka sani kan mutumin da ake zargi da kai wa Trump hari

    Jami'an tsaron FBI sun fara fitar da bayanai kan mutumin da ake zargi kai da buɗe wuta a ɗakin taron da Shagaba Trump na Amurka ke halartar taro a birnin Washinton.

    Kafofin yaɗa labaran Amurka sun ce jami'an tsaron sun fitar da bayanai game da mutumin mai shekara 31.

    Ƴansandan sun bayyana sunansa da Cole Tomas Allen, wanda ke zaune a Torrance da ke birnin California a jihar Los Angeles.

    Kafar yaɗa labarai ta CBS, abokiyar hulɗar BBC ta ce Allen na aiki ne a matsayin mai koyarwa a Torrance bayan kammala karatunsa a cibiyar fasaha ta California.

    Ƴansanda sun kuma ce Allen ya sauka a otal ɗin da lamarin ya faru a matsayin baƙo, kuma yana ɗauke da makamai masu yawa, ciki har da bindigogi da wuƙaƙe.

    Tuni dai ƴansanda suka bazama gidansa da ke California domin bincikarsa.

  19. An fitar da Trump daga ɗakin taro bayan wani ɗanbindiga ya buɗe wuta

    Jami'an tsaron FBI sun samu nararar fitar da shugaban Amurka, Donald Trump daga wani taron cin abincin dare na ƙungiyar masu aiko da rahotonni daga fadar shugaban ƙasar da ake yi kowace shekara a birnin Washintong bayan da wani mutum ya buɗe wuta a wurin taron.

    Da yake jawabi daga fadarsa jim kaɗa bayan faruwar lamarin, Mista Trump ya ce wani mutum ne ɗauke da makamai ya yi yunƙurin kutsawa wurin da taron ke gudana.

    Lamarin ya faru ne lokacin da baƙi suka kammala cin abinci zagaye na farko, inda ka ji ƙarar harbin bindiga, a harabar ɗakin taron da ke Hotel ɗin Hilton a birnin.

    Jami'an tsaron FBI sun yi gaggawar kai wa Trump da mai ɗakinsa ɗauki inda suka yi nasarar fitar da su cikin kariya.

    Bayanai sun ce ɗaya daga cikin harsasan da aka harba ya samu wani jami'in tsaron da ke sanye da rigar kariya, wanda yanzu haka ke asibiti.

    Tuni dai aka kama mutumin da ake zargi da kai harin.

    Wannan ne dai karo na uku da ake yunƙurin kai wa Shugaba Trump harin bindiga a cikin shekaru ƙalilan.

  20. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.