Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 4/11/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 4/11/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Isiyaku Muhammed da Abdullahi Bello Diginza

  1. Rufewa

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye nan muka kawo ƙarshen labarai da rahotonnin da sai kuma gobe idan Allah ya kai mu, za mu sake dawowa domin ci gaba da kawo muku sabbanin labarai.

    Amma kafin nan Abdullahi Bello Diginza ke cewa mu kwana lafiya

  2. Ba addini ne kawai ke haifar da rikicin Najeriya ba - EU

    Ƙungiyar Tarayyar Turai ta EU ta ce ta fahimci cewa ba addini ne kaɗai ke haifar da rikice-rikice a Najeriya ba.

    Cikin wata sanarwa kakain ƙungiyar da Anouar El Anouni ya fitar ya ce ƙungiyar EU na jajanta wa imjutanen da rikicin ya rutsa da su kudanci da arewa maso gabashin ƙasar.

    Matakin na ƙungiyar EU na zuwa ne bayan da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya, kan abin da ya kira kisan Kiristoci a ƙasar.

    Sai dai EU ta ce akwai abubuwa da dama da ke haifar da rikicin ba addini kaɗai ba.

    “Mun fahimci cewa akwai abubuwa masu yawa da ke haifar da rikici a Najeriya, addini guda ne daga cikinsu, amma ba shi kaɗai ba,'' in ji Mista El Anouni.

  3. An rufe Jami'ar Umaru Yar'adua da ke Katsina sakamakon 'saɓani da gwamnati'

    An rufe jami'ar Umaru Musa Yar'adua da ke Katsina bayan rashin jituwa da ta taso tsakanin hukumomin jami'ar da gwamnatin jihar.

    Dr. Murtala Abdullahi Ƙwara, wanda shi ne shugaban ƙungiyoyin ma'aikata na jami'ar ya tabbatar wa BBC cewa an rufe jami'ar ne ranar Litinin bayan gazawar gwamnatin na cika wasu sharuɗɗa biyar da ma'aikatan jami'ar ta gindaya.

    Ƙwara ya ce yajin aikin ya haɗa da dukkanin ƙungiyoyin ma'aikatan jami'ar guda huɗu, waɗanda suka haɗa da ƙungiyar malaman jami'o'i ta ASUU da ta manyan ma'aikatan jami'a (SSANU), da ta matsakaitan ma'aikata da kuma ta masu aiki a ɗakunan bincike.

    Ya bayyana cewa "wannan ne karo na farko da aka taɓa kulle jami'ar baki ɗaya sanadiyyar rashin aiki, kasancewar kowace ƙungiya kuma kowane ma'aikaci ya ƙaurace wa aiki."

    Murtala ya ce buƙatun da suka gabatar wa gwamnati sun haɗa da daidaita albashin ma'aikatan jami'ar da na jami'o'in tarayya, da batun bai wa jami'a ƴancin ci gaba da tafiyar da shafin intanet na jami'ar, sai kuma batun fansho da kuma na amfani da asusun bai-ɗaya.

  4. DSS ta kori wasu jami'anta 115 daga aiki

    Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya, DSS ta ce ta kori wasu jami'anta 115 daga aiki, saboda abin da ta kira wasu sauye-sauye da hukumar ke yi.

    Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, a ranar Talata, DSS ta shawarci al'umma su kauce wa mu'amala da jami'an a matsayin wakilan hukumar.

    Hukumar ta kuma wallafa sunaye da hotonan jami'an 115 da ta ce ta koran a shafinta intanet.

    Bayanan mutanen da hukumar ta fitar sun nuna cewa an kori mutanen ne tsakanin shekarar 2024 zuwa 2025.

    Matakin na zuwa ne bayan da a watan Oktoban da ya gabata hukumar ta kama wasu tsoffin jami'anta biyu bisa zargin amfani sa sunan hukumar suna damfarar mutane.

  5. Gwamnatin Sudan ta ce sojojinta za su ci gaba da yaƙar RSF

    Ministan tsaron Sudan ya ce sojoji za su ci gaba da yaƙar mayaƙan RSF bayan sun kwace ikon birnin El-Fasher da ke arewacin Darfur.

    Bayan wani taro da majalisar tsaron ƙasar ta gudanar a yau, Hassan Kabroun ya ce sun yi nazari kan shawarar da Amurka ta gabatar na tsagaita wuta, amma bai fadi martaninsu ba.

    Ya gode wa gwamnatin Amurka kan ƙoƙarinta na samar da zaman lafiya.

    Ƙasashen huɗu da ke aikin shiga tsakani domin samar da zaman lafiya da su ka haɗa da Amurka da Masar da Saudiyya da Haddadiyar Daular Larabawa sun shafe watannin suna tattaunawar diflomasiyya domin kawo ƙarshen yaƙin da aka shafe fiye da shekara biyu ana gwabzawa.

  6. Ecowas ta yi watsi da iƙirarin Trump na kisan Kiristoci a Najeriya

    Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, Ecowas ta yi watsi da abin da ta kira iƙirarin ƙarya mai cike da hatsari da shugaban Amurka ya yi cewa ƙungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi na far wa kiristoci tare da kashe su a Najeriya.

    Matakin na zuwa ne bayan da Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya, kana bin da ya bayyana da kisan kiyashin da ake yi wa Kiristoci a ƙasar.

    Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ranar Talata ta ce irin wannan na Shugaba Trump ka iya ta'azzara matsalar tsaro tare da haifar da matsalar zamantakewa a yankin da dama ke fama da matsalar masu tsattsauran ra'ayi.

    Ecowas ta jaddada cewa hare-haren masu tsattsauran ra'ayi a yankin Afirka ta Yamma na shafar mutanen da ba su ji ba su gani ba, ba tare da la'akari da addini ko ƙabila ko jinsi ba.

    Kan haka ne kungiyar ta buƙaci ƙasashen duniya su tallafa wa kowace ƙasa wajen yaƙi da ta'addanci da ke shafar kowa da kowa.

  7. Trump ya ce ba zai ci gaba da ba da tallafin abinci ga talakawan Amurka ba

    Shugaba Trump na Amurka ya ce gwamnatinsa ba za ta maido da tallafin abinci take bai wa talakawan Amurkawa ba, har sai an janye dakatar da ayyukan gwamnati da ake yi a ƙasar.

    Hakan na zuwa ne duk kuwa da umarnin kotu da ta buƙaci gwamnati ta ci gaba da biyan kuɗin tallafin.

    Mista Trump ya kuma buƙaci jam'iyyar Demokrats mai hamayya da kitsa abin da ya kira ''manaƙisar siyasa'' da ta hana majalisa amincewa da kasafin kuɗi.

    A ranar Litinin gwamnatin Trump ta ce za a biya wani ɓangare na kuɗin tallafin abincin daga asusun ayyukan gaggawa.

    Yanzu haka an kwashe kwana 35 ana gudanar da matakin dakatar da ayyukan gwamnati a Amurka, kuma na matakin na dab da zama mafi jimawa da aka taɓa yi a tarihin Amurka.

    Matakin ya haifar da asara ga miliyoyin Amurkawa masu ƙaramin ƙarfi.

  8. Sojojin Najeriya sun kashe ƴan Boko Haram shida yayin daƙile harin ƙungiyar kan sansanin soji

    Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kisan mayaƙan Boko Haram shida a lokacin da suka daƙile wani hari da mayakan ƙungiyar suka yi yunƙurin kai wa wani sansanin soji a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

    Cikin wata sanarwa da Laftanar Kalan Sani Uba, jami'in hulda da jama'a na rundunar haɗin kai mai yaƙi da Boko Haram ya fitar, ya ce mayaƙan ƙungiyar sun shirya kai hari da asubahin yau kan sansanin sojin da ke Kangar a yankin Mallam Fatori.

    ''Da misalin ƙarfe 4:30 na asubahin yau Talata, 4 ga watan Nuwamba ne mayaƙan Boko Haram da na ISWAP, suka kitsa wani hari ta hanyar amfani da jirage marasa matuƙa da bindigogi kan sansanin soji, sai kuma nan take dakarunmu suka gaggauta mayar da martani tare da daƙile harin'', in ji sanarwar.

    Sanarwar ta ci gaba da cewa, duk da jiragen marasa matuƙa da maharan suka yi amfani da su, dakarun Najeriyar ta hanyar taimakon sojojin sama sun samau nasarar fatattakar mayaƙan.

    Bayan kammala fafatawar, bayanan da sojojin suka tattara sun tabbatar musu da mutuwar mayaƙan ƙungiyar shida da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 biyar da manyan boma-bomai biyar da jirage marasa matuƙa huɗu masu ɗauke da boma-bomai, da gurneti 36 da nau'ikan alburusai masu yawa.

  9. Kullen Allah ta yi kira ga ƴansiyasar Arewa su fifita tsaro da hadin kan yankin

    Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Kullen Allah ta yi kira ga ƴansiyasar arewacin Najeriya su gaggauta mayar da hankalinsu kan samar da tsaro da wanzar da zaman lafiya da haɗin kan yankin.

    Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Khalil Moh'd Bello ya fitar ya ce Ƙungiyar ta damu da yadda al'amuran tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a yankin arewacin Najeriya.

    ''Yankin na fuskantar mummunan kashe-kashe na mutanen da ba su ji, ba su gani ba, da asarar dukiyoyi na biliyoyin naira, da sace miliyoyin shanu da raba milyoyin mutane daga gidajensu'', in ji sanarwar.

    Ƙungiyar ta ce abin takaici ne yadda yankin arewacin Najeriya da aka sani a tarihance da zaman lafiya a yanzu ta koma tamkar filin daga.

    ''Yayin da wasu yankunan suka mayar da hankali wajen ci gaba yin rajistar zaɓe, amma miliyoyin ƴan Arewacin Najeriya na ci gama da zama a sansanonin ƴangudun hijira, wani abu da zai sa katin nasu ma ya zama maras amfani'', in ji shugaban ƙungiyar ta Kullen Allah.

    Khalil Moh'd Bello ya kuma zargi ƴansiyasar arewa da mayar da hankali wajen dabarun siyasa, fiye lalubo hanyoyin magance matsalar tsaro a arewaci da ma Najeriya baki ɗaya.

  10. Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da gargaɗin Shugaba Trump kan ƙasar

    Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar ya yi watsi da gargaɗin Shugaba Trump na ɗaukar matakin soji kan Najeriya.

    Yayin da yake jawabi a taron manema labarai da ya gudanar a birnin Berlin tare da takwaransa na Jamus, Mista Tuggar ya ce Najeriya na bayar da ƴancin addini tare da aiki bisa doron doka.

    ''Kundin tsarin mulkin Najeriya da dokokin ƙasar sun haramta cin zarafin addini tare da bayar da damar ƴancin gudanar da addini'', in ji shi.

    ''Babu yadda za a yi gwamnatin Najeriya ta goyi bayan ta kowane fanni na yadda za a ci zarafin mabiya wani addini'', in ji Tuggar.

    Ministan harkokin wajen na Najeriya gwamnatin ƙasar ba za ta yarda a mayar da ƙasar tamkar Sudan ba.

    ''Abin da muke so duniya ta fahimta shi ne ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin, Najeriya na da yawan al'umma fiye da miliyan 230, ƙasar da ta fi kowace yawan jama'a da ƙarfin dimokraɗiyya a Afirka'', a cewarsa.

    Ya ƙara da cewa an ga yadda ƙasar Sudan ta koma sakamakon rikici mai alaƙa da addini da ƙabilanci da kuma ɓangaranci.

    ''Don haka babu wanda ya kamata ya magance matsalolin Afirka sai mu ƴan Afirka, kamar Najeriya - wadda ke a matsayin mamba a kwamitin tsaro na ƙungiyar Tarayar Afirka.

  11. Kotu ta amince PDP ta gudanar da babban taronta a Ibadan

    Wata babbar kotu da ke zamanta a jihar Oyo ta Ibadan, ƙarƙashin jagorancin mai shari’a A. L. Akintola, ta amince wa jam’iyyar PDP ta gudanar da babban taronta da aka tsara yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025 a filin wasa na Lekan Salami Stadium, Adamasingba, Ibadan.

    A hukuncin, kotun ta umarci jami’an PDP da wakilanta da su guji duk wani yunƙuri na dakile ko karya jadawalin da aka riga aka fitar dangane da babban taron.

    Jam’iyyar ta sanar da hakan ne a shafin sada zumuntarta na Facebook.

    Mai Shari’a Akintola ya ƙara da bayar da umurni ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta tura jami’anta domin sa ido da lura da dukkan abin da ke gudana a taron.

    Wannan mataki, a cewarsa, "Zai tabbatar da cewa an bi doka da ka’idojin gudanar da zaɓe tare da inganta gaskiya da bayyana gaskiyar abin da ke faruwa a lokacin taron."

    Kotun kuma ta ba da umurni ga Umaru Ahmadu Fintiri, wanda shi ne shugaban kwamitin shirya taron, da ya ci gaba da dukkan shiri da ya shafi gudanar da babban taron.

    Wannan hukuncin ya cire duk wasu matsalolin doka da ke ƙoƙarin jinkirta gudanar ta taron.

    Jam'iyyar ta ce wannan mataki babbar nasara ce ga jam’iyya, domin yanzu kwamitin shirya taron NCOC na da damar kammala shirye-shiryen karɓar sama da wakilai 3,000 da ake sa ran halartarsu daga jihohi daban-daban.

  12. Kotu ta bai wa Nnamdi Kanu dama ta ƙarshe ya kare kansa

    Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ƙarƙashin jagorancin mai shari’a James Omotosho, ta bai wa shugaban ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu dama ta ƙarshe domin ya kare kansa.

    Kotun ta ba shi har zuwa ranar 5 ga watan Nuwamba domin ya kare kansa kan zargin ta’addanci da gwamnati take tuhumarsa da shi, ko kuma ya rasa damar yin hakan gaba ɗaya.

    Wannan umarni ya biyo bayan gazawarsa da ya yi ta kare kansa a karo na huɗu.

    A zaman da aka yi a ranar Talata, James Omotosho ya fara da gabatar da taƙaitaccen tarihin yadda wannan shari’a take tafiya tun shekarar 2015 zuwa yau.

    Ya ce ya yi hakan ne domin kowa a zauren kotu ya fahimci yanda shari’ar ta samo asali da kuma matakin da ta kai yanzu.

    Bayan haka, alƙalin ya kira Nnamdi Kanu domin ya fara kare kanshi. Sai dai Kanu ya tashi ya tsaya kan bakansa cewa babu wata sahihiyar tuhuma ta doka da ake iya jingina masa a karkashin dokokin Najeriya.

    Ya ce ba za a iya gurfanar da shi a kan wata doka da ba ta a rubuce a littafin dokokin Najeriya ba.

    Kanu ya nemi kotu ta yi watsi da shari’ar gaba ɗaya, yana mai cewa ba zai koma wurin da ake tsare shi ba.

  13. China ta soki yunƙurin Amurka na yin katsalandan a harkokin Najeriya

    Ƙasar China ta soki abin da ta kira yunƙurin Shugaban Amurka Donald Trump na yin katsalandan kan harkokin da ta ce na cikin gida ne da suka shafi Najeriya, inda ta bayyana goyon bayanta ga mulkin shugaban ƙasar, Bola Tinubu.

    Kakakin ma'aikatar harkokin wajen China, Mao Ning ce ta bayyana haka a matsayin martani kan barazanar Shugaban Amurka Donald Trump ta tura sojoji zuwa Najeriya domin yaƙi da ta'addanci, bisa zargin ana yi wa kiristoci kisan kiyashi.

    A taron manema labarai da ta yi a ranar Talata, jaridar Daily Trust ta ruwaito Ning na cewa, "Najeriya ƙasa ce da muke da alaƙa mai kyau da ita, don haka China na bayyana goyon bayanta ga gwamnatin Najeriya da mutanenta domin gudanar da mulki daidai da abin da take ganin zai fi dacewa da ƴanƙasarta."

    Ta ce China na Allah-wadai "da duk wata barazana ko yunƙurin amfani da addini ko zargin tauye haƙƙin ɗan'adam domin yin kutse ko katsalandan a harkokin wata ƙasar da ma barazanar ƙaƙaba mata takunkumi da ƙarfi."

  14. Mataimakin tsohon shugaban Amurka George Bush ya rasu

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasar Amurka, Dick Cheney ya rasu yana da shekara 84 a duniya.

    A wata sanarwa a iyalansa suka fitar, sun ce mamacin ra yasu ne a sakamakon cututtuka masu alaƙa da zuciya da sarƙewar numfashi.

    Cheney mai shekara 84 ne mataimakin shugaban ƙasar na 46, kuma ya yi mulki ne shekara takwas a jere a zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasar, George W. Bush.

    Ana tunanin dai shi ne kan gaba wajen "yaƙi da ta'addanci' da Amurka take iƙirari, ciki har da yaƙi a Afghanistan da Iraq.

    An taɓa dakatar da shi daga jam'iyyarsu ta Republican saboda sukar da ya taɓa game da salon mulkin Donald Trump.

  15. Shugaban Majalisar Dinkin Duniya ya nemi a dakatar da rikicin Sudan

    Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya yi kira da a dakatar da rikici da tashin hankali da ake fama da shi a Sudan nan take, yana gargadin cewa rikicin jin kai na ƙara ta’azzara a ƙasar cikin sauri.

    Ya bayyana cewa lamarin na ƙara ƙamari inda ya yi kira ga ɓangarorin da ke rikici da su koma teburin sulhu.

    Wani majiyar gwamnatin Sudan ya shaida wa Kamfanin dillancin labarai ta Faransa, AFP, cewa hukumomin ƙasar na la’akari da wani shawarwari daga Amurka na ƙulla tsagaitaccen wuta.

    A Washington, ƙungiyar sulhu ta “Quad” tana ci gaba da matsa lamba domin samun tsagaita wuta da kuma tsara hanyar kawo ƙarshen rikicin a Sudan.

  16. Peru ta yanke alaƙar diflomasiyya da Mexico

    Kasar Peru ta ce ya yanke huldar diflomasiyya da kasar Mexicon saboda ba tsohuwar shugabar kasar mafaka.

    An bayyana cewa Betssy Chavez ta samu mafaka ne a ofishin jekadancin Mexico a Lima Tana fuskantar tuhuma kan zargin juyin mulki shekara uku da suka gabata, lokacin da tsohon shugaban kasar Pedro Castillo ya yi kokarin rusa majalisa.

    Gwamnatin Mexico dai ba ta mayar da martani ba kan zargin na Peru

  17. Harin Ukraine ya illata cibiyar man fetur a Rasha

    Hukumomi a Rasha sun ce jirage marar matuka na Ukraine sun kai hari wata cibiyar man fetur ta kasar.

    Sun ce cibiyar ta Sterlitamak na da tazarar nisan kilomita sama da dubu daya da kan iyakar Ukraine.

    hotunan Bidiyo sun nuna yadda wuta da hayaki suka turnike sama bayan harin na kasar Ukraine a cibiyar ta fetur.

    Babu dai rahoton rasa rai ko jikkata da aka bayar har zuwa yanzu.

  18. Amurka ta tura dakaru gaɓar Venezuela don daƙile masu safarar miyagun ƙwayoyi

    Jamhuriyar Dominican ta sanar da cewa, an dage wani taron yankin kasashen Caribbean, saboda takun sakar Amurka da wasu kasashen yankin.

    Kasancewar dakarun Amurka a yankin Caribbean ya harzuka wasu gwamnatocin kasashen yankin.

    Amurka ta ce ta tura dakaru gabar tekun Venezeula don kakkabe masu safarar miyagun kwayoyi.

    Amurka ta kashe fiye da 60 a hare-haren da ta kai Jamhuriyar Dominican, wadda ya kamata ta karbi bakuncin taron a watan Disamba, ta ce barnar da guguwar Melissa ta haddasa, wani karin dalili ne da ya tilasta dage taron zuwa shekara mai zuwa.

  19. Ƴanbindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 10 a Kebbi

    Rahotanni daga jihar na nuna cewa ƴanbindiga sun yi garkuwa da aƙalla mutum 10 a wasu hare-hare da suka kai garuruwan Tungar Wazga da Unguwar Chiroma a ƙaramar hukumar Danko-Wasagu da ke jihar Kebbi a arewa maso yammacin Najeriya.

    A wata sanarwa da rundunar ƴansandan jihar ta fitar, kakakin rundunar CSP Nafiu Abubakar ya ce jami'ansu sun bibiyi ƴanbindigar, inda suka haɗu da su a ƙauyen Marina da ke bakin iyakar jihar da jihar Zamfara da suke maƙwabtaka.

    "A lokacin da ƴansandan suke musayar wuta da ƴanbindiga ne suka saki mutum shida daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da su, sannan suka tsere da raunuka zuwa jihar Kebbi," in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

  20. Jagoran mulkin sojin Guinea zai tsaya takarar shugaban ƙasar

    Kwamandan soji da ke jagorantar Guinea tun kwace mulki a wani juyin mulki shekaru hudu da suka gabata, ya ce zai tsaya takarar shugaban kasa.

    Kanal Mamadi Doumbouya ya tafi kotun kolin kasar a jiya Litinin sanye da bakin gilashi da rakiyar sojoji inda ya gabatar da bukatarsa ta tsayawa takara.

    An haramta wa manyan jam'iyyun hamayya na kasar shiga zaben na watan Disamba.

    ‘Yan kasar Guinea sun kadu a watan da ya gabata da sanarwar cewa ‘yantakarar shugaban kasa dole sai ya biya kudi har kusan dala Amurka dubu dari kafin tsayawa takarar shugaban kasa