Iran ta yi barazanar ta faɗaɗa yaƙin da take yi zuwa maƙwabtan ƙasashe, inda ta yi kira ga Hadaddiyar Daular Larabawa ta fara kwashe ƴan ƙasarta daga yankunan da ke kusa da tashoshin jiragen ruwa a Abu Dhabi da Dubai da kuma Fujairah.
Yayin da rikicin ya shiga mako na uku, Iran ta ci gaba da harba muggan makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan kayayyaki da cibiyoyi na ƙasashe makwabtanta da kuma Isra'ila.
Duk da ruwan bama-bamai ba ƙaƙƙautawa tsawon mako biyu na sojojin Amurka da suka fi ƙarfi ainun, Iran ta ci gaba da ƙaddamar da hare-hare.
Wani mai bayar da shawara na diflomasiyya ga shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa, ya mayar da martani da cewa ƙasarsa tana da ƴancin kare kanta, amma ta zaɓi ta ci gaba da amfani da hankali da tunani.
An ji fashewar bama-bamai a Manama, babban birnin ƙasar Bahrain.