Shugaban Faransa ya yi kiran a gaggauta tsagaita wuta a Lebanon

Asalin hoton, Reuters
Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya yu kiran a gaggauta dakatar da buɗe wuta a Lebanon.
Ya yi kalaman ne da yawun kungiyar kasashen da ke amfani da harshen Faransanci, wanda Lebanon mamba ce a cikinsu.
Mr Macron ya kara da cewa ya yi nadamar matakin da firaiministan Isra'ila Benyamin Netanyahu ya ɗauka na kai samame ta ƙasa.
Dubban magoya bayan Falasdinawa ne sukai maci a biranen Faransa da wasu kassashen duniya, tare da kiran a dakatar da buɗe wuta a Gaza, da kawo ƙarshen tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya.















