Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 19/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis19 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Amurka ta jaddada yunƙurin ficewa daga hukumar makamashi ta duniya

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakataren Makamashi na Amurka, Chris Wright, ya sake sabunta barazanar ficewar kasarsa daga Hukumar kula da Makamashi ta Duniya.

    Mista Wright ya shaidawa taron ministocin kasashen kungiyar a birnin Paris cewa, kamata ya yi hukumar ta koma kan aikinta na tabbatar da wadatuwar makamashi.

    Ya kara da cewa kamata ya yi ta yi watsi da abin da ya kira, mafarkin da take yi cewa, za a iya cimma lokacin da ba a fitar hayakin mai gurbata muhalli, a bisa yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris a shekarar 2015.

    Amma Mista Wright ya nuna cewa Washington za ta yi jinkirin ficewa saboda hakan na iya bai wa China damar mamaye hukumar makamashi ta duniya.

  2. Birtaniya ta soki matakin Iran na yanke wa ƴan ƙasarta hukunci bisa zargin leƙen asiri

    Birtaniya

    Asalin hoton, Reuters

    Sakatariyar harkokin wajen Birtaniya Yvette Cooper ta ce matakin da Iran ta dauka na yanke wa, wasu ma'aurata 'yan Birtaniya hukuncin daurin shekaru goma a gidan yari, bisa samunsu da laifin leken asiri abu ne mai ban takaici wanda babu hujjar yinsa.

    Craig da Lindsay Foreman, wadanda suka musanta zargin, an kama su ne wata 13 da suka gabata a lokacin da suke tafiya cikin kasar ta Iran a babura.

    An tsare su a gidan yarin Evin na Tehran, inda a wasu lokutta akan killace su daga sauran fursunoni. Iyalan su sun ce, duk da cewa an gurfanar da su a gaban kotun ba a bayar da wata shaida ba, kuma ba a ba su da damar kare kansu ba.

    Shi ma ɗansu ya ce ya damu ƙwarai da halin da suke ciki.

  3. Lakurawa sun 'kashe aƙalla mutum 30' a Kebbi

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu 'yanbindiga da ake zargin 'yan ƙungiyar Lakurawa ne sun kashe mutum 30 tare da lalata ƙauyuka bakwai a hare-haren da suka kai a yankin arewa maso yammacin Jihar Kebbi, kamar yadda ’yan sanda suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Alhamis.

    Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Bashir Usman, ya ce ’yan ƙungiyar sun kai farmakin ne a yankin Bui na ƙaramar hukumar Arewa da misalin ƙarfe 1:15 na rana a ranar Laraba.

    Wani rahoton da AFP ya gani ya nuna cewa maharan sun kashe sama da mutum 30.

    Usman ya ce adadin waɗanda suka mutu yana dayawa idan aka haɗa da mutanen da suka fito daga ƙauyukan Mamunu da Awasaka da Tungan Tsoho da Makangara da Kanzo da Gorun Naidal da Dan Mai Ago domin kare kansu daga harin.

    Wani mazaunin ƙauyen Kanzo ya ce sun ji ƙarar bindiga suna cikin gidajensu, lamarin da ya sa mutane suka riƙa gudu domin neman mafaka, inda harsasai suka samu wasu daga cikinsu.

    ’Yan sanda sun ƙara da cewa maharan sun kuma kwashe shanu a yayin farmakin.

    Bayan faruwar lamarin, an tura jami’an tsaro da sojoji tare da ’yan sa-kai zuwa yankin domin daƙile harin da kuma dawo da zaman lafiya.

  4. Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafi

    ...

    Asalin hoton, Abba Kabir/Facebook

    Gwamnatin Jihar Kano ta fara aikin tantancewa tare da ɗaukar bayanan ’yan kasuwar da gobarar kasuwar Singer ta shafa domin tsara yadda za a bi matakan ba su tallafi.

    Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta tashi ne da yammacin ranar Asabar inda ta ƙone shaguna da tebura fiye da 1,500, lamarin da ya jawo asarar dukiya mai yawa ga ’yan kasuwa.

    Tuni gwamnatin tarayya ta bai wa waɗanda abin ya shafa tallafin Naira biliyan biyar, baya ga gudummawar da wasu hukumomi da daidaikun jama’a suka bayar.

    Hukumomin jihar sun sanar da fara aikin tantance ’yan kasuwar ta hannun Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha wato SEMA.

    Hukumar ta bayyana cewa duk lokacin da aka samu iftila’i irin wannan, sukan je su ƙididdige tare da ɗaukar bayanan waɗanda abin ya shafa domin sanin yadda za a taimaka musu.

    Shugaban hukumar, Isyaku Abdullahi Kubarachi, ya ce suna gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA reshen jihar Kano.

    SEMA ta ce aikin zai ɗauki kwanaki biyar ana yi, bayan haka za su rubuta rahoto su miƙa wa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, wanda ake sa ran zai yi nazari tare da kafa kwamitin da zai kula da raba tallafin ga waɗanda suka cancanta.

  5. Somaliland ta soki gargaɗin shugaban Turkiyya kan amincewa da ita

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar harkokin wajen Somaliland ta yi allawadai da gargaɗin shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, game da yuwuwar amincewa da yankin a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta, tana mai kiran matakin a matsayin “tsoma baki da ba za a amince da shi ba” da nufin hana hulɗarta da ƙasashen yankin.

    Wannan na ƙunshe ne a rahoton gidan talabijin na gwamnati, Somaliland National TV.

    Kafofin watsa labarai na Somaliya sun ruwaito cewa yayin ziyararsa a Addis Ababa ranar 17 ga Fabrairu, Erdoğan ya shaida wa firaministan Habasha, Abiy Ahmed, cewa ƙasarsa ba za ta amfana ba idan ta bi sahun Isra'ila wajen amincewa da yankin a matsayin kasa mai cin gashi kanta.

    Ma’aikatar ta ce dole ne manufofin harkokin wajen ƙasashen yankin Kahon Afirka su kasance a hannun gwamnatocin yankin da al’ummominsu, tare da kira ga Turkiyya da ta guji ɗaukar matsayin da zai iya ƙara rura wutar rikici a yankin.

    Haka kuma ta buƙaci Ankara da ta mutunta ƙa’idojin girmama juna, da kuma ikon kowace ƙasa na yanke shawara da kanta.

    Yawancin ƙasashen yankin Kahon Afirka sun nuna adawa da matakin Isra’ila na amincewa da yankin, sai dai Habasha ba ta bayyana matsayinta a hukumance ba har zuwa yanzu.

  6. Hisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a Kano

    ..

    Asalin hoton, MUJALLAR HIZBA/FACEBOOK

    Hukumar Hisbah a jihar Kano ta ce jami'anta sun kama wasu mutum tara Musulmai a jiya Laraba a take ranar farko ta azumin watan Ramadan saboda an gan su suna cin abinci da tsakar rana.

    Jihar Kano na da yawan Musulmai, inda tsarin shari’ar Musulunci ke aiki tare da dokokin ƙasa na yau da kullum.

    A kowane Ramadan, Hisbah na bincika wuraren sayar da abinci da kasuwanni domin tabbatar da cewa Musulmai na bin dokokin azumi.

    A wasu wurare, wurarern cin abinci na ci gaba da aiki musamman a yankunan da Kiristoci da dama ke zaune.

    Ga Musulmai masu azumi, cin abinci daga fitowar rana zuwa faduwar rana haramun ne.

    Yin azumi na daga cikin ginshikan Musulunci guda biyar da ke kafa yadda Musulmai ke gudanar da rayuwarsu.

    Mujahid Aminudeen, mataimakin kwamandan Hisbah, ya shaida wa BBC cewa daga cikin wadanda aka kama akwai mata biyu da maza bakwai.

    Ya ce: "Mun kama su kuma suna tare da mu inda za mu koya musu muhimmancin azumi, yadda za su yi salla da karanta Al-Qur’ani, kuma su zama Musulmai nagari."

    Ba a bayyana lokacin da Hisbah za ta saki wadanda aka kama ba.

  7. Majalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara

    .....

    Asalin hoton, RSGH Media

    Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakiyarsa, Ngozi Odu daga mukamansu, bayan tsoma bakin Shugaban Kasa, Bola Tinubu.

    Majalisar ta ɗauki matakin dakatar da shirin tsige gwamnan ne a ranar Alhamis, yayin zaman da aka ci gaba da gudanarwa a birnin Port Harcourt, babban birnin jihar.

    Tun daga farkon wannan shekara ne wasu ‘yan majalisar suka fara magana kan yiwuwar tsige gwamnan saboda zarge-zarge kan yadda wasu ayyukan gwamnati ke tafiya da kuma rikice-rikicen siyasa a jihar.

  8. Bill Gates ya fice daga taron AI a Indiya saboda alaƙarsa da Jeffrey Epstein

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban kamfanin Microsoft, Bill Gates, ya fice daga wani babban taron ƙirkirarriyar basira ta AI a Indiya sakamakon bayanan da aka bankaɗo da ke alaƙanta shi da Jeffrey Epstein, mutumin da ya mutu a gidan yari kan laifin cin zarafi ta hanyar lalata.

    Cikin wata sanarwa da aka fitar a shafin X, gidauniyar Bill Gates ta bayyana cewa ya ɗauki matakin ƙauracewa taron ne domin tabbatar da cewa an mayar da hankali kan muhimman batutuwan babban taron da za a gudanar a yau Alhamis kan ƙirkirarriyar basira.

    Tun da farko an tsara cewa Bill Gates zai gabatar da jawabi a wajen taron, inda zai yi tsokaci kan alfanun AI da kuma tasirin da barazanar da ke tattare da ƙirkirarriyar basira.

    Gidauniyar ta kuma bayyana cewa ficewar Gates ba ta nufin wata amfani ko rashin amincewa da taron ba, sai dai matakin ya zo ne domin kare darajar taron da tabbatar da cewa mahalarta za su mayar da hankali kan muhimman batutuwa kawai.

    Masu sharhi sun nuna cewa wannan lamari zai iya jawo cece-kuce a kafafen yada labarai, amma a hukumance an tabbatar da cewa babban burin Gates shi ne ganin taron ya mayar da hankali kan cigaban fasaha da tattaunawa mai amfani.

  9. Masu haƙar ma’adinai 40 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

    ...

    Aƙalla masu haƙar ma’adinai 40 ne suka mutu sakamakon shakar iskar gas ta sinadarin carbon wace take guba mai ƙarfi yayin da suke hakar ma'adinai a Jihar Plateau, kamar yadda wasu suka shaida wa BBC.

    Ana hasashen wannan mummunan lamari ya faru ne kafin fitowar rana a wani wuri a wajen garin Wase, wanda kamfanin ma’adinai na Solid Unity Nigeria Ltd, ke gudanarwa.

    Ana ganin cewa guba mai ƙarfi ta sinadarin ta taru a cikin ramin ƙasa da iska ba ya samun shiga sosai, wanda ya sa ma’aikatan suka fadi a kasa kafin su kammala aikin dare.

    Wadanda suka je aiki da safe ne suka tarar da gawawwakin.

    Jami’an tsaro sun rufe wurin hakar ma’adinan, wanda ke kimanin kilomita 200 daga gabas zuwa kudu maso gabas na Jos, babban birnin Jihar Plateau, yayin da ake gudanar da bincike domin gano musabbabin zubar sinadarin.

    Hukumomin jihar har yanzu ba su kai ziyara wurin ba, kuma rahotanni sun nuna cewa an samu cikkas wajen kai taimakon gaggawa saboda rashin tsaro a yankin.

    Safiyanu Haruna, ɗaya daga cikin ma’aikatan hakar ma'adinai da suka tarar da gawawwakin ya shaida wa BBC cewa wasu daga cikin ma’aikatan da ke cikin rami sun tsira kuma an kai su asibiti a Wase don samun kulawa.

  10. Birtaniya za ta gabatar da ƙudurin bincike kan zargin aikata manyan laifuka a Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Birtaniya za ta yi kiran da a tabbatar da gaskiyar munanan laifukan da aka aikata a Sudan a wajen taron kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

    Kasar zata yi amfani da damarta wajen ganin an gano irin barnar data biyi bayan yakin basasar Sudan din.

    Ana kyautata tsammanin Sakatariyar harkokin wajen Birtaniya, Yvette Cooper zata tabo batun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma irin cin zarafi ta hanyar lalatar da aikata a yakin Sudan.

    Wannan shi ne matakin mafi kusa da zai sa Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana cewa dakarun RSF sun aikata kisan kiyashi a yankin Darfur a yakin da ake a Sudan

    Yayin da ake zargin bangarorin da ya ke yaki da juna a Sudan da aikata irin wadannan laifuka, Majalisar Dinkin Duniya ta ce bangaren mayakan RSF sun fi aikata ta'asa a yayin yakin.

  11. Majalisar Peru ta naɗa shugaban riƙon-ƙwarya bayan Jose Heri ya yi murabus

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokokin Peru ta zaɓi sabon shugaban riƙon ƙwarya bayan an tilasta wa tsohon shugaban ƙasar, Jose Heri, ya sauka daga mukaminsa sakamakon wasu badakala da aka bayyana.

    Jose Balcazar ne zai riƙa shugabancin ƙasar na ɗan wani lokaci, kuma shi ne tsohon alkali da ya riƙe mukamin shugaban ƙasa karo na takwas cikin shekaru goma.

    An bayyana cewa Balcazar zai ja ragamar ƙasar ne har zuwa ƙarshen watan Yuli, lokacin da za a gudanar da sabon zaɓe don shugabanci mai ɗorewa.

    Shugaba Heri ya yi sauka ne daga mukaminsa saboda wasu zarge-zarge da suka haɗa da ganawa da wani hamshakin ɗan kasuwa daga ƙasar China.

    Bugu da ƙari, an zarge shi da cewa ya na nada mata mukamai da dama a gwamnatinsa, sannan yana gayyatar su zuwa fadar shugaban ƙasa a cikin dare, abin da ya haifar da tirjiya daga 'yan majalisa da jama’a.

  12. An yanke wa tsohon shugaban Koriya ta Kudu hukuncin ɗaurin rai da rai

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata kotu a Koriya ta Kudu ta yanke wa tsohon shugaban ƙasa, Yoon Suk Yeol, hukuncin ɗaurin rai da rai kan tuhume-tuhumen da ake yi masa na yunkurin da ya yi na ƙarfafa mulkin soji a watan Disamba 2024.

    Wannan hukunci na zuwa ne bayan shari’a mai tsawo da ta ɗauki hankulan 'yan ƙasar da ma na ƙasashen duniya.

    Yunƙurin tsohon shugaban ƙasar ya jawo zanga-zanga mai ƙarfi a kan titunan ƙasar, inda dubban mutane suka fito domin nuna adawa da matakin da ya ɗauka.

    Daga bisani, majalisar dokokin ƙasar ta tsige Yoon daga muƙaminsa, tare da tuhumarsa da aikata laifuka da dama da suka haɗa da cin hanci da yunƙurin tauye haƙƙin dimokuradiyya da dai sauransu.

    Har yanzu dai Yoon ya dage cewa ya ɗauki matakin ne domin kare 'yancin ƙasar daga abin da yake ganin barazana ce ga tsaro da zaman lafiya, kuma ya ƙara jaddada cewa ba shi da wata manufa ta cin zarafin jama’a.

    Duk da haka, kotu ta ga cewa yunƙurin nasa ya saba wa dokokin ƙasa, abin da ya sa aka yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

    Masu lura da al’amuran siyasa a yankin Asiya sun bayyana cewa wannan lamari zai iya shafar tsaro da zaman lafiya a ƙasar Koriya ta Kudu da ma yankin baki ɗaya.

  13. Amurka na matsa wa Iran lamba kan amincewa da yarjejeniyar nukiliya

    ...

    Asalin hoton, Reuters/Epa

    Fadar White House ta gargaɗi gwamnatin Iran cewa zai zama abin hikima gare ta ta amince da ƙulla yarjejeniya da gwamnatin Amurka kan batun shirin nukiliyar ƙasar, yayin da ake ƙara tura rundunar sojojin ruwa da wasu manyan makamai zuwa yankin Gabas ta Tsakiya.

    Kakakin fadar White House, Karoline Leavitt, ce ta bayyana hakan yayin da ake ci gaba da zama tsakanin Amurka da Iran a birnin Geneva don tattaunawar da ke da nufin dakile saɓani kan shirin nukiliyar Tehran.

    Leavitt ta ce shugaban Amurka, Donald Trump, na fatan ganin an sami mafita ta diflomasiyya kan batun.

    Wannan ya zo ne a daidai lokacin da mahalarta tattaunawar suka nuna cewa an sami ci gaba kan wasu manyan ƙa’idojin da za su iya zama hanyar faɗaɗa yarjejeniya idan har an sami lokacin rubuta takardun yarjejeniya.

    A ƙarƙashin wannan yanayi, Amurka ta ƙara ƙarfafa matsayinta na soji a yankin, inda ta tura manyan jiragen yaƙi da sauran makamai masu yawa don nuna tanadin shirin kare muradunta idan tattaunawa ta gaza cimmawa.

    Rahotanni sun nuna cewa Iran na fuskantar matsin lamba daga ɓangaren duniya yayin da take ƙoƙarin kare shirinta na nukiliya daga abin da take ganin takunkumi ne, yayin da wasu ƙasashen duniya ke kira ga samun diflomasiyya mai dorewa.

    A gefe guda, shugabannin Iran suna bayyana cewa za su ci gaba da tattaunawa kan batun.

  14. El-Rufai na hannunmu - ICPC

    ....

    Asalin hoton, Muyiwa Adekeye/X

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya ICPC ta sanar cewa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, na hannunta daga jiya ranar Laraba 18 ga Fabrairu 2026.

    Sanarwar wadda mai magana da yawun hukumar, J. Okor Odey, ya fitar ta ce "El-Rufai na hannun mu a halin yanzu domin tambayoyi masu alaƙa da binciken da muke yi."

    Hakan na zuwa ne bayan da tsohon gwamnan ya shafe kwanaki uku a hannun EFCC, bayan ya kai kansa a ranar Litinin domin amsa gayyata kafin daga bisani suka tsare shi, sannan aka samu labarin ya koma hannun ICPC daga EFCC.

    El-Rufai dai wanda ke cikin jagororin adawa a ADC da ke shirin ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Tinubu na APC a zaɓe mai zuwa, ya zargi gwamnati da matsa wa ‘yan adawa lamba ta hanyar amfani da binciken rashawa.

  15. Manyan gyare-gyaren da aka yi wa dokar zaɓen Najeriya

    ....

    Asalin hoton, X/Tinubu

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanya hannu kan ƙudurin dokar zaɓen ƙasar na 2026, wanda aka yi wa gyaran fuska.

    Shugaban ya sa hannu kan dokar – wadda ta ƙunshi ƙa'idojin yin zaɓukan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomin yankin birnin tarayya - ne ranar Laraba a Abuja, gaban manyan jami'an gwamnati.

    A lokacin sanya hannu kan dokar, Tinubu ya ce "babu batun siyasa a cikin wannan gyare-gyare. Abu ne na tsari. Ƙoƙari ne na cike giɓi da ƙarfafa tsari da kuma samar da tsaftatacciyar hanya ga masu tsarawa da kuma masu yin zaɓuka."

    Shugaban na Najeriya ya sanya hannu kan dokar ne kwana ɗaya bayan hargitisn da aka samu a zaurukan majalisar tarayyar ƙasar game da amincewa da gyaran da aka yi wa dokar.

    Dokar wadda majalisar dattijai da ta wakilai suka amince da ita a ranar Talata ta bayar da damar tura sakamako daga rumfunan zaɓe ta laturoni da kuma ta takarda kamar yadda aka saba, ta yin amfani da fom ɗin EC8A.

  16. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.