Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 19/05/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 19 ga watan Mayun, 2024.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Muhammad Annur Muhammad

  1. Tarayyar Turai da ƙasashen duniya na taimaka wa wajen gano inda jirgin ya yi haɗari

    Jirgi mai saukar ungulu da motoci

    Asalin hoton, IRNA

    Ƙasashe da dama na tayin bayar da taimako ga Iran wajen gano inda jirgin ya yi hadari tare da ceto.

    Zuwa yanzu Rasha da Azerbaijan da Armenia da Iraqi dukkaninsu sun yi tayin taimakawa wajen gano jirgin.

    Haka kuma Rasha ta ma yi tayin taimakawa a binciken abin da ya haddasa hadarin.

    Ita Hadaddiyar Daular Larabawa ta gabatar da tayinta na taimakawa, ta kuma ce tana tare da Iran.

    Turkiyya kuwa tuni ta aika ta tawagar kwararrn masu aikin agaji a tsaunuka zuwa kasar ta Iran, kuma tun da farko Shugaba Tayyip Erdogan ya ce hadarin ya sanyaya masa jiki.

    Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ce, ta shiga aikin taimakawa wajen gano inda jirgin sama mai saukar ungulun da ya yi hadari da Shugaba Raisi da ministansa na harkokin waje yake.

    EU ta ce tana amfani da na'urorinta na daukar hotunan tauraron dan'Adam don gano ainahin inda hadarin ya auku.

    A wani sako da kwamishinan kungiyar ta Turai kan agaji, Janez Lenarcic ya sanya a shafinsa na X, ya ce EU na taimakawa ne kamar yadda Iran ta nemi agaji daga kungiyar.

    Ita kuwa fadar gwamnatin Amurka ta ce an yi wa Shugaba Biden bayani a kan hadarin na Iran.

    A nasu bangaren hukumomin Iran din sun ce an tura tawaga wajen 40 ta masu aikin agaji domin gano inda lamarin ya faru.

    Masu aikin neman suna amfani da karnuka da kuma kananan jiragen sama marassa matuka a aikin, wanda ke da wuyar gaske saboda tsananin rashin kyawun yanayi da kuma tsaunuka da ke yankin.

  2. Jagoran addini na Iran ya buƙaci a yi wa Shugaba Raisi addu'a

    Ayatollah Ali Khamenei

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Ayatollah Ali Khamenei ya ce babu aikin Iran da zai tsaya

    Babban jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bukaci a yi wa Shugaba Ebrahim Raisi addu'a bayan rahotannin da ke cewa jirgin da yake ciki ya yi hadari.

    Kafar yada labarai ta kasar ta IRIB ta bayar da rahoton Khamenei yana kira ga kasar ta yi addu'a kan lafiyar Raisi.

    Babban jagoran addinin ya karada cewa, ''Idan al'ummar Iran ba za su damu ba, babu ayyukan kasar da za su tsaya.''

  3. Wane ne Ebrahim Raisi?

    Ebrahim Raisi

    Asalin hoton, EPA-EFE/REX/Shutterstock

    An zabi Raisi, mai shekara 63, a matsayin shugaban Iran a yunkurinsa na biyu na zama shugaban a 2021.

    Ana yi masa kallon malami mai ra'ayin rikau sannan ana daukansa a matsayin wanda ake ganin wata rana zai gaji babban shugaban addini na kasar ta Iran Ayatollah Khamenei, da ke kan wannan matsayi tun 1989.

    A 2019, babban shugaban addinin ya nada shi a matsayin shugaban bangaren shari'a na kasar, wanda mukami ne mai karfin gaske.

    Haka kuma an zabi Raisi a matsayin mataimakin majalisar kwararrun, wadda majalisa ce ta manyan malamai 88 da ke zaben babban shugaban addini na kasar na gaba.

  4. Red Crescent ta musanta rahotan batan ma'aikatanta

    Tun da farko kakakin kungiyar agaji ta Red Crescent, ya ce ma'aikatansu guda uku da ke aikin neman jirgin saman da ya yi hadari sun bata.

    To amma kuma a yanzu kungiyar ta fito ta ce babu wani ma'aikacinta da ya bata

    Babbar mai magana da yawun kungiyar ta ce duk wata sanarwa ko karin bayani game da aikin ceton ya kamata ya ne daga tawagar musamman da ke aikin ceton.

  5. Azerbaijan ta ce hankalinta ya tashi kan rahotannin haɗarin jirgin

    Shugaban Iran da na Azerbaijan

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Azerbaijan Ilham Aliyev ya ce, ya kadu sosai bayan rahotannin da ya samu na kadarin jirgin na Shugaba Ebrahim Raisi.

    Tun da farko Shugaba Aliyev ya kasance tare da shugaban na Iran waen bikin bude madatsun ruwa biyu a kusa da iayakar Iran din da Azerbaijan.

    Shugaban ya ce, "A yau bayan mun yi sallama da Shugaban Jamhuriyyar Musulunci ta Iran, Ebrahim Raisi, hankalinmu ya tashi bayan labarin da muka samu na hadarin jirgin sama mai saukar ungule da ke dauke da tawagar ta Iran," kamar yadda ya rubuta a shafinsa na X.

    "Muna addu'a ga Allah ga Shugaba Ebrahim Raisi da tawagar da ke masa rakiya".

    Shugaban ya kara da cewa kasarsa a shirye take ta nayar da dukkanin taimakon da ake bukata.

  6. Raisi ya halarci bikin buɗe madatsar ruwa kafin haɗarin jirgin

    Ebrahim Raisi da Ilham Aliyev

    Asalin hoton, Iranian Presidential Office

    Bayanan hoto, Ebrahim Raisi ya ziyarci madatsar ruwa tare da shugaban Azerbaijan Ilham Aliyev

    Kamar yadda rahotanni ke cewa shugaban na Iran yana kan hanyarsa ta zuwa birnin Tabriz da ke arewa maso gabashin kasar bayan komawa daga iyakar Iran da Azerbaijan lokacin da lamarin ya faru.

    Raisi na kai ziyara a kan iyakar Iran da Azerbaijan, inda ya bude madatsun ruwa na Qiz Qalasi da Khodaafarin tare da takwaransa na Azerbaijan, Ilham Aliyev.

  7. Ma'aikatan agaji uku sun ɓata in ji ƙungiyar Red Crescent

    Ma'aikacin agaji

    Asalin hoton, IFRC

    Ma'aikatan agaji uku da ke aikin neman jirgin sama mai saukar ungulu da ke dauke da shugaban na Iran sun bata, in ji kakakin kungiyar agaji ta Red Crescent.

    Kakakin ya kara da cewa tawagar ma'aikatan agajin na kusa da inda jirgin ya watakila jirgin ya yi hadari.

    Sun ce aikin neman zai gamu da cikas saboda ana sa ran yanayin sanyi zai karu sosai nan da dan lokaci, kuma za a samu karin ruwan sama.

  8. Shekara biyu da ta wuce jirgin da ke dauke da ministan wasanni na Iran ya fadi a Kerman

    Jirgin sama mai saukar ungulu na kungiyar agaji ta Red Crescent a kasa

    Asalin hoton, TASNIM

    Shekara biyu da ta gabata jirgin sama mai saukar ungulu da ke dauke ministan wasanni na Iran Hamid Sajjadi, ya yi hadari a lardin Kermano.

    Mista Sajjadi tare da mutane da dama da ke cikin jirgin da suka hada da Ismail Ahmadi, mai ba wa ministan shawara da babban daraktan a ofishin ministan sn rasu a hadarin.

    Tawagar tana komawa Tehran ne daga Bafat a cikin jirgin saman mai saukar ungulu na kungiyar agaji ta.

    Binciken da hukumomi suka yi ya nuna cewa kuskuren mutum ne ya haddasa hadarin ba wata matsala ta na'ura ko injin jirgin ba.

    Wata biyu kafin wannan hadarin shugaban kungiyar agaji ta Red Crescent Society a Iran ya ce jiragen sama masu saukar ungulu na agaji na kungiyar guda 10, ba sa aiki saboda rashin kudaden gyara su.

  9. Muna sanya ido kan labarin hatsarin jirgin shugaban Iran - Amurka

    Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Amurka ya ce ƙasarsa na ''sanya idanu cikin tsanaki'' game da labarin hatsarin jirgi mai saukar ungulu da ke ɗauke da shugaban Iran da ministan harkokin wajen ƙasar.

    "A yanzu babu abin da za mu ce game da batun,"in ji shi.

    Rahotonni daga ƙasar na cewa shugaba Biden ya samu labarin hatsarin jirgin na shugaban Iran

  10. Hoton jirgin Ebrahim Raisi kafin faruwar hatsarin

    .

    Asalin hoton, IRNA

    Wannan ne hoton jirgin da ke ɗauke da shugaban Iran Ebrahim Raisi, da aka ɗauka jim kaɗan kafin faruwar hatsarin.

    An ɗauki hoton ne bayan kammala bikin ƙadamar da madatsar ruwa a gabashin ƙasar.

  11. Za a ɗauki lokaci kafin a gano inda jirgin yake - Ministan cikin gida

    Ministan cikin gida na Iran, Ahmad Vahidi ya ce za a ɗauki lokacin kafin a gano inda jirgin yake, a yayin da tawagar ceto ke ci gaba da neman jirgin.

    Yayin da yake jawabi a gidan talbijin na ƙasar, Vahidi ya ce za a ɗauki lokaci kafin a gano wurin da jirgin yake, sakamkon rashin kyawun yanayi a yankin.

    "Komai zai daidaita, masu aikin ceto na ci gaba da aikinsu, muna fatan samun nasara nan ba da jimawa ba,'' in ji shi.

  12. Abin da muka sani game da hatsarin jirgi a Iran

    Shugaban ƙasar, Ebrahim Raisi ya yi tafiya da farko zuwa gabashin ƙasar domin ƙaddamar da wata madatsar ruwa a kan iyakar ƙasar.

    Daga cikin mutanen da ke cikin tawagar shugaban akwai ministan harkokin ƙasashen waje, Hossein Amirabdollahian, da gwamnan lardin gabashin Azarbaijan, Malik Rahmati, da limamin Juma'a na Tabriz, Muhammad Ali Al Hashem.

    Kamfanin dillancin labaran ƙasar IRNA, ya ce "mummunan yanayi da gajimare na kawo tarnaƙi ga ayyukan ceto.

  13. Labarai da dumi-dumi, Jirgi mai saukar ungulu a cikin tawagar shugaban Iran ya yi hatsari

    Kafofin yaɗa labaran sun ce wani jirgi mai saukar ungulu da ke cikin tawagar shugaban Iran ya yi hatsari.

    Kawo yanzu ba a sani ba ko shugaban na Iran, Ebrahim Raisi na cikin jirgin, wanda kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ce ya fuskancin matsalar.

    Ministan cikin gida na ƙasar ya ce masu aikin ceto na ƙoƙarin isa wurin da lamarin ya faru sakamakon mummunan yanayin da ake fuskanta a wajen.

    Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce shugaban ƙasar Ebrahim Raisi na kan hanyarsa ta zuwa birnin Tabriz, da ke arewa maso yammacin ƙasar, bayan dawowarsa daga kan iyakar ƙasar da Azerbaijan, inda ƙaddamar da aikin buɗe wata madatsar ruwa.

    Za mu ci gaba da sabunta muku wannan labari da zarar mun samu bayanai...

  14. Lafiya Zinariya: Kan jinin al'ada tsakanin 'yan mata

    Bayanan sautiLatsa hoton da ke sama domin sauraron shirin
  15. Sojojin DR Kongo sun ce sun daƙile yunƙurin juyin mulki a ƙasar

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar kongo sun ce sun daƙile juyin mulkin - da wasu 'yan ƙasar da na ƙetare suka yi yunƙurin yi wa - shugaban ƙasar Felix Tshikedi a Kinshasa, babban birnin ƙasar.

    Cikin wani jawabi da ya ta gidan talbijin na ƙasar, mai magana da yawun sojojin ƙasar Burgediya Janar Sylavin Ekenge, ya ce a yanzu ƙura ta lafa, kuma sojojin ƙasar na tsare da wasu da ake zargi da hannu a lamarin.

    Jawabin nasa na zuwa ne sa'o'i bayan da wasu mutane ɗauke da makamai suka afka gidan tsohon shugaban ma'aikata kuma babban aminin shugaban ƙasar, da safiyar ranar Lahadi.

    Shaidu sun ce ga wasu mutane kimanin 20 sanye da kayan sojoji sun afka wa gidan sannan suka ji ƙarar harbe-harben bindiga.

    Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce maharan mambobin wata ƙungiya ce da ake kira 'New Zaire Movement' mai alaƙa da ɗan siyasar ƙasar da ke zaman gudun hijira a ƙetare, Christian Malanga.

    Harin ya yi sanadiyyar mutuwar masu gadin gidan biyu da mahari guda.

    Kawo yanzu shugaban ƙasar Felix Tshisekedi bai ce komai ba game da batun.

  16. SERAP ta kai ƙarar gwamnonin Najeriya 36 da ministan Abuja

    .

    Asalin hoton, Kaduna Gov/X

    Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci a Najeriya, ta kai ƙarar gwamnonin jihohin ƙasar 36 da ministan birnin tarayya Abuja, saboda zarginsu da gaza yin bayanin yadda suka kashe maƙudan kuɗaɗen da suka samu daga kason Asusun Tarayya na FAAC, tun daga shekarar 1999.

    Cikin wata sanarwar manema labarai da mataimakin daraktan ƙungiyar, Kolawole Oluwadare ya fitar ranar Lahadi, ya ce ƙungiyar ta ɗauki matakin ne sakamakon rahoton da ta samu cewa a cikin watan Maris FAAC ta raba naira tiriliyan 1.123 tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi da ƙananan hukumomi.

    Haka kuma sun raba naira tiriliyan 1.208 a watan Aprilu, kamar yadda ƙungiyar ta bayyana.

    SERAP ta ce FAAC ya raba wa jihohin ƙasar 36 naira biliyan 398.689 a watan Maris kawai, yayin da aka raba musu naira biliyan 403.403 a watan Afrilu.

    Haka kuma ƙungiyar ta buƙaci kotun ta tilasta wa gwamnonin tare da ministan Abuja, su gayyato hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa na ƙasar, watau EFCC ta ICPC domin su binciki zarge-zargen almundahana da kason arzikin da jihohin ke samu daga asusun tarayyar, tare da yin nazarin yadda jihohin suka kashe kuɗaɗen.

    Ƙungiyar ta ce ''Yan Najeriya na da haƙƙin sanin yadda gwamnonin jihohin ke kashe kuɗaɗen jihohinsu ciki har da kason da suke samu daga asusun tarayya''.

    SERAP ta kuma koka kan yadda ta ce ''duk da ƙarin kuɗin da jihohin suka samu daga FAAC ɗin, har yanzu miliyoyin al'ummominsu na fama matsanancin talauci da rashin muhimman abubuwan more rayuwa.

    Ƙungiyar ta kuma yi zargin cewa ''sakamakon cire tallafin man fetur da ƙoƙarin gwamnatin tarayya na farfaɗo da darajar kuɗin ƙasar, gwamnatin ƙasar ta ƙara wa jihohin abin da suke samu daga FAAC, amma duk da haka babu wani cigaba da aka samu a fannin tsaro da walwalar miliyoyin 'yan ƙasar''.

    SERAP ta yi zargin cewa jihohin ƙasar 36 da Abuja na kashe kuɗaɗen da suke samun daga asusun FAAC ta hanyoyin da ba su dace ba.

    “Muna zargin cewa kuɗaɗen da suke samu daga FAAC, suna amfani da su ne ta hanyoyin da ba su dace ba tare da karkatar da su zuwa wasu fannoni, ga kuma batun yin watsi da ayyukan da suka fara. Haka kuma muna zargin jihohin da kashe kuɗin kan wasu abubuwa kamar yaƙin neman zaɓe da sabgogin siyasarsu'', in ji sanarwar.

  17. Amsoshin Takardunku 19/05/24

    Bayanan sautiLatsa hoton da ke sama domin sauraron shirin
  18. Tsoffin gwamnonin Zamfara huɗu sun gana kan 'matsalar tsaron jihar'

    .

    Asalin hoton, Yusuf Idris Gusau

    Tsofaffin gwamnonin jihar Zamfara huɗu sun yi wata ganarwar sirri domin tattauna yadda za a magance matsalar tsaro da ke addabar jihar.

    Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam'iyyar APC na jihar Zamfara, Yusuf Idris Gusau ya fitar ya ce tsofaffin gwamnonin jihar - da suka haɗa Sanata Ahmed Sani Yariman Bakura da Alhaji Mamuda Aliyu Shinkafi da Sanata Abdulaziz Yari Abubakar da kuma ƙaramin ministan tsaron ƙasar, Bello Mohammed Matawalle - sun gana ne a jiya da Asabar da daddare.

    ''Tsoffin gwamnonin - da suka gana a gidan ministan tsaron - sun ɗauki tsawon lokaci suna tattaunawa kan batutuwan da suka shafi matsalar tsaron jihar da nufin lalubo hanyoyin magance matsalar, don inganta ci gaban rayuwar al'ummar jihar ta fannonin ilimi da na lafiya'', in ji sanarwar.

    Sanarwar ta kuma ambato gwamnonin na cewa idan ana batun tsaro, ya kamata a ajiye duk wani bambanci musamman na siyasa da ke tsakani domin sama wa al'umma mafita.

    A baya-bayan nan dai jihar Zamfara na fama da ƙaruwar hare-haren 'yan bindiga da ke sace mutane domin neman kudin fansa.

  19. Hanya ɗaya tilo da ta rage wa Arsenal cin kofin Premier

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Da maraicen yau ne za a ƙarƙare wasu daga cikin gasannin nahiyar Turai da wasu sassan duniya, ciki har da Premier League ta ƙasar Ingila.

    A wasu gasarnin ƙasashen tuni aka samu waɗanda suka lashe su, kamar Bundesliga da La Liga da Serie A.

    Amma a gasar Premier Ingila har yanzu akwai sauran rina a kaba, domin kuwa wasan na yau shi ne zai zama raba-gardama tsakanin Pep Guardiola da Arteta.

    A yanzu haka Manchester City ce ke jagorantar teburin da maki 88 tazarar maki biyu tsakaninta da Arsenal mai 86.

    Arsenal na fatan ɗaukar kofin karo na farkon cikin shekara 20, yayin da Manchester City ke fatan kafa tarihin lashe kofin karo huɗu a jere.

    Ko wace hanya Arsenal za ta bi domin ɗaukar kofin?

  20. Abubuwan bajinta da suka faru a Gasar Premier da za a kammala yau

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    A yau Lahadi ne za a kammala gasar Premier League da wasa 10 a filaye daban-daban a kuma duka a lokaci guda.

    Wannan ita ce ɗaya daga babbar gasar tamaula ta Ingila da ba a taɓa yin irinta ba a tarihi, kama daga bajintar cin ƙwallaye da tasirin da gasar ke da shi a faɗin duniya, da sauran abubuwa.

    Ga wasu jerin abubuwan tarihin da aka yi kakar wasanni ta bana.

    Cin ƙwallaye:

    Kawo yanzu an zura ƙwallo 1,209 kwawo yanzu, kakar da aka fi zurawa a raga ita ce ta 2022/23, wadda a wasa 380 aka ci 1,084 a raga.