Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Tinubu ya buƙaci ƴan Najeriya su mayar da al'amuransu ga Allah

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi and Abdullahi Bello Diginza

  1. Rufewa

    Masu bin mu a wannan shafi nan muka kawo ƙarshen labarai da rahotonnin abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sasan duniya musamman kan shagulhulan bikin Babbar Salla.

    Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu sake dawo wa domin kawo muku sabbin labarai.

    Abdullahi Bello Diginza ke cewa a ci naman salla a hankali

  2. Babu sulhu tsakaninmu da 'yan bindiga - Gwamnatin Zamfara

    Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta ce ba za ta yi sulhu da 'yan bindigar da ke addabar jihar, a wani sabon mataki na samar da tsaro a jihar

    Hakan na zuwa ne a yayin da ‘yan bindigar ke ci gaba da kashe mutane tare da satar wasu domin karbar kudin fansa.

    Sabanin tsarin tsohuwar gwamnatin jihar Zamfara na tataunawa da ‘yan bindiga da zummar kawo ƙarshen zubar da jini, a yanzu gwamnatin Zamfara ta PDP ta nuna cewar babu batun sulhu tsakaninta da ‘yan bindiga.

    Babban mataimakin gwamnan jahar Zamfara akan kafafen watsa labarai Malam Mustapha Muhammad Kaura, ya shaida a BBC cewa sabuwar gwamnatinsu ba za ta lamunci yin sulhu da ɗan bindiga ko ɗan ta'adda ba.

    Ya ci gaba da cewa ''Shi tsari na sulhu ba zai yiyu a ce gwamnati ce ke neman sulhu, in ma ta ce tana neman sulhu to yaudara ce, domin kuwa sulhun nan yau shekara 13 ana wannan maganaa jihar zamfara''.

    ''Shin ka zo ka yi sulhu da 'yan bindiga a kan me? a kan ka kasa? Sai an karbe makamai'', Malam Mustapha Muhammad Kaura

    Ya ce babu wani matakin da gwamnatin za ta ɗauka da ya wuce murkushe 'yan bindigar.

    A shekarun baya dai, tsohon gwamnan jahar Zamfara, Bello Mutawalle, ya yi ta bukukuwan yin sulhu da ‘yan bindiga.

    To sai dai bisa ga dukkan alamu kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba.

    • Yadda aka karbo mutum 75 daga hannun 'yan bindiga a Zamfara
    • 'Yadda matata ta haihu a wajen masu satar mutane a Zamfara'
  3. Biden ya ce Putin ya zama saniyar ware a idon duniya

    Shugaba Joe Biden na Amurka ya ce shugaban Rasha Vladimir Putin ya zama saniyar ware a idon duniya, kuma a bayyane take karara babu wata nasara da yake samu a yakin Ukraine, ga kuma matsalolin yakin cikin gida.Mista Biden ya ara da cewa, gwiwar Mista Putin ta yi sanyi tun bayan boren da mayaƙan ƙungiyar Wagner ta yi a ƙarshen mako.Shugaban na Amurka ya ce ba a abin da zai faru nan gaba ba, ko daga bangaren kasashen waje, amma kowa ya san tarihin wagner.

    Mista Diden ya ce babu shakka akwai dalilin da ya sanya ƙungiyar yin abin da ta aikata.

    ''Ga su can kuma an ba su kyakkyawar mafaka a Belarus mai iyaka da Poland'', in ji Mista Biden.

    Shugaban kasar Poland Andrzej Duda, ya ce kasancewar Yevgeny Prigozin da tawagarsa a makofciyar ƙasarsa Belarus, babbar barazana ce ga tsaron ƙasarsa da Lithuania da kuma Latvia.

  4. Hotunan yadda wasu shugabanni suka gudanar da sallar Idi

  5. Abin da ke sa wayarku zafi da yadda za ku magance hakan

  6. An gano tarkacen sunduƙin yawon buɗe idon Titanic

    A karon farko tun bayan ɓacewarsa, an gano tarkacen sunduƙin da ya yi ƙokarin zuwa wajen jirgin ruwan Titanic.

    A makon da ya gabata ne aka bayar da rahoton cewa duka mutum biyar da ke cikin sunduƙin sun mutu.

    A ranar Laraba ne aka gano tarkacen sunduƙin a gaɓar tekun ruwan canada

    Hotunan da aka yaɗa sun nuna wasu tarkacen karafunan jirgin a lokacin da ake cire su daga cikin tekun ta hanyar amgani da na'urar lalubo abubuwa a cikin teku.

    A ranar 18 ga watan yuni ne aka bayar da rahoton mutuwar duka mutanen da ke cikin sunduƙin, bayan ya yi nisa a ƙoƙarinsa na zuwa inda jirgin ruwan Titanic ya yi hatsari.

  7. Ya rage wa ƙasashen Afirka ci gaba da alaƙa da Wagner - Rasha

    Mai magana da ma'aikatar harkokin wajen Rasha Maria Zakharova ta ce zaɓin ci gaba da alaƙa tsakanin ƙasashen Afirka da ƙungiyar sojojin hayar Rasha ta Wagner ya rage na hannun ƙasashen na Afirka.

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambato Misis Zakharova na cewa zaɓi ya rage wa ƙasashen na Afirka.

    Kamalan na Misis Zakharova na zuwa ne bayan da ƙungiyar Wagner ta gudanar da tawayen da bai yi nasara ba a karshen makon da ya gabata.

    Lamarin da ya sa shugaban ƙasar Vladimir Putin ya yanke alaƙa da ƙungiyar, duk da cewa babu wani bayani game da makomar kungiyar a ƙasashen Afirka.

    "Ko za su ci gaba da aiki a Afirka a matsayin kwantiragi, kuma su ci gaba da kasancewa a can, wannan zaɓi ne da ya rage wa ƙasashen na Afirka,''in ji Misis Zakharova.

    Dubban sojojin hayar Rasha aka kai ƙasashen nahiyar Afirkan tun 2018, inda mafi yawansu ke aiki a ƙasashen Jamhuriyar Tsakiyar Afirka da Mali.

  8. Manyan hafsoshin Najeriya sun yaba wa dakarun ƙasar da ke fagen daga

    Babban hafsan hafsoshin Najeriya Manjo Janar Christopher Musa da babban hafsan sojin ƙasar na ƙasar Manjo Janar Toareed Lagbaja sun yaba wa dakarun sojin ƙasar musamman waɗanda ke fagen daga, bisa sadaukarwa da kishin ƙasa da jajircewa da suke nunawa wajen tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da haɗin kan ƙasar.

    “Tabbatar da tsaro da ci gaban ƙasarmu wani babban nauyi ne da ya rataya a wuyan kowanne ɗan Najeriya'', kamar yadda dakartan yaɗa labaran hukumar tsaron ƙasar ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin babban hafsan tsaron ƙasar.

    Janar Musa ya tabbatar wa jami'an tsaron ƙasar irin goyon bayan da yake ba su a ƙoƙarinsu na gudanar da ayyukansu.

    A nasa ɓangare, babban hafsan sojin ƙasa na ƙasar Manjo Janar Toareed Lagbaja ya yaba wa sojojin ƙasa na Najeriyar dangane da saudaukarwa da jajircewa da ya ce sojojin na nunawa wajen gudanar da ayyukansu a faɗin kasar.

    Ya kuma yi kira ga dakarun sojin su ci gaba da nuna jarunta da kishin ƙasa a yayin gudanar da ayyukansu.

    A makonni biyu da suka gabata ne shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa sabbin hafsoshin tsaron ƙasar, bayan sauke tsoffin dakarun tsaron.

  9. Yankin arewa maso gabashin Najeriya na dab da faɗawa ƙangin yunwa - MDD

    Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargaɗi game da ƙaruwar buƙatun ayyukan jin ƙai a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

    Fiye da mutum 40,000 ne aka kashe tare da raba kusan mutum miliyan biyu da muhallansu a yaƙin da aka kwashe shekara 14 ana gudanarwa tsakanin Sojoji da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi, da suka haɗar da Boko Haram.

    Babban jami'in kula da ayyukan jin-ƙai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya Matthias Schmale, ya ce dole ƙasashen duniya su gaggauta ɗaukar mataki kafin al'amura su taɓarɓare a yankin.

    Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ambato Mista Schmale na cewa "fiye da mutum 500,000 ne ke fama da matsalar ƙarancin abinci: Saura kiris su faɗa ƙangin yunwa. Don haka muke ankarar da jama'a''.

  10. Sarkin Saudiyya ya miƙa gaisuwar salla ga mahajjatan bana

    Shugaban masallatai biyu masu alfarma Sarki Salman bin Abdulaziz na Saudiyya ya aike da sakon gaisuwar salla ga mahajjatan da ke gudanar da aikin Hajjin bana da kuma sauran musulmai a faɗin duniya

    Cikin wani saƙo da sarkin ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce: ''A wannan rana mai albarka ta babbar salla, muna roƙon Allah S.W.T ya amashi ibadun da mahajjanmu ke gudanarwa, muna roƙon Allah ya kawo wa ƙasarmu ci gaba da kwanciyar hankali, da musulman duniya baki ɗaya, ina yi muku barka da salla''

    Sarkin ya ƙara da cewa ''Mun ji daɗin yadda ake gudanar da aikin hajjin bana, wanda ke nuna 'yan uwantaka da hadin kai da jin-ƙai da alhazai ke nuna wa junansu a lokacin gabatar da ibadar aikin hajjin, sun manta da bambancin muƙami ko matsayi duk sun haɗu domin manufa guda, wato bautar ubangijinsu''.

    Kimanin alhazai fiye da miliyan biyu ne dai ke gudanar da aikin hajjin na bana a Saudiyya, karon farko da aka samu adadi mai yawa na mahajjata, tun bayan ɓarkewar annobar corona a shekarar 2019.

    • An kashe Babban Dogarin Sarki Salman na Saudiyya
    • An buɗe wa mata damar shiga aikin soja a Saudiyya
  11. Ɗan sanda ya harbe wani matashi a Faransa

    Zanga-zanga ta kaure a birnin Paris bayan wani ɗan sanda ya harbe wani matashi mai shekara 17 saboda ya ƙi tsayawa a lokacin da danjar kan hanya ta tsayar da shi.

    Bidiyon da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna ɗan sandan na saita direban motar da bindiga kafin daga baya aka ji ƙarar bindigar.

    Matashin mai suna Nahel ya mutu bayan da harsashin ya ɓula masa ƙirji, duk kuwa da kokarin ceto ransa da likitoci suka yi.

    A yanzu dai an tsare ɗan sandan da ake zargi da kashe matashin, inda ake tuhumarsa da aikata kisan kai.

    Lamarin dai ya haifar da ɓarkewar zanga-zanga ranar Talata da daddare a unguwar Nanterre, yankin da ke yammacin birnin Paris inda aka kashe matashin.

    Kawo yanzu an kama mutum 31 sakamakon zanga-zangar.

    • Yadda wani mutum ya caccaka wa yara wuƙa a Faransa
    • 'Yan sandan Faransa sun kashe wani a farautar 'yan ta'adda

    Nahel ne mutum na biyu da aka kashe a Faransa cikin wannan shekara sakamakon harbin da 'yan sanda ke yi a wuraren bayar da hannu a kan titunan ƙasar.

    A shekarar da ta gabata mutum 13 ne suka mutu ta dalilin wannan hanya.

    Kafar yaɗa labaran Faransa ta ambato 'yan sandan na cewo matashin ne ya tuƙo mota inda ya haro inda suke da niyyar cutar da su.

    To sai dai bidiyon da ke yawo a shafukan sada zumuntan ba su nuna alamun hakan ba.

    Bidiyon ya nuna 'yan sandan biyu na tsaye a kan motar. Inda ɗaya daga cikinsu ke nuna direban da bindiga, inda ya yi harbi a daidai lokacin da direban ya yi yunƙurin tuƙa motar.

    Shugaban Faransa ya bayyana lamarin a matsayin abin da ba za a ''lamunta ba'', yana mai cewa wannan harbi ne na babu gaira babu dalili.

  12. 'Rashin kuɗi ya hana mutanen Sudan da dama yin layya'

    Mutane da dama a ƙasar Sudan - inda ɓangarorin da ke faɗa da juna suka amince da tsagaita wuta domin bai wa fararen hula gudanar da bikin babbar salla - ba su samu damar gudanar da bukukuwan sallar kamar yadda ya kamata.

    Sallah babbar salla na nufin 'bukukuwan yanka dabbobi'', abin da ke tunasar da lokacin da Allah ya umarci Annabi Ibrahim A.S ya yanka ɗansa Annabi Isma'il. Yayin da yake dab da yanka shi sai Allah ya musanya ɗan da rago.

    Domin tunawa da wannan rana musulmai a faɗin ƙasashen duniya ciki har da Sudan kan yanka dabbobi daban-daban domin raba wa iyalai da abokan arziki da mabuƙata naman.

    To sai dai ministan harkokin addinin ƙasar Sudan Abdel Ati Abbas ya faɗa wa BBC cewa tsadar dabbobin da aka samu a wannan shekara - sakamakon yakin da aka kwashe makonni kusan 10 ana gudanarwa - zai sa iyalai da dama ba za su iya gudanar da ibadar a bana ba.

    “Matsalar yaƙin ta shafi ɓangarori da dama ciki har da kasuwar dabbobi ta Sudan, domin kuwa 'yan ƙasar da dama ba su iya sayen dabbobin layya a wannan shekara ba'', in ji Ministan.

    Mohammed Abboud Soliman, wani dillali ne a kasuwar dabbobi ta jihar Kordofan ta Yamma, ya kuma shaida wa BBC cewa “A kowacce shekara mukan saro dabbobi masu yawa domin sayar da su a lokacin sallar layya, to amma wannan shekara lamari ya sauya. Saboda yakin da ake yi a ƙasar, ya sa da yawa ba su iya sayen dabbobin layyar ba, saboda tsadar farashinsu''.

    • Me za a yi da gawawwakin mutanen da aka kashe a Khartoum?
    • An kashe gwamnan jihar Darfur ta Yamma a Sudan
  13. Ƙayatattun hotunan kwalliyar Idi daga ƙasashen duniya

    Babbar Sallah ko kuma Eid al-Adha - wadda ke nufin 'lokacin yin layya' lokaci ne na yin koyi da annabi Ibrahim wanda ya bi umarnin Ubangiji wajen sadaukar da ɗansa annabi Isma'il.

  14. An rantsar da Maada Bio a matsayin shugaban Saliyo karo na biyu

    Jim kaɗan bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar Saliyo, Julius Maada Bio ya sha rantsuwar kama aiki a karo na biyu.

    Hakan na zuwa ne duk da cewa jam'iyyar adawa ta ƙasar ta bayyana zaɓen a matsayin mara inganci.

    Alƙaluman da hukumar zaɓe ta ƙasar ta fitar sun nuna cewa Mista Bio ya samu kashi 56% na ƙuri'un da aka kaɗa, yayin da babban abokin hamayyarsa Samura Kamara ya samu kashi 41%.

    A lokacin da aka bayyana kashin farko na sakamakon zaɓen a ranar Litinin, Samura Kamara ya bayyana lamarin a matsayin 'fashi da rana tsaka.'

    Masu sanya ido daga waje sun nuna damuwa kan rashin yin komai a faifai sa'ilin ƙirga ƙuri'u.

    An gudanar da zaɓen ne cikin halin ɗarɗar saboda rikice-rikice da aka rinƙa samu gabanin zaɓen, sai dai shugaba Bio ya buƙaci al'ummar ƙasar su kwantar da hankula.

    A cikin dare, ranar Talata ne ka rantsar da shugaban ƙasar mai shekara 59 a wa'adin mulki karo na biyu na shekara biyar.

    Magoya bayan shugaban ƙasar sun rinƙa tattaki suna murna a Freetown, babban birnin ƙasar.

  15. Tinubu ya buƙaci ƴan Najeriya su mayar da al'amuransu ga Allah

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu wanda ya yi sallar Idi a birnin Lagos ya amince cewa Najeriya na fuskantar kalubale mai tarin yawa amma kuma a cewarsa yana kokarin samar da hanyoyin magance matsalolin.

    A cikin sanarwar da ya fitar na taya musulmin Najeriya murnar Barka da Sallah, Asiwaju Tinubu ya ce "Dole ne mu gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya ba mu damar halartar wata Sallar Idi".

    Ya ƙara da cewa Allah ba ya ɗora wa mutum abin da ba zai iya ɗauka ba."

    "Allah Ya san halin da ƴan Najeriya ke ciki kuma zai kawo musu sauƙi."

    Sannan ya buƙaci al'umma da su yarda cewa ƙasar za ta gyara, su kuma haɗa hannu wajen cimma nasarar hakan.

    Ya kara da cewa gwamnatinsa ta fara neman hanyar magance matsalolin da ke addabar kasar ta hanyar shawarwarin da suke samu daga wajen kwararru don gyara tattalin arziƙi da kuma kawarda duk wani cikas da zai hana bunƙasar Najeriya.

    • Muhimman alƙawuran da Tinubu ya ɗauka
    • Na san ƙuncin da janye tallafin mai ya jefa ku - Tinubu
  16. Hotonun yadda Tinubu ya yi sallar Idi a Legas

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya halarci sallar Idin ne a filin Idi na 'Dodan Barak' da ke unguwar Obalende a birnin Legas.

    Bayan kammala sallar, Tinubu ya buƙaci al'ummar Najeriya su guji rikice-rikice na banbancin addini da na ƙabila.

    Waɗanda suka raka shugaban ƙasar wurin sallar sun haɗa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, da shugaban ma'aikatan fadar gwamnati, Femi Gbajabiamila, da kuma toshon ministan ayyuka da gidaje Babatunde Raji Fashola.

  17. Bidiyon jerin gwanon motocin Tinubu ya haifar da cece-kuce

    Bidiyon jerin gwano motocin da suka yi wa shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu rakiya a lokacin da ya sauka a jihar Legas ya tayar da kura, inda jama'a ke ta cece-kuce a shafukan sada zumunta.

    Shaidu sun ce sabon shugaban kasar ya samu rakiyar motoci sama da dari bayan dawowa daga Birtaniya domin gudanar da bikin Babbar Sallah a Legas.

    Kazalika an ga gwamman motocin soji na masa rakiya a hanyoyin da aka rufe aka hana kowa wucewa, abin da ya haifar da gagarumin cunkoso.

    • Tinubu ya dakatar da shugaban EFCC AbdulRasheed Bawa
    • Zan cire tallafin man fetur ko za a yi zanga-zanga a Najeriya - Tinubu
  18. An ci gaba da gumurzu a Sudan ranar Idi

    Da alama yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ayyana tsakanin ɓangarorin mayaƙa biyu da ke gumurzu da juna a Sudan, domin bikin Idin babbar sallah, ta ruguje.

    Wata mai aikin agaji, Duaa Tariq ta shaida wa BBC cewa an rinƙa jin rugugin manyan bidigogi a wasu sassa na Khartoum, babban birnin ƙasar tun da sanyin safiya.

    A ranar Talata, shugaban gwamnatin mulkin sojin Sudan, Abdel Fattah al-Burhan ya yi kira ga matasa da shiga yaƙin da ake yi da mayaƙan RSF.

    Sai dai Ms Tariq ta shaida wa BBC cewar dakarun RSF ɗin ne suka fi yawa a Khartoum, inda suka mamaye gidaje da kasuwanni da kuma titunan birnin.

    Wasu yarjeniyoyin da aka cimma a baya duk sun samu matsala a faɗan wandsa aka kwashe mako goma ana gwabzawa.

    • An kashe jarumar fina-finan Larabci a musayar wutan Khartoum
    • Tuwo na fara nema bayan dawowa gida daga Sudan- Ɗaliba
  19. Barka da Sallah

    Masu bibiyar mu ta wannan shafi muna muku barka da sallah a wannan ranar ta Laraba.

    Ku kasance tare da mu a tsawon wannan wuni inda za mu kawo muku duk wasu muhimman labarai daga Najeriya da Afirka da ma saurarn sassan duniya.

    A ci gaba da shagalin sallah cikin tsanaki.