Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Ban ce duk lalacewar Kirista ya fi ɗan takara Musulmi ba - Shettima

Wannan shafi ne da ke kawo abubuwan da ke wakana a Najeriya da ƙasashe makwabtanta da kuma sauran sassan duniya kai tsaye.

Rahoto kai-tsaye

Mukhtar Adamu Bawa, Aliyu Tanko and Haruna Kakangi

  1. Ayyukan masu haƙar zinare na barazana ga rayuwar al'ummar Ghana

    Ghana ta sake komawa kan matsayinta na wadda ke kan gaba wajen fitar da zinare daga nahiyar Afirka bayan ƙarin kashi 32 cikin ɗari a ayyukan haƙar zinaren a bara.

    Hukumar Kula da Kasuwanci ta Ghana ta alaƙanta hakan a kan bunƙasar da aka samu wajen ayyukan haƙar zinaren a manya da ƙananan ɓangarori.

    Sai dai yanzu ƙasar na fuskantar matsalar muhalli sanadiyyar ƙarin ayyukan haƙar zinaren.

    Yanzu haka dazuka da rafuka da ƙoramu duk sun lalace sanadiyyar ayyukan masu haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba, wani lamari da ya zamo mai haɗari ga al'umma.

    Ɓangaren haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba wanda ake wa laƙabi da 'galamsey', na samar wa matasa da dama hanyar rayuwa, musamman a kudancin ƙasar.

    Gwamnati da kuma masana na ganin cewa matuƙar ba a kawo ƙarshen matsalar ba to kuwa nan gaba kaɗan dole sai ƙasar ta rinƙa shiga da ruwan sha daga ƙasashen waje.

    Hatta ɓangaren noman cocoa na fuskantar barazana, kasancewar ayyukan masu haƙar ma'adanai na lalata gonaki.

    A baya gwamnati ta ɗauki matakin tura sojoji domin fatattakar masu haƙar ma'adanan ba bisa ƙa'ida ba, sai dai lamarin bai yi nasara ba.

    A 2021 dai Afirka ta Kudu ta zarce Ghana a matsayin wadda ta fi fitar da zinare daga nahiyar Afirka sanadiyyar koma baya a ɓangaren haƙar zinaren.

    Sai dai yanzu Cibiyar Kasuwanci ta Ghana ta ce ɓangaren ya samu bunƙasa sosai.

  2. 'Ana tafka ta'addanci a wasu yankunan Sudan'

    Wani ma'aikacin lafiya a Sudan ya tabbatar wa BBC cewar ƙungiyar dakarun RSF na aikata ayyukan ta'addanci kan mazauna yankunan da suke iko da su a birnin Khartoum.

    Mohammed Gibbril ya ce mayaƙan na kai samame kan dukiyar al'umma, da yin garkuwa da mutane da kuma yin sintiri kan tituna.

    Ya ce wasu daga cikin waɗanda aka ɗauka domin yi wa rundunar yaƙi har da yara ƙanana.

    Ya kuma ce a ranar Litinin an lakaɗa masa duka a lokacin ɗaya daga cikin samamen da irin waɗannan mayaƙa ke kaiwa.

    Mazauna Khartoum da dama sun bayar da shaida irin haka.

    Dakarun RSF a shafin ƙungiyar na facebook sun ce a shirye suke su tsagaita wuta.

    An dai fi martaba yarjejeniyar tsagaita wuta ta baya-bayan nan wadda ta ƙare a ranar Lahadi, fiye da sauran yarjenoyoyi da aka yi a baya.

    Sai dai an ruwaito cewa yaƙin ya sake ɓarkewa, inda mazauna birnin suka rinƙa ganin jiragen yaƙi na shawagi da kuma jin rugugin bindigogi.

  3. Ƴan bindiga sun kashe likita tare da buɗe wuta kan ƴan makarantar Islamiyya a Zamfara

    Wasu ƴan bindiga sun kai hari kan garin Jangebe da ke Ƙaramar Hukumar Talatar Mafara a jihar Zamfara, inda bayanai suka ce sun kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu.

    Ɗaya daga cikin waɗanda suka rasa rayukansu shi ne wani sanannen likita, sannan kuma ƴan bindigar sun yi garkuwa da yariman garin.

    Dan uwan likitan wanda ya zanta da BBC, ya ce ƴan bindigan sun je gidan likitan ne da misalin ƙarfe 12 na dare.

    Ya ce “suna zuwa gidan sai suka harbe shi, harbi huɗu suka yi mashi.”

    Ya kuma ce ƴan bindigan sun tafi da matan marigayin biyu da yara huɗu.

    Baya ga wannan, a yankin Shinkafi kuma ƴan bindiga sun buɗe wa wasu daliban makarantar Islamiya wuta.

    Hon Aliyu Moyi wanda ya tabbatar da faruwar hakan ga BBC, ya ce ƴan bindigan sun tafi da wasu daga cikin ɗaliban, sai dai babu wanda ya rasa ransa a cikinsu.

    Rundunar ƴan sanda reshen jihar Zamfara dai ba ta ce komai ba kan batun duk da cewa BBC ta yi ƙoƙarin tuntuɓarta ta hanyar kiran mai magana da yawunta ta waya.

    A yanzu haka dai mazauna wasu kananan hukumomin jihar Zamfara na kokawa dangane da yadda ‘yan bindiga ke kai musu jerin hare-hare, waɗanda ke sanadiyyar rasa rayuka da dama, da kuma garkuwa da wasu domin neman kuɗin fansa.

    Hakan na zuwa ne a lokacin da damina ta faɗi a yankin, inda akasarin mazauna suka kasance manoma.

  4. Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashi

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu ta ƙasa.

    Mai magana da yawun Gwamnatin Tarayya, Dele Alake ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar yau Litinin.

    Sanarwar ta ce za a ajiye kuɗaɗen da za a rinƙa bayar da bashin ne a asusun Ma'aikatar Ilimi, kuma ɗaliban manyan makarantu ne kawai za su iya cin gajiyarsu.

    Mako biyu da suka gabata ne ƙudirin, wanda shugaban Majalisar Wakilan Tarayya, Femi Gbajabiamila ya gabatar, ya tsallake karatu na uku a Majalisar Dokokin Tarayya.

    Dokar za ta bai wa ɗalibai ƴan asalin Najeriya damar karɓar bashi cikin sauƙi, wanda babu ruwa a tattare da shi daga Asusun Bayar da Bashin Karatu na Najeriya.

  5. Ƴan bindiga sun sace fasto a Kaduna

    Wasu ƴan bindiga sun sace shugaban masu wa'azi a cocin Katolika na Holy Trinity da ke Karku a ƙaramar Hukumar Kauru da ke jihar Kaduna, Rabaran-fada Jeremiah Yakubu.

    Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da daddare a gidansa da ke jikin mujami'ar.

    A lokacin da ya tabbatar da faruwar lamarin, ɗaya daga cikin shugabannin Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya a jihar Kaduna, Rabaran Joseph John Hayab, ya ce cocin ta rubuta musu takarda inda ta sanar da su kan sace malamin kiristan.

    Takardar ta buƙaci a yi addu'a domin ganin an ceto faston cikin ƙoshin lafiya.

    Kaduna na ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da sace-sacen mutane da garkuwa da su domin neman kuɗin fansa.

  6. Ban ce duk lalacewar Kirista ya fi ɗan takara Musulmi ba - Kashim Shettima

    Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya nesanta kansa da wasu kalamai da ya ce "ba daidai ba ne, kuma masu hatsari" da wasu ke alaƙantawa da shi.

    Wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran mataimakin shugaban ƙasar ya fitar, ta ruwaito Kashim Shettima na cewa kalaman da ake ambatawa ya furta lokacin wani taro da sanatoci ranar Lahadi wasu masu jamhuru ne suka kitsa a yunƙurinsu na nuna rashin dacewar 'yan takara Musulmai da ke neman shugabancin Majalisar dattijai.

    Sanarwar ta zo ne bayan wani bidiyo da ke ta yawo a shafukan sada zumunta wanda a ciki aka jiyo Kashim Shettima lokacin gabatar da jawabi, yana cewa "A wajena idan ana maganar wannan gwamnati, Kirista mafi lalacewa kuma mafi rashin ƙwarewa daga Kudancin Najeriya, ya fi Musulmin Arewa na-ƙwarai a kan muƙamin shugaban majalisar dattijan tarayyar Najeriya".

    Ya ce ba a bayyana kalaman a muhallin da aka yi su ba, kuma an canza musu ma'ana don kawai su dace da manufar masu zagon ƙasa ga burin al'ummar Najeriya na tabbatar da haɗin kan ƙasa.

    Sanarwar ta ci gaba da cewa a yayin taron da 'yan majalisar dattijai masu gangamin ganin Sanata Godswill Akpabio da Sanata Barau Jibrin sun jagoranci majalisar dattijai ta goma, Kashim Shettima ya jaddada tsarin siyasar ƙasar inda ya yi nuni da cewa samun Kirista daga kudancin Najeriya da kuma wani Musulmi daga Arewaci shi ne zai tabbatar da daidaiton adalci don inganta muradin shigar da kowa a dama da shi a gwamnatin tarayya.

    Ta ce kalaman Sanata Kashim Shettima sun taso ne sanadin wani gagarumin gangami game da rarrabuwar da ke tsakanin al'ummar ƙasar, kuma sun dace da alƙawarin jam'iyya mai mulki na ganin an dama da kowa a dukkan lardunan da rukunonin al'umma.

    Ta ambato Sanata Shettima yana nunar da cewa, bisa la'akari da ganin shugaban Najeriya da mataimakinsa duk Musulmai ne, to ba zai kasance rashin kan gado ga 'yan majalisar ba, idan suka zaɓi ɗan takarar da ba Musulmi ba, ko da kuwa akwai Musulmin da ya fi cancanta, saboda tabbatar da daidaito.

    A cewarsa, abin fargaba ne idan aka jirkita irin wannan roƙo maras harshen damo don nunar da cewa mataimakin shugaban ya ce duk lalacewar Kirista ya fi ɗan takara Musulmi.

    Kashim Shettima ya ce rashin kan gado ne ma a ce mataimakin shugaban ƙasar wanda shi kansa Musulmi ne, zai iya ƙasƙantar da ƙwarewar ɗan'uwansa Musulmi a ƙasar da Musulmi ke jagoranta, har ma ya nuna nagartar shugabancin da babu kamarta, bisa doron da aka zaɓe su ƙarƙashin inuwar jam'iyyar APC a watan Fabrairun da ya wuce.

  7. Fasinjoji 10 sun mutu a kan hanyar dawowa daga ɗaurin aure

    Aƙalla mutum goma ne suka mutu, ƙarin wasu 25 kuma suka ji raunuka bayan wata motar bas ta yi karo a wani yankin da ya shahara kan harkar barasa a ƙasar Ostireliya.

    Fasinjojin na dawowa ne daga wani ɗaurin aure a wani kamfanin sarrafa barasa cikin daren Lahadi a Hunter Valley, wani fitaccen wuri na masu yawon buɗe ido da ke zuwa shan barasa, lokacin da motarsu ta kife.

    'Yan sanda sun tuhumi direban motar bas ɗin mai shekara 58 a kan zarge-zarge guda goma masu alaƙa da mugun gudun da ya yi sanadin mutuwa.

    Sun ce har yanzu suna ƙoƙarin tantance su wane ne mutanen da suka mutu.

    Sai dai an ba da rahoton cewa ma'auratan ba sa cikin motar bas ɗin lokacin da hatsarin ya faru.

    Kwamishiniyar 'yan sanda Karen Webb ta ce wurin da aka yi karon "har yanzu ana yi masa kallon cikakken wurin da aka aikata laifi".

    Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 lokacin da a cewar 'yan sanda ake zabga tururin saukar ruwan sama a yankin. Motar dai ta hantsila a lokacin da take ƙoƙarin juyawa a wani shataletale.

  8. AC Milan na alhinin mutuwar tsohon mai kulob ɗin

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta AC Milan ta miƙa saƙon ta'aziyyarta kan mutuwar tsohon mai kulob ɗin "da ba za a manta da shi ba" wato Silvio Berlusconi wanda ya rasu yana da shekara 86 a ranar Litinin.

    Berlusconi ya sayi kulob ɗin da ke mahaifarsa a 1986, kuma ya mayar da shi ɗaya daga cikin ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa mafi samun nasara.

    A ƙarƙashin shugabancinsa, AC Milan ta lashe gasannin nahiyar Turai biyar, sai gasar Serie A sau takwas.

    A 2017 ne, ya sayar da kulob ɗin ga masu zuba jari na ƙasar China a kan kuɗi yuro miliyan 740.

    Milan ta wallafa saƙon Tuwita da ke cewa: "Cike da alhini, AC Milan na juyayin mutuwar mutumin da ba za a taɓa mantawa da shi ba wato Silvio Berlusconi, muna kuma fatan isar da saƙon ta'aziyya ga iyalai da abokan hulɗa da sauran makusantansa."

    Tsohon firaministan Italiyan ya koma harkar ƙwallon ƙafa ne a 2018, ƙasa da wata 18 bayan kamfaninsa, Fininvest, ya saye hannayen jari kashi 100% na ƙungiyar ƙwallo ta Monza da ke taka leda a rukuni na uku.

  9. Ɗan gayen ɗan siyasa da ya saba sauka daga mulki yana komawa a Italiya

  10. 'Yan sanda na fuskantar shari'a saboda mutuwar ɗan Najeriya a Switzerland

    'Yan sanda shida ne ake gurfanarwa a gaban shari'a a ƙasar Switzerland a kan tuhume-tuhumen aikata kisa ga wani ɗan Najeriya ba da gangan ba shekara biyar da ta wuce.

    Mike Ben Peter ya rasu ne bayan an kama shi a birnin Lausanne.

    'Yan sanda sun ce sun yi amfani da tsarin da aka saba amfani da shi wajen kama mutumin da ake zargi da dillancin ƙwaya.

    Jami'an tsaron sun tokare shi a ƙasa bayan ya ƙi yarda a bincika shi.

    Lauyoyin waɗanda ake ƙara za su tafka muhawarar cewa mutuwar Mike Ben Peter mai yiwuwa ne ta faru sanadin kwantattun cutuka da yake fama da su.

    Iyalan mamacin da kuma ƙungiyoyin yaƙi da wariyar launin fata a Switzerland sun kwatanta abin da ya faru da mutuwar George Floyd, wanda 'yan sanda suka kashe a jihar Minneapolis ta Amurka.

  11. Saudiyya da Amurka sun yi alla-wadai da ci gaba da faɗa a Sudan

    Amurka da Saudiyya sun yi alla-wadai da komawa rikicin da ɓangarorin da ke gaba da juna suka yi a Khartoum, babban birnin ƙasar Sudan.

    Mazauna birnin dai sun bayyana cewa ana ci gaba da kai hare-hare ta sama da kuma musayar wuta.

    Cikin wata sanarwar haɗin gwiwa, ƙasashen biyu sun lura cewa sojojin Sudan da dakarun RSF, dukkansu na iko da sojojinsa duk da yarjejeniyar tsagaita wuta ta tsawon sa'a 24 da aka cimma.

    Wata ƙungiya mai rajin kare dimokraɗiyya ta ce hare-hare da ɓangarorin biyu ke kai wa a kudancin birnin na faɗawa a kan gidajen jama'a.

    Shi ma wani mazaunin birnin, wanda ya farka daga barci sanadin ɓarkewar faɗa ya ce lafawar ƙura da aka samu na tsawon kwana ɗaya ranar Asabar tamkar wani mafarki ne da a yanzu ya ɓace.

  12. Tsohon firaministan Italiya Berlusconi ya mutu

    Tsohon Firaministan Italiya, Silvio Berlusconi wanda ya fuskanci zarge-zargen cin hanci da rashawa ya rasu ya nada shekaru 86 a duniya.

    Ya mutu ne a asibitin San Raffaele da ke birnin Milan.

    A cikin watan Afrilu, Berlusconi ya yi fama da ciwon huhu.

    Attajirin kuma dan gaye, ya soma jagorantar Italiya ne a shekarar 1994, sannan kuma ya ci gaba da jan zarensa a lokuta daban-daban har zuwa shekara ta 2011.

    Berlusconi ya jagoranci jam'iyyar Forzia Italia wajen shiga gwamnatin hadin gwiwa inda daga bisani aka zabe shi a matsayin dan majalisar dattijai a watan Satumbar bara.

  13. Na san ƙuncin da janye tallafin mai ya jefa ku - Tinubu

  14. Ukraine na murnar samun galabar farko a kan Rasha

    Ukraine ta sanar da samun nasarar farko a kan hare-haren mayar da martani da take kai wa dakarun Rasha wadanda suka sake kwace wasu kauyuka uku a yammacin yankin Donetsk.

    Wasu hotuna da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda dakarun Ukraine ke murna a wasu kauyuka biyu da suka kwace.

    Ɗaya daga cikin sojojin Ukraine ɗin ya bayyana cewa; "Mun fatattaki maƙiyanmu daga yankinmu. Wannan wani abin jin dadi da alfahari ne",

    "Ukraine za ta yi nasara", in ji shi.

    Mataimakiyar ministan tsaron Ukraine, Hanna Malyar, ta ce an ƙwace ƙauyen Makarivka da ke makwabtaka da kauyukan da sojojin nasu suka kwace.

    Ta kara da cewa, sojojin nasu na ci gaba da lugudan wuta a arewaci da kuma kudancin Bakhmut.

  15. Jama'a, barkanmu safiya

    Masu bibiyar wannan shafin labarai kai tsaye na BBC Hausa, barkanmu da sake kasancewa. Wannan shafi zai kawo muku labarai da rahotanni da abubuwan da ke faruwa a Njaeriya da ma sauran sassan duniya

    Mukhtari Adamu Bawa ne ke muku sallama a yau Litinin.

    Ku ci gaba da bibiyarmu don sanin halin da dunbiya take ciki daga yanzu haru zuwa dare.