A karon farko a tarihin Tanzaniya, shugabar ƙasan Samia Suluhu Hassan, ta halarci taron ranar mata ta duniya da babbar jam'iyyar adawa ta Chadema ta shirya.
Shugaban jam'iyyar Freeman Mbowe ya yi maraba da halartar shugaba Samia Suluhu, inda ya ce buƙatar taron ne ganin an yi sulhu tsakaninsu.
Samia, wadda ta yi jawabi ga dubban mutane a wurin taron, ta ce ana ci gaba da sasantawa a siyasar ƙasa, kuma tuni aka ɗauki wasu matakai yayin da wasu kuma ke ci gaba da gudana, ciki har da samar da sabon kundin tsarin mulki.
A cikin jawabinta, shugaba Samia ta ce an fuskanci matsala kafin fara sulhuntawa saboda wasu a jam'iyyarta mai mulki ba su shirya ba.
Ta ce, "An yi muhawara da yawa a nan da can, kuma hakan ya bayyana ga 'yan adawar ƙasar. Don haka jam'iyyun biyu suna da wasu daga cikin jama'arta da ba su ji daɗin matakin sulhuntawa na siyasa ba."
Ita ce shugabar mata ta farko a Tanzaniya, bayan rasuwar John Magufuli a shekarar 2021.
'Yan adawar sun zargi mista Magufuli da zama mai son mulki, da taka shugabanni da kuma mambobinsu.