Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abba Kyari: Shugabannin duniya sun yi wa Buhari ta’aziyya

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. Rufewa

    A nan za mu dakatar da kawo maku labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a duniya musamman kan annobar cutar corona.

    Da fatan za ku kasance da mu gobe Insha Allah inda za mu ci gaba da kawo maku rahotanni kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa daga sassan duniya.

    ku kasance da mu.

  2. Ana zanga-zangar adawa da hana fita a Amurka

    Ana ci gaba da gudanar da zanga-zanga a wasu biranen Amurka domin adawa da matakan hana fita da hukumomi suka dauka.

    Mutane sama da dari biyu da hamsin ne suka hada gangami a Austin da Texas suna neman a bude harakokin kasuwanci. Haka ma a New Hampshire da Maryland. Masu zanga-zangar sun yi kiran a tube Anthony Fauci daga mukaminsa, daya daga cikin shugabannin tawagar da ke jagorantar yaki da bazuwar cutar korona.

    Ana dai ganin ya yi wuri a dage dokar hana fita, inda ake fargabar kara yaduwar cutar a Amurka bayan cutar ta kashe dubban mutane

  3. Cutar korona: Wadanda suka mutu a Spain sun haura 20,000

    Adadin wadanda suka mutu a Spain sun haura mutum 20,000 zuwa ranar Asabar, kamar yadda hukumomin lafiyar kasar suka bayyana.

    Yanzu adadin mutum 20,043 cutar korona ta kashe a Spain, kuma 565 sun mutu ne cikin sa’a 24.

  4. Kasashen Opec sun kadu da mutuwar Abba Kyari

    Kungiyar kasashe masu arzikin man fetir ta jajantawa shugaban Najeriya Muhammadu Buhari kan rasuwar shugaban ma’aikatan fadarsa Malam Abba Kyari.

    Cikin wata Sanarwar mai dauke da sa hannun babban sakataren kungiyar Muhammad Sanusi Barkindo wanda dan Najeriya ne, ya ce ya kadu matuka da ya samu labarin rasuwar Abba Kyari.

    Ya bayyana Abba Kyari a matsayin jajirtaccen ma’aikaci, kuma mai biyayya.

    Barkindo ya ce: “A madadin kungiyar kasashe masu arzikin man fetir Opec, muna mika sakon ta’aziyarmu ga shugaban kasa, da iyalansa da dukkanin‘yan kasarmu Najeriya.

  5. Shugabannin duniya sun min ta’aziyar rasuwar Abba Kyari – Buhari

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ya samu sakwanni da dama na ta’aziya daga shugabannin kasashen duniya kan rasuwar Abba Kyari, shugaban ma’aikata a fadarsa.

    Sanarwar da mai Magana da yawun shugaban ya fitar Malam Garba Shehu, ta ce shugaba Nana Akuffo-Ado na Ghana da Muhammadou Youssoufou na Nijar sun kira shugaban ta wayar tarho.

    Ya kuma amsa kira daga tsohon shugaban Benin Boni Yayi da kuma tsoffin shugabannin kasashen Najeriya guda biyu Janar Yakubu Gowon da Janar Abdulsalami Abubakar da kuma Sarkin Musulmi Dr. Sa’ad Abubakar 111 da kuma shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya Rev. Samson Ayokunle da kuma Aliko Dangote attajirin Afirka.

    Kasashen Chadi da Masar da Liberia dukkaninsu sun jajantawa shugaban daga sakwannin da ofisoshin jekadancinsu suka aiko.

    Sauran wadanda suka jajantawa shugaban a cikin Najeriya sun hada da gwamnoni da Sarakuna da ministocinsa da ‘yan Majalisar tarayya.

  6. Najeriya ta yi babban rashi - Dangote

    Attajirin Afirka Aliko Dangote ya jajantawa Iyalan Abba Kyari da Shugaba Buhari da kuma 'yan Najeriya kan rasuwar shugaban ma'aikata a fadar shugaban kasa.

    Dangote wanda ya wallafa sakon alhinin a Twitter ya ce Najeriya ta yi babban rashin kwararre wanda ya kira bai basira.

  7. Cutar Korona: Mutum daya ya warke a Bauchi

    Gwamnatin jihar Bauchi ta ce an sallami mutum daya bayan gwaji ya tabbatar da ya warke daga cutar korona.

    Gwamnan jihar Sanata Bala Mohammed ya wallafa a Twitter cewa cikin mutum biyu da aka killace, dayansu yanzu ya warke kuma an sallame shi.

  8. Labarai da dumi-dumi, Ganduje ya tube Kwamishinan da ya yi murnar rasuwar Abba Kyari

    Gwamnan Kano Umar Abdullahi Ganguje ya tube kwamishinansa na ayyuka Engr. Mu’azu Magaji bayan wasu kalamansa da suka nuna yana murnar rasuwar Abba Kyari.

    A sakon da kwamishinan ya wallafa a Facebook, Injiniya Muazu, ya bayyana cewa "nasara, nasara. Najeriya ta tsira, Abba Kyari ya mutu a cikin annoba."

    Wadannan kalamai sun janyo masa kakkausan suka daga mabiyansa a shafin Facebook, inda wasu suke cewa bai kamata mai mukami kamar sa ya yi kalamai irin wadannan ba.

    Wata sanarwa da kwamishinan watsa labarai na jihar Kano Malam Muhammad Garba ya fitar ya ce an tube kwamishinan ne bayan kalaman nasa, wandanda ya ce bai kiyaye ba.

    Sanarwar tube kwamishinan ta ce, "ya kamata a matsayinsa na kwamishina ya mutunta ofishinsa na kaucewa aikata duk wani abin da zai ci mutuncin ofishin.

  9. Gwamnan Gombe ya yi ta'aziyyar Abba Kyari

    Gwamnan Jihar Gombe Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana alhinin rasuwar Mallam Abba Kyari Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Kasa, wanda ya mutu ranar Juma'a.

    Gwamna Yahaya ya ce Najeriya Najeriya "ta yi rashin jajirtacce mutumin kirki kuma dan kishin kasa, wanda a koyaushe yake ankare a kan aikinsa", a wata sanarawa da Ismaila Uba Misilli, mai magana da yawunsa ya fitar.

    Ya kara da cewa za a tuna da Abba Kyari ne da irin salon shugabancinsa da kuma jajircewarsa yayin gudanar da ayyukan da suka shafi ofis dinsa.

    Tuni aka yi jana'izar Abba Kyari a Makabartar Gudu da ke Abuja a yau Asabar, bayan an kai gawarsa daga Jihar Legas inda ya yi jinyar cutar korona.

    "A madadin gwamnati da jama'ar Jihar Gombe, ina so na mika ta'aziyyata ga Shugaba Muhammadu Buhari da iyalan marigayin tare da gwamnati da jama'ar Jiharsa ta Borno bisa wannan babban rashi," in ji Muhammadu Inuwa Yahaya.

  10. Yadda aka yi Jana'izar Abba Kyari

  11. Abba Kyari: Kalaman Kwamishinan Ganduje sun jawo takaddama

    Wasu kalamai da Kwamishinan ayyuka na jihar Kano, Injiniya Muazu Magaji ya yi wadanda ake gani tamkar na nuna murna ne kan rasuwar Abba Kyari, shugaban ma'aikatan fadar shugaban Najeriya, sun jawo takaddama.

    A sakon da ya wallafa a Facebook, Injiniya Muazu, ya bayyana cewa "nasara, nasara. Najeriya ta tsira, Abba Kyari ya mutu a cikin annoba."

    Wadannan kalamai sun janyo masa kakkausan suka daga mabiyansa a shafin Facebook, inda wasu suke cewa bai kamata mai mukami kamar sa ya yi kalamai irin wadannan ba.

    Da alama shi ma Malam Bashir Ahmad, mai bai wa shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya shawara kan shafukan sada zumunta na zamani, bai ji dadin kalaman ba.

    A sakon da ya wallafa a Twitter ranar Asabar, ya yi kira ga Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya dauki mataki kan wani kwamishinansa.

    Bashir Ahmad ya ce ya yi matukar rashin jin dadi bisa murnar da kwamishinan ayyuka na Kano, Injiniya Muazu Magaji ya yi.

    Malam Abba Kyari ya rasu ne ranar Juma'a bayan ya yi fama da cutar korona.

  12. 'Babu zaman makokin Abba Kyari’

    Fadar shugaban Najeriya ta ce babu zuwa yin gaisuwar ta'aziya ga iyalan Marigayi Abba Kyari da kuma fadar shugaban kasa.

    Sanarwa da kakakin shugaba Buhari, Garba Shehu ya fitar ta ce an yi jana’izarsa bisa bin umurnin kariya da hukumomin kasar suka gindaya kuma babu zaman makoki ko kuma zuwa ta’aziyya ga fadar shugaban kasar.

    Sanarwar ta bukaci jama’a a maimakon kokarin zuwa yin gaisuwa, su yi wa mamacin addu’a - Allah Ya jikansa da rahama.

    Ta bayyana cewa an birne Malam Abba Kyari a makabartar Gudu da ke Abuja bayan gawarsa ta iso daga Lagos a safiyar ranar Asabar.

    A ranar Lahadi za a bude rijistar rubuta ta’aziyyar Malam Abba Kyari a ofishin sakataren gwamnatin tarrayar Najeriya.

  13. PDP 'tana bakin ciki game da rasuwar Abba Kari'

    Babbar jam'iyyar hamayya a Najeriya, PDP, ta mika ta'aziyya ga shugaban kasar Muhammadu Buhari bisa rasuwar shugaban ma'aikatansa, Malam Abba Kyari.

    PDP, a sakon da mai magana da yawunta Kola Ologbondiyan ya sanya wa hannu ranar Asabar, ta bayyana mutuwarsa a matsayin "abin bakin ciki da takaici."

    "Jam'iyyar PDP tana mai hakurkurtar da Shugaba Muhammadu Buhari, iyalin Abba Kyari, gwamnati da kuma al'ummar jihar Borno, da ma kasa baki daya bisa wannan rashi mai zafi sannan tana addu'ar Allah ya jikan Mallam Abba Kyari," in ji kakakin jam'iyyar.

  14. Me Aisha Buhari ta ce kan rasuwar Abba Kyari?

    Mai dakin shugaban Najeriya, Aisha Buhari, ta bi sahun 'yan Najeriya wajen mika ta'aziyya bisa rasuwar shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Malam Abba yari.

    "Daga Allah muke kuma gare shi za mu koma. Ina mika ta'aziyya ga matar Abba Kyari, Kulu, da dukkan iyalan marigayi Malam Abba Kyari bisa rasuwar mjinta kuma mahaifin 'ya'yanta," in ji Aisha Buhari a sakon da ta wallafa a Twitter ranar Asabar.

    Malam Abba Kyari ya rasu raanr Juma'a bayan ya yi fama da cutar korona.

  15. Covid-19:Karin mutum uku sun mutu a Lagos

    Gwamnatin jihar Lagos da ke kudu mas yammacin Najeriya ta ce karin mutum uku sun muta sakamakon cutar korona a jihar.

    Kwamishinan Lafiya na jihar, Farfesa Akin Abayomi ne ya bayyana haka a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Asabar.

    A cewarsa, yanzu jumullar mutanen da suka mutu ta kai 13.

    Ya kara da cewa an samu sabbin masu dauke da cutar korona guda 32, yanzu kenan adadin masu fama da cutar a jihar ya kai 286.

  16. Ina sa ran Abba Kyari ya yi shahada – Sheikh Isa Pantami

    Sheik Isa Ali Pantami ya ce babu abin da ya kamata mutane su yi illa su yi wa Malam Abba Kyari addu'a saboda yanayin halin da ake ciki na annobar cutar korona, yana mai cewa ba sai an je zaman makoki ba.

    Pantami wanda ya jagoranci addu'a a wurin bimne Abba Kyari, ya ce ana kyautata zaton Abba ya yi shahada.

    "Manzon Allah S.A.W. ya ce yana daga cikin kyakkyawan karshe mutum ya mutu ranar Juma'a sannan wanda annoba ta kashe shi yana mai imani shi ma dan Aljanna ne," in ji Pantami.

    Ya kara da cewa saboda kiran da kwararru suka yi na bayar da tazara, ya kamata kowa ya tafi harkokinsa bayan binne shi.

    "Daga nan wurin an sallami kowa, ba sai an je wurin karbar gaisuwa ba saboda da ma karbar gaisuwa din al'ada ne."

    An binne Malam Abba Kyari ne a makabartar yankin Gudu da ke Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja bayan an kai gawarsa daga Jihar Legas, inda ya mutu bayan jinyar cutar korona.

  17. An yi jana'izar Abba Kyari

    An binne gawar Malam Abba Kyari a makabartar Gudu da ke Abuja, Birnin Tarayyar Najeriya.

    Da ma gwamnatin Najeriya ta ce ba za a yi taro ba a wurin jana'izar tasa.

    Sai dai kamar yadda kuke gani mutanen da suka halarci binne shi suna da dan yawa sannan kuma babu maganar bayar da tazara.

  18. Za a bude kasuwanni a Jihar Ogun

    Gwamnatin Jihar Ogun za ta bude kasuwanni a jihar a ranakun Litinin da Laraba da Juma'a domin bai wa jama'a damar sayen kayan masarufi daga karfe 7:00 na safe zuwa 2:00 na rana.

    Gwamnan jihar Dapo Abiodun ne ya bayyana hakan a ranar Juma'a a wani taron manema labarai da ya gudanar, inda ya ce hakan ya biyo bayan tsawaita dokar hana fita ne da gwamnatin tarayya ta yi da tsawon mako biyu.

    Ya ce hakan yana nufin mazauna jihar za su ci gaba da kasancewa a kulle a ranakun Asabar 18 ga watan Fabarairu, da Lahadi 19 ga wata, da Talata 21 ga wata da Alhamis 23 ga wata.

    Jihar Ogun tana cikin jihohi uku da Shugaba Muhammadu Buhari ya sanya dokar hana fita ta mako biyu a ranar 29 ga watan Maris sannan ya tsawaita ta da wasu mako biyu a ranar 13 ga watan Afrilu.

    Ya zuwa yanzu Ogun ta tabbatar da mutum 10 da suka kamu da cutar korona a jihar.

  19. Labarai da dumi-dumi, Gawar Abba Kyari ta isa Abuja

    Mai magana da yawun Shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya ce gawar marigayi Abba Kyari ta isa birnin Abuja.

    Garba Shehu ya ce za a yi jana'izar ne a cikin sirri bisa sharuddan hukumar NCDC mai yaki da yaduwar cutuka a Najeriya da kuma Ma'aikatar Lafiya.

    "Saboda haka babu taron jana'iza. Ana bukatar 'yan uwa da abokan arziiki da kuma sauran jama'a su yi masa addua'a," in ji Garba Shehu.

  20. Goodluck Jonathan ya mika ta'aziyyar rasuwar Abba Kyari

    Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Ebele Jonathan ya mika ta'aziyyar rasuwar Malam Abba Kyari ga iyalansa da Shugaba Buhari da kuma sauran 'yan Najeriya.

    Jonathan ya ce: "Allah ya saka shi a Aljannah Firdaus kuma ya bai wa iyalansa da abokansa hakurin rashinsa a wannan lokaci na alhini.

    Cutar korona ce ta yi ajalin Malam Abba Kyari a daren Juma'a, wanda kafin mutuwarsa shi ne Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Najeriya.

    Ya rasu ne a Jihar Legas, inda ya yi jinyar cutar.