Karanta bayanai game da rayuwar mutumin da ya mamaye siyasar Zimbabwe tun lokacin da ta samu 'yancin kai a shekarar 1980.
An haife shi a shekarar 1924
Ya yi aki a Ghana inda ya hadu da matarsa ta farko Sally Hafron
1964: Gwamnatin Rhodesian ta daure shi
1980: Ya lashe zaben bayan 'yancin kai
1996: Ya auri Grace Marufu
2000: Ya sha kaye a zaben raba gardama kan ikon shugaban kasa da kuma filaye mallakar fararen fata
2008: Ya zo na biyu bayan Morgan Tsvangirai a zagaye na farko na zaben shugaban kasa, amman madugun 'yan adawar ya janye daga zaben da aka yi a zagaye na biyu yayin da ake kai hare-hare kan magoya bayansa
2009: Ya rantsar da Tsvangirai a matsayin Firayim minista a lokacin da kasar take fuskantar tabarbarewar tattalin azriki
2016: Ya gabatar da takardun lamuni yayin da karancin kudade ya yi kamari
2017: Ya kori amininsa wanda suka dade tare, mataimakin shugaban kasa Emmerson Mnangagwa