Zaben Malaysia: Mai shekara 92 ya lashe zaben shugaban kasa

Former Malaysian PM and opposition candidate Mahathir Mohamad celebrates with other leaders of his coalition in Kuala Lumpur on early May 10, 2018

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Mista Mahathir na sa ran a gudanar da bikin rantsar da shi ranar Alhamis

Tsohon firai ministan Malaysia, Mahathir Mohamad mai shekaru 92 ya bada mamaki bayan ya kayar da jam'iyyar da ta mulki kasar na tsawon shekara 60 a zaben shugabancin kasar.

Hukumar zaben kasar ta ce hadakar jam'iyyun siyasa na Mista Mahathir sun lashe kujeru 115, wanda ya zarce 112 da suke bukata domin kafa gwamnati.

Mista Mahathir mai shekara 92 ya kada jam'iyya mai mulki ta Barisan Nasional wadda ta shafe fiye da shekara 60 tana kan mulki.

Ya dade da yin ritaya, amma saboda zaben ya dawo domin karawa da tsohon yaronsa a siyasa, Najib Razak.

"Ba mun zo ramuwa ba ne, so muke mu dawo da doka da oda," inji Mista Mahathir.

Karanta karin wasu labaran

Ya kuma ce yana fatan za a gudanar da bikin rantsar da shi ranar Alhamis, wanda zai mayar da shi shugaban kasa mafi yawan shekaru a duniya.

Saboda wannan nasarar, an bayyana ranakun Alhamis da Jumma'a a matsayin hutu a fadin kasar.

Supporters of Mahathir Mohamad celebrate in Kuala Lumpur on early May 10, 2018

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Magoya bayan Mista Mahathir sun fita titunan birnin Kuala Lumpur domin nuna murnarsu

Wannan yakin neman zaben ya hada Mista Mahathir da tsohon yaronsa na siyasa, wato firayi minista mai ci Najib Razak.

Mahathir (C) and Najib (L) stand at an UMNO annual general assembly meeting in 2009

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Hoton Mista Najib (hagu) wanda tsohon yaro ne na siyasa ga Mista Mahathir (wanda ke tsakiya)