Arsenal ta ƙwallafa rai kan Lukeba, Liverpool da Man U na rige-rigen ɗaukar Mane

Asalin hoton, Getty Images
Liverpool ce kan gaba a fafatawar da ake yi tsakanin kungiyar da Manchester City da Arsenal wajen neman tsohon dan wasan gefe na Everton Anthony Gordon, mai shekaru 24 wanda ke taka leda a Newcastle United inda ya je aro, amma farashin dan wasan na Ingila zai kan fam miliyan 95. (Caughtoffside)
Wannan na faruwa ne yayin da Mohamed Salah, mai shekaru 33, ke shirin barin Liverpool a karshen kakar wasan nan, inda kungiyoyi a Masar da Saudiyya ke nemansa. (Teamtalk)
Har wayau Liverpool din na kuma fafatawa da Manchester United, wajen kokarin daukar dan wasan gaba na Wolves Mateus Mane mai shekaru 18 a wannan bazarar. An kiyasta farashin Matashin dan wasan na Ingila wanda aka haifa a Portugal da fam miliyan 50. (Fichajes)
Tottenham ta ƙi amincewa da bukatar Aston Villa da Chelsea ta neman ɗan wasan tsakiyarta dan asalin Sweden Lucas Bergvall, mai shekaru 20. (Athletic)
Kocin Arsenal Mikel Arteta ya ƙuduri aniyar siyan ɗan wasan tsakiya na Faransa Castello Lukeba, mai shekaru 23, daga RB Leipzig, inda ƙungiyar ta Jamus ta shirya sayar da shi kan fam miliyan 52.1. (Sports Boom)
Har wayau Arsenal din na neman ɗan wasan gefe na RB Leipzig mai shekaru 20, Antonio Nusa, wanda aka kimanta tsakanin Yuro miliyan 50-60 (£43m-£52m). (Fussball Daten)
Masu sa ido a kan 'yan wasan Manchester United sun je San Siro ranar Asabar don kallon Federico Dimarco na Inter Milan mai shekaru 28, dan wasan gefe na Italiya da kuma Pierre Kalulu na tsakiya na Faransa, mai shekaru 25, daga Juventus. (Calciomercato)
Har yanzu Enzo Maresca ne kan gaba, a jerin kwaca-kwacan da ake kyautata zaton za su maye gurbin Pep Guardiola idan ya tashi daga Manchester City (Fabrizio Romano)










