Ra'ayoyin jama'ar Kano kan kirkiro sabbin masarautu

Latsa alamar hoton da ke sama domin kallon wannan bidiyon

Wasu daga cikin mazauna jihar Kano sun bayyana ra'ayoyinsu dangane da sabbin masarautun da aka kirkiro a jihar Kano.

A ranar Laraba ne Gwamna Ganduje ya sanya hannu kan dokar da majalisar dokokin jihar ta yi a ranar Litinin, ta neman kara yawan marautun jihar.

Lamarin dai ya janyo ce-ce ku-ce a tsakanin al'ummar kasar baki daya ba ma na Kano ba kawai.