Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Kahutu Rarara: 'Abin da ya sa na yi wakar 'Ta leko ta labe'
Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon hirarmu da Rarara.
Fitaccen mawakin siyasar nan a Najeriya, Dauda Kahutu Rarara, ya bayyana farin cikinsa bisa nasarar da dan takarar jam'iyyar APC a Kano Abdullahi Umar Ganduje ya samu na lashe zaben jihar.
A hirar da BBC ta yi da mawakin, ya yi bayani kan wasu kalamai da ya yi amfani da su a wakokinsa da ya yi wa Gwamna Ganduje.