Jami'an tsaro sun kai samame a gidan tsohon gwamna Bello Matawalle

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtan ƙasashe

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Mukhtar Adamu Bawa and Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Ganduje ya ƙai ƙarar gwamnan Kano wurin Tinubu kan rusau - Ganduje

    ...

    Tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya ce ya bayyana wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu halin da ake ciki kan maganar rushe-rushe a jihar Kano.

    Ya kuma ce ya miƙa koke kan lamarin ga sifeta-janar na ƴan sandan ƙasar domin ganin an ɗauki mataki.

    Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin ganawa da manema labaru bayan wata tattaunawa da shugaba Bola Ahmed Tinubu.

    Ya bayyana abin da gwamnatin sabon gwamnan jihar Kano, Abba Kabir ke yi ta hanyar rushe gine-gine da abin da ya saɓa wa doka.

    Ya kuma nuna matuƙar ɓacin ransa ga tsohon gwamnan jihar Rabi'u Musa Kwankwaso inda ya yi barazanar marin sa.

    Ya ce "inda na haɗu da shi da na mare shi.

    Dangantaka dai ta yi matuƙar tsami tsakanin Ganduje da Kwankwaso tun bayan da suka raba gari a shekarun baya bisa saɓanin fahimta.

    Tun bayan kama aiki, gwamna Abba Kabir ya bayar da umurnin rushe wasu gine-gine waɗanda ya zargi tsohuwar gwamnatin ta Abdullahi Ganduje da assasawa ba bisa ƙa'ida ba.

  2. Ƴan sanda sun gano motoci sama da 40 a gidan Matawalle - Gwamnatin Zamfara

    ...

    Asalin hoton, Twitter/BelloMatawalle1

    Gwamnatin jihar Zamfara ta ce jami'an ƴan sanda waɗanda suka kai samame a gidan tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle sun gano motoci fiye da 40.

    Hakan na zuwa ne bayan da rahotanni suka bayyana cewa jami'an tsaro sun yi dirar mikiya a gidajen tsohon gwamnan da ke Gusau, babban birnin jihar da kuma a Maradun.

    Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta hannun mai taimaka wa gwamnan, Dauda Lawal kan harkar yaɗa labaru, Sulaiman Bala Idris, ta ce an kai samamem ne bayan samun izini daga kotu.

    Idan za a iya tunawa, gwamnatin jihar ta zargi Bello Matawalle da tafiya da wasu kayan gwamnati, ciki har da motocin alfarma na gwamnati bayan saukar sa daga mulki.

    Tuni dai tsohon gwamnan ya musanta zarge-zargen.

    Sanarwar da gwamnatin ta fitar ta ƙara da cewa cikin motocin da aka gano daga gidan tsohon gwamnan akwai motoci masu sulke guda uku da kuma manyan motoci na SUV guda takwas.

    An dai fara takun-saƙa tsakanin toshon gwamna Bello Matawalle da sabon gwamna Dauda Lawal ne tun gabanin miƙa mulki.

    Dauda Lawal na jam'iyyar PDP shi ne ya kayar da Bello Matawalle na APC a zaɓen gwamna da ya gabata, inda adawa ta yi matuƙar zafi.

  3. An kashe sojan wanzar da zaman lafiya na majalisar dinkin duniya a Mali

    ...

    An kashe akalla sojan wanzar da zaman lafiya na majalisar dinkin duniya daya a wani hari da aka kai a arewacin kasar Mali, yayin da Wasu hudu suka jikkata.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce dakarun sun fara karo da wani abin fashewa kafin aka bude masu wuta.

    An kai harin ne a garin Ber, a yankin Tombouctou da aka shafe fiye da shekaru goma ana artabu da masu jihadi wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane.

    Majalisar dinkin duniya ta girke dakarun wanzar da zaman lafiya kusan 12,000 a arewacin kasar Mali, domin tunkarar 'yan ta'adda. an kashe kusan guda 300 daga cikin su.

    Kimanin mutane miliyan shida ne suka rasa matsuguni sakamakon rikicin.

  4. Ƴan bindiga sun hallaka mutane 10 da gatari a Kongo

    ...

    Wasu da ake zargin masu da'awar jihadi ne sun kashe akalla mutum 10 a gabashin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo.

    Rahotannin cikin gida sun ce mutanen sun yi amfani da gatari da adduna wajen kai wa fararen hula hari a gidajensu a kauyen Bukokoma da ke lardin Nord Kivu a yammacin ranar Alhamis.

    Ana tunanin cewa maharan sun fito ne daga kungiyar Allied Democratic Forces (ADF), da ke da alaka da kungiyar IS.

    Gabashin ƙasar DR Congo, ya kasance wuri ne da ke fama da ‘yan tawaye da ake zargi da kai hare-haren da suka kashe dubban mutane.

    Wani hari makamancin wannan a makon da ya gabata a yankin Beni ya yi sanadin mutuwar akalla mutane tara.

  5. Jami'an tsaro sun kai samame a gidajen tsohon gwamna Bello Matawalle

    ...

    Asalin hoton, UGC

    Ƴan sanda sun kai samame a gidan tsohon gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle, wanda ba shi da nisa da gidan gwamnati a Gusau, babban birnin jihar.

    A wata tattaunawa da BBC, tsohon daraktan yaɗa labaru na tsohon gwamnan, Yusuf Idris ya ce lamarin ya faru ne a yau Juma'a.

    Wannan samame dai na zuwa ne 'yan kwanaki bayan gwamnan jihar Dauda Lawal Dare ya zargi Matawalle da wasu jami'an gwamnatinsa da yin sama da fadi da wasu kayayyakin gwamnatin jihar.

    Gwamnan ya kuma zargi Matawalle da yin awon gaba da motocin da ke gidan gwamnati kafin ya mika masa shugabancin jihar.

    Da take tabbatar da afkuwan lamarin jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara, a wata sanarwa da ta fitar, ta yi Allah-wadai da afkawa da kuma ɓarnatar kayan gidajen tsohon gwamnan jihar, da rundunar ‘yan sandan a jihar ta Zamfara da jami'an DSS suka yi a Gusau da Maradun, tana ikirarin cewa babban cin zarafi ne kuma ya saɓa wa kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na 1999.

    Sanarwar ta ci gaba da cewa jam'iyyar na kira ga rundunar ‘yan sandan Najeriya da na DSS da su gaggauta daukar kwararan matakai don yakar wannan barna da gwamnatin jihar Zamfara ke yi, kuma dole ne a gano wadanda suka gudanar da wannan aikin domin su fuskancihukunci.

    ''Muna kira ga Sufeto Janar na ‘yan sanda da ya bayar da umarnin gudanar da bincike cikin gaggawa tare da hukunta wadanda suka aikata wannan abu ta haramtacciyar hanya ta kutsawa gidajen shugaban jam’iyyar APC na Jihar Zamfara.'' In ji sanarwar.

  6. A bai wa gwamnati lokaci kan cire tallafin man fetur - Sarkin Kano

  7. Ɓangarorin da ke gwabza faɗa a Sudan sun amince da tsagaita wuta na kwana guda

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Saudiyya ta sanar da cewa ɓangarori biyu da ke fada a Sudan sun bayyana aniyarsu ta tsagaita wuta na kwana guda.

    Ma'aikatar harkokin waje ta Saudiyya ta ce tuni ɓangarorin biyu suka amince da batun.

    Tsagaita wutar za ta fara aiki ne daga ƙarfe 05:00 na safiya, agogon GMT.

    Saudiyya da Amurka na ta ƙoƙarin ganin sun sasanta tsakanin ɓangarorin biyu tun bayan da faɗa ya ɓarke a watan Afrilu.

    Saudiyyar ta yi barazanar cewa za ta dakatar da duk wani yunkuri na sulhu matuƙar aka gaza tsagaita wutar ƙarƙashin wannan yarjejeniya.

    Ɓangarorin biyu dai sun yi watsi da wani yunƙurin da aka yi a baya.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙiyasta cewa kimanin mutum miliyan 1.5 ne rikicin ya tursasa musu tserewa daga gida tun bayan ɓarkewar faɗan.

  8. An ceto jariran da rikicin Sudan ya ritsa da su a gidan marayu

  9. Gwamnatin Senegal ta hana 'yan adawa yin zanga-zanga

    Senegal

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamantin Senegal ta hana 'yan adawar kasar yin zanga-zangar da suka shirya sakamakon arangamar 'yan sanda da masu zanga-zanga a satin da ya gabata.

    Lamarin ya faru ne sakamakon hukuncin zaman gidan gyaran hali da kotu ta yanke wa jagoran 'yan adawar kasar Ousmane Sonko, wanda aka samu da laifin kokarin cin zarafin wata matashiya.

    Sanko ya musanta dukkan zarge-zargen da aka yi masa, ya kuma ce hukuncin wata maarashiya ce aka shirya masa domin Shugaba Macky Sall ya hana shi takarar shugabancin kasar a zabe mai zuwa.

    Kungiyar kare hakkin ta Amnesty International ta ce mutum 23 aka kashe a rikicin makon da ya gabata, adadin da ya zarta wanda gwamnati ta bayyana na mutum 16.

  10. Tinubu ya gana da sarakuna a Abuja

    Tinubu

    Asalin hoton, State House

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi ganawar sirri da manyan sarakunan gargajiya daga kowane bangare na kasar.
    Tinubu

    Asalin hoton, State House

    Bayanan hoto, Taron wanda aka yi a yau Juma'a, ya gudana ne a Fadar Shugaban Najeriya.
    Tinubu

    Asalin hoton, State House

    Bayanan hoto, Duk da cewa babu cikakken bayani kan abin da suka tattauna, fadar shugaban na cewa ganawar wani ɓangare ne na tattaunawa da neman shawarwari a ƙasa baki ɗaya.
    Tiubu

    Asalin hoton, State House

    Bayanan hoto, Sarkin Musulmi Abubakar Sa'ad III ne ya jagoranci sarakunan zuwa fadar, inda suka nemi Tinubu ya yi amfani da su wajen shawo kan matsalolin tasro da suka addabi ƙasar, kamar yadda Channels TV ta ruwaito.
  11. Kifi ya halaka mutum a Masar

    Kifi

    Asalin hoton, AFP

    Wani shirgegen kifi ya kashe wani ɗan Rasha a kusa da wurin shaƙatawa na Hurghada da ke gaɓar Tekun Maliya a Masar.

    Mutumin ya gamu da ajalinsa ne da tsakar ranar Alhamis, a cewar hukumomin Rasha da Masar, yayin da yake ninƙaya a ruwan.

    Wani da abin ya faru a kan idonsa ya naɗe shi a bidiyo kuma ya bai wa kamfanin labarai na Reuters.

    Bidiyon ya nuna matashi mai shekara 20 da 'yan-kai yana dirango a ruwa kafin daga baya a janye shi zuwa ƙasan ruwa.

    A cewar Reuters, wani mai ninƙaya ya bayyana yadda wani mai aiki a wurin ya yi yekuwa a wani otel da ke kusa kuma mutane suka yunƙuro don ceto shi, amma ba su iya kaiwa gare shi a kan lokaci ba.

    Yanzu dai an hana ninƙaya da sauran harkokin wasanni a wurin na kwana biyu daga yau Juma'a, kamar yadda ma'aikatar kula da muhalli ta Masar ta bayyana.

    Wata tawagar ƙwararru ta kama kifin da ake kira shark a Turance kuma suna tantance shi da zimmar gano musababin kai wa mutumin hari, in ji ma'aikatar.

  12. 'Yan sandan Kano sun sake kama masu kwasar 'ganima' 57

    Mota ɗauke da kaya

    Asalin hoton, Kano State Police Command

    Rundunar 'yan sandan Najeriya reshen Jihar Kano ta sake kama mutum 57 da zargin satar kayayyakin jama'a a matsayin "ganima" yayin da gwamnatin jihar ke rushe-rushen gine-gine.

    Wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Juma'a ta ce Kwamashinan 'Yan Sanda Mohammed Usaini Gumel ne ya ba da umarnin yin fatiro babu dare ba rana don kare dukiyoyin mazauna jihar.

    A farkon makon nan ma rundunar ta kama wasu mutane, akasarinsu matasa, da zargin fasawa tare da sace kayayyaki a shagunan da ke ginin tsohuwar jaridar Triumph a ƙwaryar birnin Kano.

    Lamarin na faruwa ne yayin da sabuwar gwamnatin Kano ƙarƙashin jam'iyyar NNPP ke rushe gine-ginen da ta ce an yi su a kan filayen gwamnati ba bisa ƙa'ida ba, waɗanda tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ta sayar.

    A farkon makon nan wasu hotuna da bidiyo suka karaɗe shafukan sada zumunta, inda suke nuna wani gini yana ruftawa da matasa suna tsaka da ɗibar rodina da ƙarafa na wani ginin da gwamnati ta rusa.

    Bayanan bidiyo, Me al'ummar Kano ke cewa kan rusau da gwamnatin Abba ta ƙaddamar?
  13. Za a tuhumi tsohon shugaban Amurka a kan ɓoye takardun sirrin ƙasa

  14. Sudan ta kori wakilin MDD daga ƙasar

    Volker Perthes

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Sudan ta ce ba za ta amince da cigaba da zaman Volker Perthes ba, mutumin da Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta tura a matsayin jakadanta a kasar.

    Shugaban sojojin Sudan - kuma mai rike da mulkin ƙasar - Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya zargi Mista Perthes da sake assasa rikici a ƙasar, inda ya nemi a gaggauta sauya shi.

    Kafin soma yaƙi tsakanin sojojin Sudan da dakarun rundunar RSF, an yi ta samun zanga-zangar adawa da MDD a Sudan bayan zargin katsalandan a harkokin kasar daga ƙetare.

  15. An kori ministan kyautata rayuwa a Angola saboda cire tallafin man fetur

    Ministan Angola

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Shugaba Lourenço ya fara wa'adin mulki na biyu a shekarar da ta gabata da zimmar haɓaka tattalin arzikin ƙasar

    Shugaban Angola João Lourenço ya kori ministan kula da harkokin tattalin arziki da kyautata rayuwar al'umma sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke bayan matakin gwamnati na cire tallafin man fetur.

    Ya maye gurbin Manuel Nunes Júnior, ƙwararren minista kuma farfesa kan tattalin arziki, da gwamnan babban bankin ƙasar, Jose de Lima Massano, a cewar wata sanarwa.

    Cire tallafin - wanda Mista Nunes Júnior ya ce an yi ne don rage kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa - ya fara aiki ranar 1 ga watan Yuni, abin da kuma ya sa farashin man ya hauhawa.

    Tuni zanga-zanga ta ɓarke a ƙasar mai arzikin fetur, inda ake sa ran za ta ƙaru a ranakun ƙarshen mako.

    A ranar Litinin, mutum biyar sun mutu sannan wasu takwas suka jikkata bayan 'yan sanda sun buɗe wuta kan masu zanga-zanga a garin Huambo.

    Angola na cikin ƙasashen da suka fi arzikin man fetur a Afirka.

  16. Makomar wasu manoman Kaduna, Zamfara, Sokoto na hannun 'yan bindiga

    Manoma a Najeriya

    Yayin da harkokin noma suka fara kankama a wasu sassan Najeriya, manoma a jihohin arewa maso yammacin ƙasar na ci gaba da kokawa kan yadda ‘yan bindiga suka ƙaƙaba musu biyan haraji.

    Da yawan mazauna ƙauyukan Sokoto da Kaduna da Zamfara sai sun biya 'yan fashi diyya kafin su ƙyale su yi shuka, kamar yadda suka shaida wa BBC Hausa.

    Manoman sun ce barazanar da ‘yan bindigar ke yi musu ta jefa su cikin tsoro da tasku.

    Sai dai rundunar 'yan sanda na cewa tana ɗaukar matakai.

    Latsa hoton ƙasa ku saurari rahoton Khalifa Shehu Dokaji:

    Bayanan sautiLatsa hoton sama ku saurari rahoton Khalifa Shehu Dokaji:
  17. Ƙasashen Turai za su sauya dokokinsu kan baƙin-haure

    Baƙin-haure

    Asalin hoton, EPA

    Ministocin harkokin cikin gida na ƙasashen Turai sun amince a aiwatar da garanbawul a tsare-tsare da kuma dokokin kan baƙin-haure da kuma 'yan gudun hijira.

    Sauyin ya ƙunshi yin adalci wajen karɓar baƙin da kuma 'yan gudun hijira kai ɗaya tsakanin mambobin Ƙungiyar Tarayyar Turai domin rage nauyin hidimarsu kan ƙasashe irinsu Italiya da Girka.

    Akasari irin waɗannan baƙi na shiga Turai ta kasashen na Girka da Italiya.

    Wannan sauyi na zuwa ne daidai lokacin da adadin baƙin-haure da ke tsallaka tekun Bahar Rum ya ƙaru da kashi 30 cikin 100.

    Ministocin na harkokin cikin gida a yanzu sun amince da tsarin raba-daidai domin ɗaukar dawainiya iri ɗaya kan ire-iren wadannan baƙi.

  18. Sojojin Tunisiya huɗu sun mutu a hatsarin jirgin sama

    Tunisiya

    Asalin hoton, Tunsisia Presidency

    Sojojin Tunisiya huɗu sun mutu yayin da suke bakin aiki bayan jirginsu na helikwafta ya afka cikin ruwa a arewacin ƙasar.

    Shugaban Ƙasa Kais Saied ya miƙa ta'aziyyarsa a ranar Alhamis ga iyalan mamatan, yana mai cewa "hatsarin ya halaka dakarun soja maza huɗu".

    Ya ƙara da cewa akwai buƙatar "sabunta kayayyakin aiki" yayin da ya gana da ministan tsaron ƙasar.

    Shugaba Saied ya ce hastarin "zai iya faruwa a kowace ƙasa." Ya kuma amince cewa lalacewar wasu kayan aiki a Tunisiya ne "suka haddasa kuma suke ci gaba da haddasa irin waɗannan haɗurra".

    A 2021, wasu sojoji uku sun rasu sakamakon hatsarin da helikwaftansu ya yi a lardin Gabes - sai dai ba a bayyana sakamakon binciken hatsarin ba.

  19. Ana fargabar ɓarkewar kwalara a Ukraine saboda ambaliyar ruwa

    Ambaliyar ruwa

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi gargaɗi kan yiwuwar ɓarkewar cutar kwalara a yankunan Ukraine da ambaliyar ruwa ta shafa bayan ɓallewar madatsar ruwa ta Kakhovka.

    A baya, an taɓa samun alamomin wannan cuta ta kwalara a Ukraine.

    Shugaban WHO, Tedros Ghebreyesus, ya ce suna kokarin ganin yadda za su taimaka wa fannin lafiyar kasar domin kauce wa cutar.

    Wata babbar jami'i a WHO ta ce suna aiki tuƙuru da ma'aikatar lafiyar Ukraine domin ganin yadda za a tunkari lamarin.

    Yayin da ake ci-gaba da aikin kwashe mutane a yankunan da ambaliyar ta shafa, Ukraine da Rasha sun zargi junan su da buɗe wuta kan masu aikin ceto a Kherson, wanda ya sake ta'azzara ambaliyar da madatsar ta haifar.

  20. Assalamu Alaikum

    Ma'abota BBC Hausa barkanmu da hantsin Juma'atu babbar rana, tare da fatan kun tashi lafiya.

    Ku biyo ni Umar Mikail don samun rahotanni kai-tsaye na abubuwan da ke faruw a sassan duniya.

    Sai dai za mu fi mayar da hankali kan Najeriya da Nijar da maƙwabtansu.