Amurka ta bayar da tallafin $100m don yaƙar ta'addanci a Afirka

Mataimakiyar shugaban kasar Amurka, Kamala Harris, ta sanar da tallafin dala miliyan 100 don aikin dakile tashe-tashen hankula a yammacin Afrika, a yayin da ta fara ziyarar aiki ta mako guda a nahiyar.
A wani jawabi da ta gabatar a Ghana, ta ce za a yi amfani da kudin ne don tallafawa kasashen Ghana da Benin da Guinea da Ivory Coast daTogo, don yakar ayyukan masu tsattsauran ra’ayin addini da tashe-tashen hankli a kasashen.
Wannan ce ziyara ta baya-bayan nan da wani babban jami’in kasar Amurka ya kai nahiyar, yayin da gwamnatin Washington ke kokarin dakile karuwar tasirin China da Rasha a Afrika.
Shugaba Biden ya ayyana wani shirin dakile barazanar tsaro na shekaru 10 a yammacin Afrika.














