El Rufai ya janyo ce-ce-ku-ce a kan Peter Obi

Wannan shafin na kawo muku labarai kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Aisha Shariff Bappa

  1. Shugaba Buhari ya taya William Ruto murnar cin zaben shugaban Kenya

    Shugaba Muhammadu Buhari

    Asalin hoton, BUHARI SALLAU

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya taya mutumin da ya ci zaben shugaban kasar Kenya, William Ruto, murna.

    A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga Buharin a harkokin yada labarai Femi Adesina, ya fitar a yau Litinin, ya ce, shugaban ya yaba wa al'ummar kasar ta Kenya kan yadda aka fitar da sakamakon zaben na ranar 9 ga Agustan nan a fayyace kuma lami lafiya.

    Shugaban ya kara da cewa zaben ya nuna yadda tsarin na dumukuradiyya da manufofi da kuma hanyoyinsa shi ne har yanzu hanyar da ta fi dacewa wajen zabar shugabanni da kuma bincikensu.

    Shugaba Buhari ya ce Najeriya na martaba Kenya a matsayin muhimmiyar kawa a yaki da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi na tayar da hankali.

    Alakar da ta danfaru a dadadden tarihi na abokantaka da tattalin arziki da kasuwanci da kuma kyakkyawar mu'amulla ta aiki tare a kungiyoyin kasa da kasa kamar Tarayyar Afirka da Majalisar Dinkin Duniya da kuma kungiyar kasashe renon Ingila (Commonwealth).

    Bayan fata da Shugaban na Najeriya ya yi wa Mista Ruto na rantsar da shi da kama aiki cikin nasara, ya ce yana fatan ci gaba da samun kyakkyawar alaka tsakanin kasashen biyu a kan muhimman abubuwa na hadin gwiwa da suka fi ba fifiko kamar zaman lafiya da tsaro a nahiyar Afirka da dumukuradiyya da kuma bunkasar tattalin arziki da kyautatuwar rayuwar jama'a.

    Haka kuma Buharin ya yaba wa Shugaba Uhuru Kenyatta a kan dattijantaka da shugabanci na-gari da ya ce ya nuna ga al'ummar Kenya a shekara tara da ta gabata.

    Da kuma irin muhimman ababan tarihi da gwamnatinsa ta samar a fannin kayan jin dadin jama'a da ilimi da sauye-sauye a harkar kula da lafiya da yawon bude idanu tare da kwakkwaran tasiri da tallafi ga tsaron nahiyar.

  2. Yawan hare-haren 'yan-bindiga ya karu a Najeriya - Rahoto

    Harin gidan yarin Kuje

    Asalin hoton, OTHERS

    Bayanan hoto, Harin gidan yarin Kuje ya tayar da hankali a Najeriya

    Kamfanin bincike kan harkokin tsaro a yankin Sahel na Beacon Consulting ya ce yawan hare-haren da 'yan bindiga ke kaiwa a Najeriya ya karu a watan jiya na Yuli da kashi 35% idan aka kwatanta da wanda ya gabace shi.

    A cikin wani rahoton da ya fitar yau Litinin kamfanin ya ce an kai hare-hare har sau 506 A kananan hukumomin kasar 236.

    Hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutum 576 da kuma sace wasu 525.

    Sai dai rahoton ya nuna yawan mace-mace sakamakon hari ya ragu da kashi 24 cikin dari a watan Yulin.

    Yayin da satar jama’a ta ragu da kashi 19 cikin dari idan aka kwatanta da watan ya gabace shi na Yuni.

    A tattaunawarsa da BBC shugaban kamfanin Dr. Kabir Adamu ya ce watan Yuli ya kasance mafi sarkakiya ta fuskar tasaro a tarihin Najeriya na nan kusa-kusa, inda aka yi taron majalisar tsaro har uku a dalilin yanayi na tayar da hankali.

    Ya ce babban abin da ya tayar da hankalin shi ne harin da aka kai gidan yarin Kuje a karkashin Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda hakan ya sa fargaba kan za a iya kai wa birnion da ma wasu jihohi na kusa hari.

    Dr Kabiru ya kara da cewa bayanb harin sai kuma ya kasance jami'an gwamnati da suka kai ziyarar duba abin da ya faru a gidan yarin sai suka rika bayar da bayanai masu karo da juna.

    Hakazalika ofisoshin jakadanci a Abujar sun fitar da gargadi ga 'yan kasashensu a kan su yi taka tsan-tsan a kan halin da ake ciki a kasar, wanda wannan duk ya nuna irin mawuyacin halin da kasar ta shiga a harkar tsaro a wannan lokaci.

  3. 'Yan-sanda sun ce sun hallaka 'yan-ta'adda a Jihar Katsina

    Usman Alkali Baba

    Asalin hoton, NIGERIA POLICE

    Rundunar 'yan-sandan Najeriya a Jihar katsina ta ce jami'an tsaro sun hallaka 'yan ta'adda da ba a tantance yawansu ba a yayin musayar wuta biyu a yankin Karamar Hukumar Kurfi a yau Litinin.

    An yi ba-ta-kashin ne a kauyukan Dadawa da Barkiya na karamar hukumar, kamar yadda kakakin rundunar Gambo Isah ya bayyana, a rahoton da jaridar Punch ta ruwaito.

    Ya ce lamarin ya faru da misalin karfe 1.30 na rana, kuma an yi nasarar kwato tumakai 74 da awakai 34 da kuma shanu biyu da 'yan ta'adar suka sata.

    Kakakin ya ce rundunarsu ta samu kira ne na taimakon gaggawa cewa wasu 'yan ta'adda da suka kai 80 a kan babura dauke da makamai sun kai hari kauyukna na Dadawa da Barkiya.

    Ya ce da samun kiran ne suka tura jami'ansu na musamman wadanda suka shiga musayar wuta da su, inda suka kashe wasu tare da raunata wasu.

    Har zuwa lokacin da yake bayar da labarain ya ce jami'ansu na can suna bincike dajin domin kama wadanda aka runata cikin 'yan ta'addar.

  4. Kotu da daure kasurgumin mai satar mutane, Wadume, shekara bakwai

    Wadume

    Asalin hoton, TWITTER/@POLICENG

    Mai shari'a Binta Nyako ta babbar kotun tarayya ta Abuja ta daure kasurgumin mai satar mutanen nan domin karbar kudin fansa da ke Jihar Taraba, a kudu maso gabashin Najeriya, Hamisu Bala, wanda aka fi sani da Wadume, shekara bakwai ba tare da zabin tara ba.

    A shari'ar da aka shafe tsawon shekara uku kotu ta samu Wadume da laifi a kan tuhuma ta biyu da ta goma daga cikin goma sha uku da kuma wasu mutum biyu wadanda Babban Lauyan Gwamnatin Najeriya ya gabatar a kan su bakwai.

    Laifukan da aka daure shi a kai sun shafi gudu daga inda ake tsare da shi da kuma ta'ammali da haramtattun makamai.

    Sauran wadanda aka tuhuma a shari'ar sun hada da Aliyu Dadje, wanda sufeton 'yan-sanda ne, da Auwalu Bala, mai lakabin omo razor da Uba Bala, mai lakabin Uba Delu da Bashir Wazlri mai lakabin baba runs da Zubairu Abdullahi mai lakabin Basho) da kuma Rayyanu Abdul.

    Kotun ta daure Aliyu Dadje (sufeton 'yan-sanda) wanda shi ne babban jami'i a hedikwatar 'yan-sanda a karamar hukumar Ibi ta Jihar Taraba shekara uku bisa laifin kokarin lalata sheda domin boye laifi.

    Mai shari'ar ta kuma daure Delu, da Abdullahi, da Abdul shekara bakwai a gidan yari, yayin da ta wanke da kuma sallamar Omo Razor da Baba Runs sabodarashin sheda.

    A ranar 22 ga watan Yuli ne Justice Nyako ta yanke hukuncin, amma sai ranar Lahadi 14 ga watan Agusta aka bayyana shi ga 'yan jarida.

  5. El Rufai ya janyo ce-ce-ku-ce a kan Peter Obi

    Nasir El Rufai

    Asalin hoton, OTHERS

    Bayanan hoto, El-Rufai ya ce ko shigo da mutane aka yi daga jihohin Igbo Mista Obi ba zai tara mutum miliyan biyu ba

    Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El Rufai, ya janyo ce-ce-ku-ce bayan da ya yi wani martani a shafin tuwita kan rubutun da wani ya yi cewa kusan mutane miliyan biyu za su yi gangamin nuna goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Peter Obi.

    Gwamnan ya mayar da martanin ne a kan rubutun da Abdullahi Zarma, wanda ke gayyatar mutum miliyan biyu domin macin na nuna gogon baya ga Peter Obi a garin Kaduna.

    Ba a dai sanya ranar da za a gudanar da tattakin ba.

    A martanin nasa El-Rufai ya ce, ko da jam'iyyar ta LP ta gayyato magoya baya daga jihohin kudu maso gabas domin wannan gangami Mista Obi ba zai samu mutanen da suka kai yawan haka ba.

    Ya ce , ''A Kaduna? Ba Kaduna Twitter ba? - Ina fatan za ka samu mutum Dari Biyu ma a titunan, hadi da wadanda za a shigo da su, wadanda ba za su iya bude shagunansu ranar Litinin ba, da suka biyo motar dare, a daren da ya gabata!!

    “Dariya nake kawai, wallahi tallahi!! in ji shi a sakon.

    Sakon na gwamnan jaihr Kaduna ya janyo martni iri-iri da masu goyon baya da kuma masu suka.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  6. Gwamantin sojin Mali ta amince MDD ta sabunta sojojinta a kasar

    Sojin Majalisar Dinkin Duniya

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, kasashe 10 ne ke bayar da karon sojojinsu ga rundunar ta Majalisar Dinkin Duniya

    Gwamantin mulkin soji ta Mali ta amince rundunar sojojin tabbatar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya ta ci gaba da sauya dakarun kasashen da ke aiki a karkashinta.

    A wtan da ya gabata ne gwamnatin Mali ta dakatar da hakan sakamakon wani sabani da aka samu da Ivory Coast bayan da jami'an tsaron Malin suka kama kusan sojojin Ivory Coast din 50 a babban filin irgin saman kasar, saboda dalilai na tsaro.

    Kasashe goma ne ke bayar da karo-karon sojoji ga rundunar ta Majalisar Dinkin Duniya wadda ake kira Minusma a takaice.

    A ranar Juma'a ne Jamus ta dakatar da wasu ayyukanta na soji bayan da hukumomin na Mali suka janye wata dama da suka ba wa sojojin na Mali.

    Yayin da take fama da matsalar masu ikirarin jihadi, gwamnatin sojin ta Mali ta kara alakarta da Rasha abin da ya sa dangantakar kasar da Majalisar Dinkin Duniya ta yi tsami.

  7. Sojin Isra'ila 'sun tumɓuke hanyar ƙarƙashin ƙasa da Hamas ke haƙawa' don shiga ƙasar

    Sojin Isra'ila

    Asalin hoton, Getty Images

    Sojojin Isra'ila sun ce sun yi nasarar tumɓuke hanyar ƙarƙashin ƙasa da ƙungiyar Hamas ke haƙawa domin samun hanyar shiga Isra'ila daga arewacin zirin Gaza.

    Sojojin ba su yi ƙarin bayanin yadda aka yi aikin toshe ramin ba.

    Mai magana da yawun sojin Isra'ila ya ce babu wani hatsari da hakan zai yi ga mazauna garuruwa biyu da ke iyakar Gaza da Isra'ilar sakamakon kasa fasa wata katanga mai na'u'rori ta ƙarƙashin kasa da ke bai wa yankin kariya.

    Isra'ila dai tana aiki tuƙuru wajen sanya fasahar da take ankarar da hukumomi da zarar an fara haƙar hanyar ƙarƙashin ƙasa.

    Ba wannan ne karon farko da ake gano hanya irin wannan da mayakan kungiyar Hamas ke kokarin yi ba.

  8. An fargabar ɓarkewar amai da gudawa da maleriya a arewacin Najeriya

    Ƙwararru a fannin Kiwon Lafiyar Jama’a a jihar Kanon Najeriya, sun fara bayyana damuwa kan yiwuwar barazanar ɓarkewar cutar amai da gudawa da zazzabin cizon sauro a wasu daga cikin jihohin da ke arewacin kasar.

    Gargaɗin na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da samun ambaliyar ruwan sakamakon mamakon ruwa sama.

    Ƙwararrun sun ce akwai matakai da dama da ya kamata a ce hukumomi sun ɗauka gabanin faduwar damunar bana, la’akari da hasashen masana da hukumomin kula da yanayi daban-daban suka bayar na fuskantar ambaliyar ruwa sakamakon mamakon ruwan sama da za a samu.

  9. An yanke wa Aung San Suu Kyi hukuncin ƙarin shekara shida a gidan yari

    Aung San Suu Kyi

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata kotu a Myanmar ta yanke wa hamɓararriyar shugabar kasar, Aung San Suu Kyi, hukuncin ƙarin shekara shida a gidan kaso, bayan samunta da laifukan cin hanci da rashawa.

    Wakilin BBC ya ce laifukan da ake tuhumar Aung-San Suu Kyi da su sun haɗa da karkatar da kuɗin tallafin da aka bayar domin bunƙasa fannin lafiyar 'yan Burma, wanda aka ba da a asusun kungiyar da ta sanyawa sunan mahaifiyarta, inda ta karkatar da kudaden asusunta da gina gidan alfarma.

    An yanke wannan hukunci ne ba tare da an bai wa mutane damar shiga kotun ba, ciki har 'yan jarida.

    Kuma Ms Suu Kyi ta sha musanta aikata ba daidai ba kan tuhume-tuhumen da akai mata.

    Tuni dai ta ke zaman shekara 11 da aka yanke mata kan wani laifin na almundahana, a shari'ar farko tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Fabrairun shekarar da ta gabata, nan ma ta musanta zargin.

  10. Iran ta musanta alaka da wanda ya kai wa Salman Rushdie hari

    Salman Rushdie

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Salman Rushdie

    Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta musanta dangantaka da mutumin da ya caka wa Salman Rushdie wuka.

    Mai magana da yawun ma'aikatar, Nasser Kanaani, ya ce marubucin da kuma magoya bayansa ke da alhakin harin saboda batanci ga addinin Musulunci.

    Har yanzu Mr Rushdie na cikin halin rai kwa-kwai-mutu-kwa-kwai bayan caka masa wukar da aka yi a lokacin da yake kan dandamali don gudanar da jawabi a wani taron marubuta a birnin New York na Amurka a ranar Jumma'a.

    Ko da yake a yanzu yana iya numfashi.

    Martanin Iran din ya zo ne bayan sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya yi tir da hukumomin Iran saboda ingiza bore kan marubucin.

    A ranar Lahadi gwamnan New York, Kathy Hochul, ta ce mutumin da ke dauke da wuka ba zai rufe bakin mai dauke da alkalami ba.

    Mutumin da ake zargi dai bai amsa tuhumar da ake masa ta yunkurin kisa ba.

  11. Taliban na bikin zagayowar ranar kwatar 'yanci

    Taliban
    Bayanan hoto, Taliban

    'Yan kungiyar Taliban da masu goyon bayansu na kai komo a babbar hanyar da ke kudancin birnin Kandahar, wato cibiyar 'yan kungyar.

    Mayaka dauke da makamai, a kan ababen hawa na daga tuta mai launin fari da baki a yayin da yara kananan kuma cike da murna ke zaune a gefensu.

    Ga 'yan kungiyar ta Taliban, yau ce ranar bikin samun 'yanci daga dakarun kawancen da Amurka ke jagoranta.

    Da yawa daga cikin 'yan kasar ta Afghanistan ba su san makomar kasar ba har yanzu kamar yadda ake ci gaba da rufe makarantun 'yan mata a kasar.

    Ba ko ina ne ake zaman kunci a kasar ba, alal misali a yankunan karkara, musamman wadanda ke a kudanci da gabashin kasar, wadanda a baya aka yi taho mu gama sosai, a yanzu mazauna kauyukan na zaman lafiya ba tare da wata fargaba ba.

    Abin da yake hada kan kasar shi ne yadda ake nuna damuwa a game da matsalar tattalin Arziki da mawuyacin halin da 'yan kasar ke ciki, ga talauci da kuma karuwar rashin abincin mai gina jiki saboda dakatar da bayar da kudaden waje

  12. NDLEA ta gano tarin miyagun kwayoyi da aka boye a kan kifi

    The haul was meant for export to Dubai from a Nigerian airport

    Asalin hoton, Getty Images

    Mahukunta a Najeriya sun bankado kunshin kwayar crystal methamphetamine da aka boye a kan wani kifi da aka sanya a cikin kwalin da za a kai shi Hadaddiyar Daular Larabawa.

    A ranar Juma'a ne aka gano kunshin wanda nauyinsa ya kai kusan kilogram 12 a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Legas.

    Hukumar hana sha da fataucin miyagin kwayoyi ta kasarce ta sanar kama kwayar a ranar Lahadi.

    Hukumar ta ce an samu kunshi-kunshin kwayar 442 kowannesu an nade shi da leda a kan bushasshen kifin da aka zuba su a kwalaye za a fita da su.

    Tuni aka kama mutumin da ke da kwalayen kifin.

  13. Sojojin Najeriya sun sake kubutar da wata dalibar makarantar Chibok

    A baya an sako 'yan matan Chibok da dama

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, A baya an sako 'yan matan Chibok da dama

    Rundunar sojin Najeriya ta ce ta yi nasarar kubutar da wasu 'yan makaranta mata hudu wadanda 'yan Boko Haram suka sace.

    Daya daga cikin matan 'yan makarantar Chibok ce da aka sace shekaru takwas da suka wuce kuma an same ta da danta dan shekara hudu.

    A ranar Juma'a ne sojojin suka kubutar da matan. Ba a sani ba ko sakin 'yar makarantar Chibok din aka yi ko kuma kubutar da ita sojoji suka yi.

    A watan Afrilun 2014 ne 'yan Boko Haram suka sace dalibai a makarantar mata ta Chibok su 270 abin da ya harzuka 'yan Najeriya har aka kiraye-kiraye a kan gwamnati ta yi kokarin kubutar da su.

    Da yawa daga cikinsu dai sun kubuta yayin da wasunsu kuma aka musaya da su domin sakin wasu 'yan kungiyar da gwamnati ta kama.

  14. Ana zargin dakarun Burkina Faso da kashe Fulani 40

    Burkina Faso's military has denied repeated accusations of rights abuses

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Dakarun Burkina Faso sun sha musanta aikata ba daidai ba

    Kungiyoyin kare hakkin dan adam a Burkina Faso sun zargi sojojin kasar da kashe fararen-hula fiye da 40 a arewacin kasar.

    Bayanan da kungiyoyin suka tattara daga wajen mazauna yankin sun bayyana cewa ana kuma sace mutane sosai, ga kuma kisa da ake yi ba gaira babu dalili.

    Kungiyoyin sun ce an gano gawarwakin mutane da dama a kan hanyar da ke tsakanin Taffogo da kuma Bouroum inda aka daure musu hannaye.

    Daya daga cikin kungiyoyin kare hakkin dan adam din mai suna the Observatory of Human Dignity, ta ce yawancin wadanda aka kashen Fulani ne Musulmai makiyaya.

    Rundunar sojojin dai ta sha musanta irin wadannan zarge-zarge na take hakkin dan adam.

    Kungiyoyin sun ce lamarin dai ya faru ne a farkon watan da muke ciki a kauyen Taffogo da ke Tougouri.

    Sojoji Burkina Faso dai na yaki da kungiyoyin masu tayar da kayar baya wadanda ake zargin suna da alaka da kungiyar al-Qaeda ko kuma kungiyar IS, inda suka kashe mutane fiye da dubu biyu da kuma tursasawa wasu miliyan daya da dubu dari tara barin muhallansu.

  15. An bayar da umarnin tsaurara matakan tsaro a asibitoci da makarantu a Najeriya

    Alkali

    Asalin hoton, Nigeria Police Force

    Babban Sufeton 'yan sandan Najeriya, Usman Alkali Baba, ya bayar da umarnin a tura karin jami'an tsaro da a makarantu da asibitocin da ke sassan kasar.

    Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan ta kasa, Olumuyiwa Adejobi, ne ya sanar da haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

    Cikin sanarwar, jami'in ya ce an bai wa jami'in 'yan sanda umarnin su rika sintiri a-kai-a-kai musamman a wuraren da ke fuskantar barazanar tsaro da kuma kai samame irin wuraren don bankado bata-gari.

    Babban sufeton ya bayar da umarnin ne bayan ya karbi wasu rahotanni da bayanai daga rundunoni daban-daban na kasar a kan yanayin da al'amuran tsaro ke ciki a kasar.

    Babban jami'in dan sandan ya kuma ba wa manyan jami'an 'yan sanda umarnin su rinka amfani da bayanan sirrin da suka tattara a yayin aikinsu da kuma sanin wadanda ya kamata a tura a wuraren da ke fuskantar barazanar tsaro.

    Usman Alkali Baba, ya kuma bukaci al'ummar kasar da su bai wa jami'ansu dukkan goyon bayan da ya kamata a yayin gudanar aikinsu.

  16. Jami'ai sun shirya tsaf domin sanar da sakamakon zaben Kenya

    Dakin sanar da sakamakon zabe

    Cibiyar da ake tattara sakamakon zaben kasar Kenya da ke Nairobi, babban birnin kasar ta dauki harama a yayin da hukumar zaben kasar take kammala tsarin sanar da wanda ya lashe zaben shugaban kasar.

    Abubuwa sun kankama a wurin da za a sanar da sakamakon zaben inda wakilan 'yan takarar shugaban kasa da lauyoyi da kuma jami'an hukumar zabe suka dukufa wajen tantance takardun rubuta sakamakon zaben da aka aiko daga yuankuna daban-daban na kasar.

    Ma'aikata suna can suna goge tebura da kujeru wadanda jami'ai suka yi amfani da su.

    Kawo yanzu babu kwamishinonin zabe a wurin da za a sanar da zaben, amma rahotanni sun ce watakila suna can suna gudanar da taruka domin fitar da sanarwar karshe ta sakamakon zaben shugaban kasar.

    Babban dakin da za a sanar da sakamakon zaben Kenya

    Babban dakin da za a sanar da sakamakon zaben kasar kenya ya kwashe kwanaki da dama cike da hayaniyar jama'a, inda a wasu lokuta akan samu sabani game da tsarin tattara sakamakon zaben, sai dai yanzu abubuwa sun lafa.

    An kara matakan tsaro a kofar shiga babban dakin tattara sakamakon zaben.

    Kawo yanzu, Mataimakin shugaban kasa William Ruto yana gaban tsohon Firai Minista Raila Odinga - inda ya samu kashi 51% yayin da shi kuma Odinga ya samu kashi 48%, a cewar kafafen watsa labaran kasar.

    Dole ne a ranar da sakamakon zaben zuwa ranar 16 ga watan Agusta, kamar yadda dokokin kasar Kenya suka bayyana.

  17. Barkanmu da safiya

    Aisha Shariff Baffa ce ke fatan kasancewa da ku a wannan shafi, inda za mu rika kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku kai-tsaye.

    Za mu mayar da hankali a kan batutuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Amma da farko, kun karya kumallo?

    Koko da kosai

    Asalin hoton, OTHER