Turkiyya za ta taimakawa Najeriya magance matsalar tsaro – Buhari

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita and Awwal Ahmad Janyau

  1. Canada za ta ɗage haramcin hana ƴan Najeriya shiga ƙasarta

    Justin Trudeau

    Asalin hoton, Reuters

    Gwamnatin Canada ta ce za ta ɗage haramcin shiga ƙasarta ga dukkanin ƙasashe 10 da ta hana a watan da ya gabata daga cikin matakan dakile bazuwar sabon nau’in korona na Omicron.

    Ministan lafiyar ƙasar Jean-Yves Duclos wanda ya tabbatar da matakin a ranar Juma’a ya ce duk da haka duk wanda zai shiga ƙasa ƙasa da sa’a 72 sai ya gabatar da gwajin da ya nuna ba ya ɗauke da cutar.

    Yawan masu kamuwa da korona na ci gaba da ƙaruwa a Canada kuma gwamnatin ƙasar ta nemi ƴan ƙasarta su gujewa yin tafiye tafiye ƙasashen waje.

    Masu suka sun ce matakin haramta wa ƴan Afrika ta Kudu da Najeriya da Masar da wasu ƙasashe bakwai ba ya da wani amfani saboda yadda cutar ta riga ta bazu.

  2. Ozil ya yi wa ‘Musulmin duniya addu’a’

    Tsohon ɗan wasan Arsenal da Real Madrid Mesut Ozil wanda yanzu ke taka leda a Fenerbahçe ta Turkiyya ya yi wa musulmi addu’a a ranar Juma’a.

    A saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Ozil ya nuna yana yankin Xinjiang na Chinainda ya daɗe yana bayyana damuwa kan zargin ƙuntatawa Musulmin Uighur a China.

    “Addu'a ga dukkaninin ƴan uwa musulmi da ake zalunta da hadin kai da ci gaban dukkan musulmin duniya,” kamar yadda ya wallafa a Facebook yana mai cewa “ba za su taɓa rasa addu’oinmu ba”

  3. An gurfanar da matar da ta sayar da jaririnta N25,000

    Wata kotu a Liberia ta tuhumi wata mata da laifin safarar mutane bayan ta sayar da jaririnta ƴar wata shida ga wata mata da ba a bayyana ba kan dala 60 (N25,000) kacal.

    Ta musanta cewa ta bayar da jaririn don a ba ta kuɗi, a cewar jaridar Liberia ta intanet The News.

    Ta yi iƙirarin cewa ta yi musayar ne saboda ta wahalar kula da yaron a matsayinta na wadda ba ta da aure, a cewar jaridar Front Page Africa.

    Babu wasu shirye-shiryen na jin dadin jama'a ga yaran da aka yi watsi da su a ƙasar.

    An kai ta gidan yari na Monrovia, a cewar Front Page Africa Online.

  4. Turkiyya za ta taimakawa Najeriya magance matsalar tsaro – Buhari

    Buhari da Erdogan

    Asalin hoton, Presidency

    Shugaba Muhammadu Buhari da ke ziyarar aiki a Turkiyya ya ce ƙasar ta yi alƙawalin taimakawa Najeriya magance ƙalubalen tsaro da ke damunta.

    Sanarwar da fadar shugaban na Najeriya ta fitar ta ce shugaban Turkiyya ne ya yi tayin taimakawa Najeriya kan fannin sha’anin tsaro.

    “A ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya a Najeriya, shugaba Muhammadu Buhari, ya ce Najeriya za ta haɗa gwiwa da Turkiyya wajen tunkarar ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta,” in ji sanarwar.

    A cewar sanarwar shugaba Buhari ya yi godiya ga shugaban Turkiyya kuma a ganawar da shugabannin biyu suka yi ya shaida masa cewa, Turkiyya ta samu ƙwarewa sosai wajen tunkarar ƙalubalen tsaro iri daban-daban kuma Najeriya za ta amfana da ƙwarewa.

  5. Kotu ta tabbatar da shugabancin APC ɓangaren Shekarau a Kano

    Shekarau

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata babbar kotu a Abuja ta tabbatar da Ahmadu Haruna Zago na ɓangaren Sanata Shekarau a matsayin shugaban APC a Kano.

    Alƙalin kotun mai shari’a Hamza Muazu wanda ya zartar da hukuncin ya kuma buƙaci ɓangaren gwamna Ganduje da ya shigar da ƙara yana neman a yi watsi da shugabancin ɓangaren Shekarau ya biya tarar miliyan ɗaya, kamar yadda Sha’aban Sharada ɗan majalisa tarayya ya shaida wa BBC.

    Ya ce kotun ta ce ɓangaren shekarau ya gudanar da zaɓukan mazaɓu da na ƙananan hukumomi, kuma zai iya gudanar da na jiha.

    Tun da farko kotun ta halatta jagorancin ɓangaren Shekarau wanda ya ƙalubalanci cewa ɓangaren Ganduje bai gudanar da zaɓukan mazaɓu ba, matakin da ya sa ɓangaren Ganduje ya nemi a dakatar da ci gaba da shari’a saboda akwai giɓi.

    Bayan sauraren koken, alƙalin kotun ya zartar da hukuncin tabbatar da zaɓukan da ɓangaren Shekarau ya gudanar.

    Hakan ya nuna kotun ta rusa shugabancin APC na Abdullahi Abbas ɓangaren gwamna Ganduje

  6. An ɗaure wasu Faransawa kan kitsa juyin mulki a Madagascar

    Andry Rajoelina.

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaba Andry Rajoelina

    Wata kotu a Madagascar ta yanke hukuncin daurin shekaru ashirin a gidan yari ga mutane biyar da suka hada da Faransawa biyu bisa laifin yunkurin kashe shugaba Andry Rajoelina a farkon wannan shekara.

    Waɗanda ake tuhumar suna cikin mutane 20 da ake zargi da yunkurin juyin mulki a watan Yuli.

    Mutanen biyar - ciki har da tsohon Kanal din sojojin Faransa, Philippe Francois - an same su da laifin shirya kisan, da kuma yin zagon ƙasa ga tsaron kasar.

    An kuma yankewa biyu daga cikinsu hukuncin daurin rai da rai bisa zargin mallakar makamai ba bisa ka'ida ba.

    Mai gabatar da kara ya ce asamamen da ƴan sanda suka yi wa sakwannin imel, an gano makamai da kuɗi da kuma wani fayil na kwamfuta ɗauke da kasafin kudin shirin. Dukkansu sun musanta zargin.

  7. Zan yi ƙoƙarin ciyar da Najeriya gaba kafin na koma gonata a 2023 – Buhari

    Shugaba Buhari

    Asalin hoton, Presidency

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce zai mayar da hankali wajen ci gaban Najeriya da al’ummarta kafin ƙarshen wa’adinsa.

    Shugaban ya bayyana haka ne tare da hotunan bikin zagayowar haihuwarsa a Turkiyya a shafin Facebook.

    “Ina fatan zuwa 2023 idan na kammala wa’adina na koma gida na kula da gona ta. Amma kafin nan zuwa lokacin zan yi iya ƙoƙarina wajen ciyar da ƙasa da al’ummarta gaba da gudanar da ayyuka kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada,” kamar yadda shugaban ya wallafa a shafinsa na Facebook.

    Ya ce ashe bai guje wa bikin haihuwarsa ba a Abuja kuma haka ma a Turkiyya sai da aka haɗa masa bikin.

    A ranar Juma’a ne shugaba Buhari ya cika shekara 79 da haihuwa. Kuma tun a ranar Alhamis ya tafi Turkiyya.

  8. Ɗan sanda ya kashe ɗan jarida bisa kuskure a Kongo

    .

    Wani ɗan jarida a Jamhuriyyar Dimokraɗiyyar Kongo ya rasu sakamakon raunin da ya samu sakamakon harbinsa da bindiga da aka yi a lokacin da ƴan sanda suka yi arangama da yan bindiga a ƙasar.

    Jean-Marie Luzingu na a Kinshasa a lokacin da aka samu arangamar.

    Wani harsashi da wani ɗan sanda ya harba ne ya samu ɗan jaridar, kamar yadda wani wanda ya shaida lamarin ya bayyana wa Mishapi Voice Radio.

    Ƴan uwansa yan jarida dai na ci gaba da jimamin mutuwarsa a shafin Twitter.

    A halin yanzu ana ci gaba da bibiya domin gano waɗanda suka haddasa wannan tarzomar.

    Ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasar ta ce tana buƙatar a bi wa wanda aka kashe haƙƙinsa.

  9. An kashe mutum tara da raunata biyu a sassan Kaduna

    KSTG

    Asalin hoton, KSTG

    Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa ƴan bindiga sun kashe mutane tara da kuma raunata mutum biyu a wasu hare-haren da aka kai a Ƙananan Hukumomin Chikun da Zaria da Zangon Kataf.

    A wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar, an kashe mutum uku yayin da ƴan bindiga suka yi wa garuruwan Buruku da Udawa tsinke.

    Haka kuma a yankunan Yola da Kadi da ke Ƙaramar Hukumar Chikun, ƴan bindigar sun kashe mutum guda da raunata ɗaya.

    Yan bindigan sun sake kashe kashe mutum biyu a ƙauyen Sako da ke Zangon Kataf, haka kuma an gano gawarwakin mutum biyu a yankunan Kurfi da Magamiya da ke a Zangon Kataf ɗin.

    Haka ma a Ƙaramar Hukumar Zaria, an kashe mutum ɗaya a ƙauye Saye.

    Gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya nuna ɓacin ransa kan wannan lamari tare da addu'a ga waɗanda suka rasu da kuma waɗanda suka jikkata su samu sauƙi.

  10. Buhari ya yanka kek ɗin murnar ranar haihuwarsa a Turkiyya

    NIGERIA PRESIDENCY

    Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yanka kek ɗin murnar ranar haihuwarsa a Turkiyya bayan ya cika shekara 79 da haihuwa.

    An tsara kek ɗin da launin Najeriya wato fari da tsanwa inda bayan ya yanka kek ɗin sai ya tattauna da hadimansa kafin suka tafi wajen taron tattaunawa kan cinikayya tsakanin Turkiyya da ƙasashen Afrika.

    Shugaban ƙasar ya bayyana cewa zai ci gaba da yin iya bakin ƙoƙarinsa wajen yi wa ƴan Najeriya aiki har zuwa lokacin da zai miƙa mulki a 2023.

    Shugaban ya kuma ce zai koma gona ne domin ci gaba noma da kiwo bayan ya miƙa mulki.

    NIGERIA PRESIDENCY

    Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

    NIGERIA PRESIDENCY

    Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

    NIGERIA PRESIDENCY

    Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

    NIGERIA PRESIDENCY

    Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

  11. Darajar kuɗin Turkiyya ta ƙara raguwa

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Kuɗin Turkiyya wato lira na ci gaba da faɗuwa a kasuwar canji ta duniya inda ta ƙara faɗuwa da kashi shida cikin 100 a daidai lokacin da ake cikin fargabar hauhawar farashin kayayyaki a ƙasar.

    Wannan na zuwa ne bayan rage adadin kuɗin ruwa a ƙasar a ranar Alhamis. Shugaban ƙasar Recep Tayyip Erdogan ya kuma sanar da cewa zai ƙara mafi ƙarancin albashin ƙasar da kashi 50 cikin 100 inda ake kyautata zaton idan aka yi hakan farashin kayayyaki zai ƙaru.

    Mista Erdogan ya dage kan cewa zai iya daƙile hauhawar farashin kayayyaki duk da rage kuɗin ruwan da ya yi, sai dai ƴan kasuwa na cikin fargaba.

    A bana kaɗai, sai da darajar kuɗin ta ragu da kashi 50 cikin 100, inda aka fi samun raguwar a watan da ya gabata.

  12. 'Masu iƙirarin jihadi' sun fille kan wani fasto a Mozambique

    .

    Asalin hoton, AFP

    Wasu da ake zargin masu iƙirarin jihadi ne sun fille wa wani fasto kai a gundumar Macomia mai ɗumbin arziƙin gas da ke lardin Cabo Delgado na Mozambique.

    A ranar Laraba, wata mata ce a ƙauyen Nova Zambézia ta tafi ofishin ƴan sandan gundumar ɗauke da jaka da ke ɗauke da kan mutum wanda kan mijinta ne, kamar yadda sojojin ƙasar suka bayyana.

    Rahotanni sun ce masu iƙirarin jihadin sun yi wa faston a tare a wani fili, inda suka fille masa kai sa'annan suka miƙa kan ga matarsa tare da ba ta umarnin kai wa hukumomi rahoto.

    Wannan ne hari na baya-bayan nan da masu iƙirarin jihadin suka kai inda suka matsa wa lardin Cabo Delgado tun shekarar 2017.

  13. Ambaliyar ruwa ta yi sanadin mutuwar mutum takwas a Iraki

    Mutum takwas sun rasu a yankin Kurdawa da ke Iraƙi sakamakon ambaliyar ruwa.

    Gwamnan Erbil babban birnin yankin na Kurdawa ya bayyana cewa akasarin waɗanda lamarin ya shafa sun maƙale ne a cikin gidajensu bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka yi a safiyar Juma'a.

    Ana ci gaba da neman mutanen da suka ɓace.

    Iraƙi dai na fuskantar sauyin yanayi a ƴan shekarun nan inda aka fuskanci yanayi mai zafi da kuma ƙarancin ruwa sai kuma a yanzu ambaliyar ruwa.

  14. An tura wani tsohon direba a Rwanda gidan yari kan kisan kiyashi

    .

    Asalin hoton, AFP

    Wata kotu a Paris ta samu wani direba Bafaranshe kuma ɗan Rwanda, Claude Muhayimana da laifi a kisan kiyashin da aka yi wa ƴan ƙabilar Tutsi a Rwanda a 1994.

    Kotun ta tura shi domin zama gidan yari na tsawon shekara 14.

    Claude Muhayimana ya yi aiki a matsayin direba a wani otel da ke Rwanda kuma ana zarginsa da jigilar ƴan ƙabilar Hutu zuwa wurare da dama da aka kashe ƴan Tutsi.

    Sai dai wanda ake zargin ya musanta duka laifukan da ake zarginsa da aikatawa.

  15. An kashe mahaifi da ƴaƴansa maza biyu a Benue

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu da ba a san ko su wanene ba sun kashe wani mahaifi da ƴaƴansa maza biyu a yayin da suke dawowa daga gona a garin Ore da ke Ƙaramar Hukumar Ado ta Jihar Benue a Najeriya.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ana ta samun kashe-kashe a wasu sassa na Ado da ke makwaftaka da Jihar Ebonyi inda ake ta samun rikice-rikicen kan iyaka.

    Haka kuma rahotanni na cewa a baya an ta samun hare-haren makiyaya a yankin.

    Mazauna yankin sun bayyana cewa wannan kisan ya sa ba su iya fita su yi walwala yadda ya kamata.

    Shugaban Ƙaramar Hukumar Ado, James Oche ya tabbatar wa manema labarai da faruwar lamarin hakazalika shi ma mai magana da yawun ƴan sanda reshen Jihar Benue ya tabbatar da hakan.

  16. Majalisar Ɗinkin Duniya za ta yi taron gaggawa kan Habasha

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar Kare Haƙƙin Bil Adama Ta Majalisar Ɗinkin Duniya za ta gudanar da taron gaggawa kan batun rikicin da ake yi a Habasha sakamakon rahotannin da ake ta samu kan irin laifukan da ake aikatawa a yankin Tigray.

    Taron wanda za a yi a ranar Juma'a, Ƙungiyar Tarayyar Turai ce ta buƙaci a gudanar da shi inda za a tattauna kan ko a kafa kwamitin bincike domin bincikar irin cin zarafin bil adama da ƙungiyoyin kare haƙƙi suka ce za su iya kasancewa laifukan yaƙi.

    An soma rikici a Tigray a Nuwambar bara a lokacin da gwamnatin Habasha ta tura jami'ai zuwa yankin domin daƙile barazanar da mayaƙan TPLF suke yi - bayan mayaƙan sun ƙwace sansanonin sojin da ke yankin na Tigray.

    A watan da ya gabata Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar da wani rahoto mai shafi 100 da ke bayar da bayanai dalla-dalla kan irin take haƙƙin da aka yi a Tigray, ciki har da ƙona garuruwa da fararen hula da kuma fyaɗe.

  17. Barkanmu da safiya,

    Jama'a barkanmu da safiyar Juma'a, 17 ga watan Disambar 2021.

    A yau ma za mu ci gaba da kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya ziyartar shafinmu na Facebook ko Twitter ko kuma na Instagram domin bayyana ra'ayoyinku kan irin labaran da muke wallafawa ko kuma tafka muhawara a kai.