Zaɓen Anambra: APGA ta ba da gagarumar tazara

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau and Umar Mikail

  1. Ƙarshen rahotannin kenan a wannan shafi

    Mun kawo ƙarshen rahotanni a wannan shafi. Amma shafin sakamako kai-tsaye na nan.

    Za mu kawo muku rahoton wanda ya lashe zaɓen a wani shafin daban - da zarar INEC ta sanar.

    • Sakamakon zaben gwamnan Anambra na 2021
  2. Magoya bayan APGA sun fara murna

    Soludo

    Ɗan takarar jam'iyya mai mulkin Anambra ta All Progressives Grand Alliance (APGA) ya nemi magaoya bayansa da kar su shiga bukukuwan murnar lashe zaɓen gwamnan jihar tukunna "saboda ba a gama fafatawa ba".

    Ya zuwa yanzu hukumar zaɓe ta INEC ta sanar da sakamakon ƙaramar hukuma 19 cikin 21 kuma APGA ce ke kan gaba da nasarar lashe 17 daga cikinsu.

    Yanzu haka Farfesa Charles Soludo na karɓar 'yan uwa da abokan arziki a gidansa da ke Isuofia na jihar, inda suke raye-raye da waƙe-waƙe.

    Da yake jawabi ga magoya bayan, Mista Soludo ya gode musu bisa ruwan ƙuri'ar da suka yi masa sannan ya nemi su jira kafin su shiga murna.

    Sai dai magoya bayan ba su ji kiran ba, inda tuni wuri ya ɓarke da sowar waƙe-waƙe da raye-raye.

    Anambra
    Anambra
  3. An yi gasar Al Kur’ani ta ƴan ƙasa da shekara 13 a Ghana

    Ghana

    An gudanar da gasar karatun Al Kur`ani ta ƙasa a Ghana a karon farko a Accra, tsakanin `ƴan kasa da shekara 13 daga yankuna uku na ƙasar da suka ƙunshi yankin Ashanti da kuma arewacin Ghana.

    Yara biyar ne daga kowanne yanki suka samu nasarar zuwa zagayen ƙarshe na wannan gasa, inda suka fafata tsakaninsu a ɗakin taro na ƙungiyar malamai ta kasa.

    Wakilin BBC na Ghana Fahd Adam ya halarci gasar kuma ya aiko da rahoto na musamman.

    Bayanan sautiAn yi gasar Al Kur’ani ta ƴan ƙasa da shekara 13 a Ghana
  4. INEC za ta yanke hukunci kan ƙaramar hukuma biyu

    Anambra

    Ya zuwa yanzu, hukumar zaɓe ta INEC ta bayyana sakamakon zaɓe na ƙaramar hukuma 19 daga cikin 21.

    Ƙaramar hukumar Orumba ta Arewa da kuma Ihiala ne suka rage, sai dai akwai matsaloli game da yankunan.

    Babban jam'in tattara sakamakon zaɓe na Orumba ta Arewa ya bayyana wa INEC cewa duk da an gudanar da zaɓe a yankin nasa, amma tilasta masa aka yi ya saka hannu kan takardar sakamakon zaɓen.

    Ita kuwa Orumba ta Arewa, baturen zaɓe na ƙaramar hukumar ya bayyana cewa ba a gudanar da zaɓen ba kwata-kwata.

    Hukumar zaɓen ta ce za ta bayyana matsayinta game da ƙananan hukumomin idan aka dawo daga hutun da aka tafi na faɗar sakamakon da ake yi yanzu haka.

  5. Ba a yi zaɓe a Ƙaramar Hukumar Ihiala ba

    Anambra

    Shugaban hukumar zaɓe na Ƙaramar Hukumar Ihiala a Jihar Anambra ya sanar da cewa ba a gudanar da zaɓen ba a yankinsa.

    Ihiala na da rumfunan zaɓe fiye da 300.

    Sai dai INEC ba ta bayyana abin da zai faru ba game da rashin gudanar da zaɓen a yankin.

    Anambra na da ƙaramar 21 kuma zuwa yanzu INEC ta sanar da sakamakon 19 daga cikinsu.

    Jam'iyyar APGA mai mulkin jihar ce ke kan gaba, inda ta lashe 17 daga ciki. Sai kuma PDP da YPP da suka lashe ɗaya kowaccensu.

  6. APGA ta yi nasara a Awka ta Arewa

    Jam'iyyar APGA ta ci gaba da doke jam'iyyun hamayya, inda ta lashe Ƙaramar Hukumar Awka ta Arewa.

    Sakamakon ya nuna:

    APC – 755

    APGA – 1,908

    PDP – 840

    YPP – 381

  7. Jami'in tattara sakamako ya ce an tilasta masa wajen saka hannu

    Babban jam'in tattara sakamakon zaɓe na ƙaramar Hukumar Orumba ta Arewa ya bayyana wa INEC cewa duk da an gudanar da zaɓe a yankin nasa, amma tilasta masa aka yi ya saka hannu kan takardar sakamakon zaɓen.

    Jami'in ya yi zargin cewa wasu jami'an tsaro ne suka tsare shi har ma suka harba hayai mai sa hawaye a wurin.

  8. Sakamakon zaɓe kai-tsaye

    Kar ku manta, za ku iya samun sakamakon zaɓen Anambra kai-tsaye a nan:

    • Sakamakon zaben gwamnan Anambra na 2021
  9. Labarai da dumi-dumi, APGA Nnewi ta Kudu

    APGA ta sake lashe Ƙaramar Hukumar Nnewi ta Kudu

    Nnewi ta Kudu:

    APC – 1,307

    APGA – 3,243

    PDP – 2,226

    YPP – 1,327

  10. Labarai da dumi-dumi, APGA ta lashe Ekwusigo

    Ƙaramar Hukumar Ekwusigo ta shiga hannun jam'iyyar APGA.

    Ita ce ta 12 da jam'iyyar mai mulki ta lashe.

    Ƙaramar Hukumar Ekwusigo:

    APC – 1,237

    APGA – 2,570

    PDP – 1,857

    YPP – 727

  11. Labarai da dumi-dumi, APGA ta sake lashe Aguata

    Jam'iyya mai mulki a Anambra ta sake lashe Ƙaramar Hukumar Aguata.

    Hakan na nufin APGA ta cinye ƙaramar hukuma 11 kenan cikin 13 da hukumar zaɓe ta INEC ta sanar.

    Jam'iyyar PDP da YPP kowaccensu ta lashe ƙaramar hukuma ɗaya.

    Ƙaramar Hukumar Aguata:

    APC – 4,773

    APGA – 9,136

    PDP – 3,792

    YPP – 1,070

  12. Labarai da dumi-dumi, APGA ta lashe Onitsha ta Arewa

    Jam'iyya mai mulki a Anambra ta sake lashe ƙaramar hukumar Onitsha ta Arewa.

    Onitsha ta Arewa:

    APC – 3,909

    APGA – 5587

    PDP – 3,781

    YPP – 682

  13. PDP ta lashe ƙaramar hukuma ta farko

    Jam'iyyar adawa ta PDP a Jihar Anambra ta lashe Ƙaramar Hukumar Ogbaru wadda ita ce ta farko da ta yi nasara a zaɓen ranar Asabar.

    Valentine Ozigbo na PDP ya samu ƙuri'a 3,445, yayin da Charles Soludo na jam'iyyar APGA mai mulkin jihar ke biye masa da 3,051.

    Ga sakamakon:

    APC – 1,178

    APGA – 3,051

    PDP – 3,445

    YPP – 484

  14. Cutar sankara na kama mutane miliyan biyar duk shekara

    Cutar sankara na karuwa a duniya, inda sabbin mutane miliyan biyar ke kamuwa da cutar a duk shekara.

    Kuma Najeriya na cikin ƙasashen da cutar ke ƙaruwa.

    Ku saurari shirin Lafiya Zinariya na BBC.

    Bayanan sautiLafiya Zinariya: Cutar sankara na kama mutane miliyan biyar duk shekara
  15. Daular Larabawa ta ba waɗanda ba musulmi ba damar yin aure a ƙasar

    Sheikh Khalifa bin Zayed al-Nahayan

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Sheikh Khalifa bin Zayed al-Nahayan

    Masarautar Abu Dhabi a Daular Larabawa ta yi wasu sabbin sauye-sauye ga dokokinta da za su ba waɗanda ba musulmi ba damar yin aure da saki da kuma samun kulawar ƴaƴa.

    A baya, aure da saki na ƙarƙashin bisa dokokin shari’ar Musulunci.

    Sanarwar da shugaban Abu Dhabi, Sheikh Khalifa bin Zayed al-Nahayan ya fitar, ta ce an ɗauki matakan ne da nufin janyo hankalin masu basira da hazaka daga ƙasashen waje domin ci gaban masarautar.

    Za a kafa wata sabuwar kotu da za ta gudanar da harkokin iyali da waɗanda ba musulmi ba a Abu Dhabi, da za ta yi aiki a harshen Ingilishi da Larabci.

    Sheikh Khalifa kuma shi ne shugaban Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa - wacce a bara ta ɓullo da wasu sauye-sauye na shari'a da suka haɗa da haramta saduwa kafin aure da shan barasa.

  16. APGA ta lashe ƙaramar hukumar Orumba ta kudu

    APC – 2,060

    APGA – 4,394

    PDP – 1,672

    YPP – 887

    Yanzu ƙananan hukumomi 10 APGA ta lashe cikin 21 da aka sanar kawo yanzu yayin da YPP ta lashe ɗaya.

    Anambra
  17. Ifeanyi Ubah na YPP ya lashe zaɓe a Nnewi ta arewa

    APC – 1,278

    APGA – 3,369

    PDP – 1,511

    YPP – 6,485

    Zuwa yanzu ƙananan hukumomi 10 Inec ta sanar kuma APGA ce kan gaba inda ta lashe ƙananan hukumomi tara a zaɓen gwamnan Anambra da aka gudanar a ranar Asabar.

  18. APGA ta lashe ƙaramar hukumar Njikoka a Anambra

    APC – 3,216

    APGA – 8,803

    PDP – 3,409

    YPP – 924

    Yanzu ƙananan hukumomi tara APGA ta lashe cikin 21 da aka sanar kawo yanzu.

  19. APGA ta lashe ƙaramar hukumar Onitsha ta kudu

    Sakamakon zaɓen ƙaramar hukumar Onitsha ta kudu

    APC – 2,050

    APGA – 4,281

    PDP – 2,253

    YPP – 271

    Yanzu ƙananan hukumomi takwas APGA ta lashe cikin 21 da aka sanar kawo yanzu.

  20. APGA ta lashe ƙaramar hukumar Idemili ta kudu

    APC – 1,039

    APGA – 2,312

    PDP – 2,016

    YPP – 752

    APGA ta sha gaban PDP ne da tazarar ƙuri’a kusan 300 a Idemili ta kudu.

    Yanzu ƙananan hukumomi bakwai APGA ta lashe cikin 21 da aka sanar kawo yanzu.