Abubuwan da suka faru a Najeriya da Nijar da makwabta

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma sauran kasashen Afirka.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Umar Mikail

  1. Sarki Sanusi ya amince da nadin Shugaban Majalisar Sarakuna

    Sarki Sanusi

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakin Kano, Muhammadu Sanusi na biyu, ya ce ya amince da nadin da gwamna Ganduje ya yi masa na shugabantar majalisar sarakuna.

    Wata takarda da gwamna Ganduje ya aike wa Sarki Sanusi ranar 19 ga Disamba ta nemi Sarki Sanusin da ko dai ya bayyana amincewarsa da nadin ko kuma ya yi watsi da shi.

    Katsam kuma a wata wasikar mai dauke da sa hannun sakataren Sarkin Kano, Abba Yusuf da fadar ta aike wa gwamna Ganduje, ta ce Sarki Sanusi ya karbi nadin da gwamna ya yi masa.

    Sai dai Sarki Sanusin ya ce "yana neman karin bayani daga wurin gwamna dangane da nadin sauran 'yan majalisar da ofishin majalisar da ma'aikatan majalisa da kuma dukkanin abubuwan da ake bukata domin gudanar da majalisar."

    Duk da cewa BBC ba ta samu ji daga fadar Kano ba kan takardar, wani ma'aikacin gidan gwamnatin jihar ya tabbatar wa BBC karbar kofin takardar.

  2. UNICEF na tantance mata masu ciki a Bauchi don dakile cutar HIV

    Mata masu ciki

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da yara ta Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ta ce ta fara tantance mata masu ciki a dukkanin kananan cibiyoyin lafiya 323 na jihar Bauchi domin gano masu dauke da cutar HIV don ba su magani.

    Shugaba mai kula da ayyukan hukumar na jihar Bauchi ne Mista Bhanu Pathak ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a yau Juma'a a Abuja.

    Ya ce matakin yunkuri ne na hana yaduwar kwayar cutar ta HIV daga uwa zuwa jaririnta, ya kara da cewa "an samar da kayayyaki kyauta a kafatanin cibiyoyi 323 na lafiya a Bauchi," kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito shi yana fada.

    "UNICEF tana kuma yi wa matan gwaje-gwaje kafin haihuwa da kuma bayan haihuwa (Ante-natal da Postnatal) har ma da karbar haihuwa a cibiyoyin.

    "Wannan ya hada da yin gwajin HIV ga kowacce mai ciki sannan a bai wa wacce aka gano tana dauke da cutar maganin dakile ta domin kare jariransu kamuwa da ita."

    Pathak ya kuma jaddada cewa hukumar, a yunkurinta na girmama yarjejeniyar da ke tsakaninta da gwamnatin jihar Bauchi, ta horar da ma'aikatan sa-kai 1,200 a kan cutukan da suka shafi yara domin shiga yankunan karkara.

  3. 'Yan sanda sun tsaurara tsaro a Abuja

    'Yan sandan Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar 'yan sanda ta babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja, ta kara kaimin sintiri a birnin domin tabbatar da cewa an yi bukukuwan Kirsimati lami lafiya.

    Kwamishinan 'yan sandan birnin, Mista Bala Ciroma, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja.

    Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito shi yana cewa rundunar ta ninka yawan jami'anta da tattara bayanan sirri da kuma duba ababen hawa a kan tituna.

    Kwamishina Ciroma ya jaddada cewa ayyukansu na kakkabe masu garkuwa da mutane daga birnin na nan suna ci gaba da yi. Sannan kuma ya yi kira ga mazauna garin da su yi takatsantsan wurin daukar 'yan aikin cikin gida da direbobi da kuma masu gadi.

  4. EFCC za ta tsare Bello Adoke tsawon kwana 14

    EFCC

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, A jiya Alhamis EFCC ta cafke Adoke a Abuja

    Wata kotu ta bai wa EFCC damar tsare Mohammed Bello Adoke a hannunta har na tsawon mako biyu.

    Wannan damar na zuwa ne a yau Juma'a bayan da hukumar ta damke Adoke jim kadan bayan saukarsa a filin jirgin sama na Abuja a yammacin jiya Alhamis, inda 'yan sandan kasa-da-kasa na Interpol suka yi masa rakiya daga Dubai.

    Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa lauyan Adoke ba ya cikin zauren kotun a lokacin da aka bai wa EFCC damar.

    Mai Shari'a O.A. Musa ya bayar da umarnin a tsare tsohon ministan shari'ar na tsawon kwana 14 yayin da ake ci gaba da bincike da kuma yi masa shari'a.

    Mohammed Bello Adoke ya rike mukamin Ministan Shari'a kuma babbban lauyan Gwamnatin Tarayyar Najeriya a zamanin mulkin Goodluck Jonathan.

    Tun a shekarar 2017 ne EFCC ta fara tuhumarsa da kamfanonin mai na Malabu Oil & Gas Limited da Shell da Agip da wasu mutanen da dama da zargin almundahana a cinikin wata rijiyar man fetur.

    A ranar 17 ga watan Afrilun 2019 ne wata babbar kotu a Abuja ta bayar da umarnin cafke shi sakamakon gaza gurfana a gabanta.

  5. Direbobi na zanga-zanga a Onitsha

    Direbobin motocin tifa sun tare babban titin zuwa Enugu daga Onitsha yayin wata zanga-zangar nuna damuwa ga kudaden da ake sanya musu da suka ce sun yi yawa.

    Jaridar Vanguard ta rawaito cewa Sanata Ifeanyi Uba wanda zanga-zangar ta ritsa da shi, ya yi wa mutane dan gajeren bayani inda ya ba su hakuri amma kuma ba su hakura ba.

    Dirbobin manyan mota na yawan samun tashin hankali da jami'an tsaro

    Asalin hoton, OTHERS

  6. Za a kara kudin wutar lantarki a Najeriya

    Gwamnatin Najeriya ta ce ta shirya kara kudin wutar lantarki a dai-dai lokacin da take gab da kammala ayyuka domin samar da wutar.

    Jaridar The Nation ta rawaito ministan wutar lantarki na kasar, Engr Saleh Mamman yana cewa ba makawa sai an kara kudin wutar bisa lura da tsadar samar da wutar

    Za a kara kudin wata a Najeriya

    Asalin hoton, Getty Images

  7. Za a fara amfani da jirage maras matauka a jarrabawar JAMB

    Shugaban hukumar jarrabawar shiga manyan makarantu na Najeriya, Farfesa Ishaq Oloyede, ya ce hukumar zai fara yin amfani da jirage maras matuka a lokacin jarrabawar 2020.

    Jaridar Punch ta rawaito Farfesa Oloyede yana fadin hakan ne ranar Alhamis yayin wani taron masu ruwa da tsaki a jami'ar Ahmadu Bello da ke Kaduna.

    Oloyede ya kara da cewa suna son fito da amfani da jiragen ne maras matuka sakamakon yadda wasu mazambata suka lalata na'u'rorin daukar hoto na sirri da aka kakkafe a cibiyoyin zana jarrabawar.

    Ya kuma yi zargin hadin baki da wasu ma'aikatan hukumar ta JAMB a lalata na'u'rorin.

    Farfesa Oloyede

    Asalin hoton, JAMB

  8. Rigakafin Ebola a Kongo

    Hukumar kula da abinci da magunguna ta Amurka, FDA ta amince da maganin rigakafi na Ebola da kamfanin magunguna na Mercy, da ake amfani da shi wajen dakile cutar ta Ebola a Jamhuriyar Dimokradiyar Kongo.

    Wannan ne dai rigakafin farko da hukumar FDA ta amince da shi domin yakar cutar Ebola.

    A farkon wannan shekarar ne dai hukumar lafiya ta duniya da Tarayyar Turai su ma suka amince da rigakafin.

    Batun rigakafin dai ya zama mai cece-ku-ce inda a watan Agusta, ministan lafiyar kasar ta Kongo ya ce ana yin amfani da 'yan kasar tasa ne wajen yin gwaji.

    Sai dai masana sun ce ana yin irin wannan gwajin ne a wurin da cutar ta barke.

    An bai wa kimanin mutum 150,000 rigakafin cutar ta Ebola kuma kaso 97 sun samu lafiya.

    Congo
  9. Ganduje ya nemi Sarki Sanusi ya amince ko watsi da mukamin shugaban majalisar sarakuna

    Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya bai wa Sarki Sanusi kwana biyu kacal da ko dai ya amince da nadin da gwamnan ya yi masa a matsayin shugaban majalisar sarakunan jihar Kano ko kuma ya yi watsi da shi.

    A wata takarda mai dauke da sa hannun babban sakataren ayyuka na musamman na jihar Kano, Musa Yahya Bichi wadda kuma ke dauke da kwanan watan 19 ga Disamba, gwamna Ganduje ya nemi dole martanin Sarkin ya kai gare shi a cikin kwanaki biyu da karbar wannan takarda.

    A lokacin da gwamna Ganduje ya yi nadin dai ya shaida wa sarakuna guda biyar na jihar cewa duk sarkin da ya ki halartar taron sarakuna sau uku ba tare da wani kwakkwaran dalili ba to za a ladabtar da shi ta hanyoyi da dama cikin har da tsigewa.

    Sai dai wasu na makusantan Sarki Sanusi sun ce Sarkin bai yi ido biyu da takardar nadin ba ballantana ya mayar amince ko ya yi watsi da mukamin na shugaban majalisar sarakuna.

    Wannan dai takarda na zuwa ne kwana daya bayan da Sarki Sanusi da sauran sarakunan guda biyar suka hadu da juna a karon farko.

    Takardar da ta nemi

    Asalin hoton, KNSG

    Sarki Snausi da Gwamna Ganduje

    Asalin hoton, Mai katanga

    Buhari yana gaisa wa da Sarki Sanusi

    Asalin hoton, Fadar shugaban kasa

  10. Yadda EFCC ta cafke Adoke bayan sauka daga jirgin Dubai

    Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta cafke tsohon ministan shari'ar Najeriya Mohammed Bello Adoke jim kadan bayan saukarsa a kasar daga Dubai.

    Kamar yadda hukumar ta sanar, 'yan sandan kasa-da-kasa na Interpol ne suka taso keyar Adoke tare da yi masa rakiya har Abuja.

    "Shugaban EFCC Ibrahim Magu da kuma mahukuntan Dubai sun dade suna tattaunawa game da tsohon ministan shari'ar," in ji EFCC.

    Tun a safiyar ranar Alhamis ne aka samu rahoton isowar Bello Adoke Najeriya , inda jami'an EFCC suka yi jiran saukarsa a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja.

    Mohammed Bello Adoke ne Ministan Shari'a kuma babbban lauyan Gwamnatin Tarayyar Najeriya a zamanin mulkin Goodluck Jonathan.

    Tun a shekarar 2017 ne EFCC ta fara tuhumar Adoke da kamfanonin mai na Malabu Oil & Gas Limited da Shell da Agip da wasu mutanen da dama da zargin almundahana.

    A ranar 17 ga watan Afrilun 2019 ne wata babbar kotu a Abuja ta bayar da umarnin cafke shi sakamakon gaza gurfana a gabanta.

    Mohammed Bello Adoke

    Asalin hoton, EFCC

  11. 'Babu wata doka da ta haramta wa mata zaman kansu'

    Wata kotu a Najeriya ta yanke hukuncin cewa 'karuwanci' ba laifi ne kasancewar babu wata doka da ta haramta shi.

    Mai shari'a Binta Nyako ta babbar kotu a Abuja, ta nemi a biya diyya ga mata 16 da aka kama bisa tuhumar 'karuwanci' a 2017.

    Wannan ne karon farko da wata kotu a Najeriya ta yanke hukunci kan halascin 'karuwanci'.

    Lauyan da ke kare matan, Babatunde Jacob ya shaida wa BBC cewa kotun ta ce jami'an tsaro sun keta hakkin wadanda yake karewa kasancewar sun kutsa cikin gidajensu suka kuma kama su bisa zargin karuwanci.

    Masana shari'a dai a kasar na ganin wannan hukunci ka iya yin tasiri ga 'yan Najeriya wadanda suka fi kowace al'umma yawa a nahiyar Afirka.

    Jami'an tsaro a Najeriya dai sun saba kama da tsare mata masu zaman kansu.

    Yayin wani samame a watan Mayu na 2019, an kama mata fiye da 60 bisa zargin yin 'karuwanci' a Abuja.

    Da dama daga cikin matan sun yi ikrarin cewa an ci zarafinsu da zamba cikin aminci sannan an kunyata su a bainar jama'a.

    Mata masu zaman kansu na yawaita a Abuja
  12. Farawa

    Masu bibiyarmu da fatan kun wayi gari lafiya. Yau take Juma'atu babbar rana. Da fatan za ku ci gaba da kasancewa da bbchausa.com domin kawo muku bayanan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Niger da Kamaru da Ghana da Chadi da ma sauran nahiyar Afirka. BBC Hausa na hangen labarai kamar yadda wannan dabba ke hangen abinci.

    Antelope

    Asalin hoton, Getty Images

  13. Mutum 51,000 sun rasa mahallansu a jihar Cross River

    Ambaliyar ruwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Cross River SEMA ta ce ambaliyar ruwa ta lalata gida 4,370 sannan ta tashi mutum 51,000 daga mahallansu a yankuna 212 na jihar.

    Daraktan hukumar Mista Princewill Ayim ya bayyana hakan ne a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN a ranar Laraba a Calabar babban birnin jihar.

    Ayim ya ce abin ya faru ne a tsakanin watannin Yuli zuwa Satumba, ya kara da cewa an dauki matakin saukaka wa wadanda abin ya shafa.

    Kamar yadda ya bayyana, wasu daga cikin mutanen sun tsere ne daga gidajensu domin su tsira da rayuwarsu sannan ya bayyana kananan hukumomin Boki da Etung da Biase da Calabar ta Kudu da Calabar Municipal da Ogoja a matsayin wadanda abin ya fi shafa.

  14. Majalisa ta dage zamanta saboda mutuwar Sanata

    'Yan Majalisar Dattawa

    Asalin hoton, @NGRSenate

    Majalisar Dattawan ta dage zamanta a ranar Alhamis domin yin alhinin rasuwar shugaban kwamitin kwadago na majalisar Sanata Ben Uwajumogu har zuwa gobe Juma'a.

    Wannan ya biyo bayan wani kudiri da Shugaban Masu Rinjaye, Yahaya Abdullahi, wanda ya nemi a jingine ayar dokar majalisar ta Rule 13 da ya tanadi cewa majalisar ta kammala zamanta na rana kafin tafiya hutun Kirsimati.

    "Kamar yadda muke yi bisa al'ada, ina neman a yi shuru na minti daya domin girmama mamacin," Sanata Yahaya Abdullahi ya fada.

    Sanata Uwajumogu ya mutu ne a safiyar ranar Laraba kuma Sanata Yahaya ya kara da cewa Uwajumogu ya rasu yana da shekara 51.

  15. Gwamnatin Najeriya ta bayyana ranakun hutun Kirsimati

    Rauf Aregbesola

    Asalin hoton, @raufaregbesola

    Bayanan hoto, Ministan Cikin Gida Rauf Aregbesola ya yi kira da a zauna lafiya yayin bukukuwan

    Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranakun 25 ga watan Disamba da 26 wato Laraba da Alhamis da kuma 1 ga Janairun 2020 a matsayin hutun Kirsimati da kuma na sabuwar shekara.

    Ministan Harkoikin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da Barista Georgina Ehuriah ya fitar a madadin gwamnatin tarayya.

    Yayin da yake taya al'ummar Kiristoci da kuma 'yan Najeriya murna, ministan ya yi kira da a zauna lafiya yayin bukukuwan ta hanyar yin koyi da Yesu Al Masihu wurin kaunar juna da tausayi da kankan-da-kai da zaman lafiya.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  16. Shugaba Buhari yana ziyara a Kano

    Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya hallara a wurin taron bikin fara zangon karatun 2019/2020 na kwalejin koyon aikin 'yan sanda da ke Wudil a Kano.

    A jawabin da ya gudanar, Buhari ya ci alwashin ci gaba da yaki da ta'addanci da inganta aikin 'yan sanda tare da amfni da kwalejin ta Police Academy wurin kara habaka kwazo da dabarun aiki.

    Ya kuma ja hankalin wadanda aka yaye wajen yin aiki tukuru ta hanayar saka Najeriya a gaba da kishin kasa a kowane lokaci. Sannnan sun yi amfani da abin da suka koya wajen kare martaba da Kuma mutincin Najeriya a idon duniya.

    Shugaba Buhari
    Shugaba Muhammadu Buhari
  17. Mutum 51,000 sun rasa mahallansu a jihar Cross River

    Ambaliyar ruwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Cross River SEMA ta ce ambaliyar ruwa ta lalata gida 4,370 sannan ta tashi mutum 51,000 daga mahallansu a yankuna 212 na jihar.

    Daraktan hukumar Mista Princewill Ayim ya bayyana hakan ne a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN a ranar Laraba a Calabar babban birnin jihar.

    Ayim ya ce abin ya faru ne a tsakanin watannin Yuli zuwa Satumba, ya kara da cewa an dauki matakin saukaka wa wadanda abin ya shafa.

    Kamar yadda ya bayyana, wasu daga cikin mutanen sun tsere ne daga gidajensu domin su tsira da rayuwarsu sannan ya bayyana kananan hukumomin Boki da Etung da Biase da Calabar ta Kudu da Calabar Municipal da Ogoja a matsayin wadanda abin ya fi shafa.

  18. 'Yan sandan kasa da kasa sun saki Mohammed Adoke

    Tsohon ministan shari'a na Najeriya, Muhammed Bello Adoke ya bar Hadaddiyar Daular Larabawa zuwa Najeriya.

    Jaridar PREMIUM TIMES ta rawaito cewa Adoke ya dauki hanyar koma wa Najeriyar ne bayan da 'yan sandan kasa da kasa suka sake shi.

    Jaridar ta PREMIUM TIMES ta bayyana cewa Adoke ya hau jirgi mai lamba 785 wanda ya baro Dubai da misalin 8:00 na safe agogon Najeriya, inda ake sa ran jirgin zai sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja da misalin karfe 3:40 na rana.

    Mohammed Bello Adoke

    Asalin hoton, OTHERS

  19. Kotu ta tuhumi Uganda da gaza kama al-Bashir

    Wata kotu a Uganda ta yanke hukuncin cewa kasar ta gaza yin abin da ya kamace ta na kama tsohon shugaban Sudan Omar al-Bashir lokacin da ya ziyarci kasar a 2016 da 2017.

    Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC ce dai ta sa sammacin kama shi da zarar ya shiga Uganda.

    To sai dai Ugandar ba ta yi hakan ba lokacin al-Bashir ya ziyarci kasar karo biyu.

    Omar al-Bashir lokacin da ya kai ziyara Uganda

    Asalin hoton, Getty Images

  20. Ana bukukuwan tunbuke al-Bashir a Sudan

    A ranar Alhamis din nan ne 'yan kasar Sudan ke fara bukukuwan zagayowar rana da aka fara zanga-zangar da ta yi sanadiyyar habbare tsohon shugaban kasar, Omar al-Bashir daga mulki.

    Tashin farashin burodi ne dai ya janyo zanga-zangar a garin Atbara kafin daga bisnai ta karade sauran sassan kasar, inda kuma shugaba al-Bashir ya yi murabus a watan Afrilu bayan kwashe shekaru kusan 30 yana jan ragamar kasar.

    Gwamnatin rikon kwarya da kungiyoyin zanga-zanga ne dai suka shirya wadannan bukukuwa domin nuna godiya ga dukkanin wadanda suka yi fafutukar ganin an tunbuke shugaba al-Bashir.

    Za a gudanar da shagulgulan ne a biranen kasar, inda a birnin Khartoum jama'a za su yi dandazo a dandalin Freedom Square da ke birnin.

    Sojoji ne da gamayyar jam'iyyar adawa suka rattaba hannu kan samar da gwamnatin wucin gadi a watan Agusta, al'amarin da ya kawo karshe ci gaba da rikici duk kuwa da cewa an tunbuke al-Bashir.

    Sudan

    Asalin hoton, Getty Images