KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 21/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 21/02/2026

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Tinubu ya buƙaci a bi doka da tsari a zaɓukan Abuja

    Tinubu

    Asalin hoton, Fadar shugaban Najeriya

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci mazauna birnin Abuja su fito domin kaɗa ƙuri'un cikin tsari da bin dokokin hukumar zaɓe.

    Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar a ranar Juma'a, shugaban ƙasar ya buƙaci masu kaɗa ƙuri'a su kauce wa tayar da fitina.

    ''Shi tsarin dimokraɗiyya ana jin daɗinsa ne kawai ta hanyar kwanciyar hankali, nutsuwa da kuma mutunta juna'', in ji sanarwar.

    Haka ma shugaban ƙasar ya buƙaci hukumar INEC ta bi tsari ta hanyar tabbatar da tantance masu zaɓe a kan lokaci.

    Sannan ya yi kira ga hukumar ta tabbatar ta yi aiki da sabbin dokokin zaɓe na 2026 da aka yi wa gyaran fuska.

  2. An fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen Abuja

    Masu zaɓe

    Masu zaɓe sun fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen ƙananan hukumomin Abuja, babban birnin Najeriya.

    Kayan zabe

    Kimanin mutum miliyan 1.5 ne suka karɓi katunan zaɓe a birnin, a cewar hukumar zaɓen ƙasar.

    kayan zaɓe

    Sai dai wakilin BBC da ya zagaya wasu rumfunan ya ce ba a samu fitowar masu zaɓe yadda ya kamata ba.

    masu zaɓe

    Shugaban ƙasar Bola Tinubu dai ya yi kira ga mazauna birnin su fito domin kaɗa ƙuri'unsu a zaɓen.

    masu zaɓe
  3. Masu zaɓe na duba sunayensu a wasu rumfuna

    wasu mutane

    Masu zaɓe na ci gaba da duba sunayensu a wasu rumfunan zaɓen birnin Abuja.

    mata

    Bayanai sun nuna cewa an samu jinkirin isar jami'an zaɓe wasu rumfunan birnin Abuja.

    ma'aikatan zaɓe

    Hukumar zaɓen ƙasar ta ce mutum fiye da milyan 1.5 ne suka karɓi katunan zaɓensu a Abuja.

    Masu zaɓe

    An gudanar da zaɓen ne a ƙananna hukumomi shida na birnin.

    masu zaɓe
  4. Ana zaɓen cike gurbi a jihohin Kano da Rivers

    Abba Kabir Yusuf

    Asalin hoton, Abba Kabir Yusuf/Facebook

    Baya ga Abuja babban birnin Najeriya da ake gudanar da zaɓukan shugabannin ƙananan hukumomi, hukumar zaɓen na jagorantar zaɓukan cike gurbi a jihohin Kano da Rivers.

    A jihar Kano da ke arewa maso yammacin ƙasar ana gudanar da zaɓukan ƴanmajalisun dokokin jihar na ƙananan hukumomin Munincipal da Ungogo.

    Haka ma a jihar Rivers da ke kudu maso kudancin ƙasar, ana gudanar da zaɓukan cike gurbi na ƴanmajalisun dokokin jihar a gundumomin Ahoada East II da Khana II.

    Tuni dai Shugaba Tinubu ya yi kira ga jami'an tsaro su tabbatar da doka a zaman lafiya a lokacin zaɓukan.

  5. Hotunan yadda birnin Abuja ya zama fayau saboda zaɓe

    Titin Abuja

    Birnin Abuja ya zama fayau babu kowa sakamakon dokar taƙaita zirga-zirga da hukumomin birnin suka sanya saboda zaɓen ƙananan hukumomin birnin.

    Titin Abuja

    Tun da farko ofishin ministan babban birnin Najeriya ya fitar da wata sanarwa a ranar Alhamis, wadda a ciki ya umarci mutane su zauna a gida, in ba waɗanda aikinsu ya zama dole ba.

    Abuja

    Yau ne dai ake gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin birnin shida da kansilolinsu.

    Abuja

    Kasuwanni da sauran harkokin yau da kullum sun kasance a rufe.

    Abuja
  6. Trump ya ce zai ci gaba amfani da wani haraji da ya laftawa ƙasashe

    Trump

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaba Trump ya bayyana wani sabon shiri na ci gaba amfani da wani haraji da ya laftawa ƙasashen duniya bayan da Kotun Koli ta soke yawancin waɗanda ya sanya a baya, da ta kira haramtattu.

    Mista Trump ya soki hukuncin da kakkausar murya, inda ya ce a yanzu zai sake gabatar da harajin kashi goma cikin 100 kan ƙasashen duniya ƙarƙashin wata dokar ta daban.

    'Yan Democrat sun yi maraba da shiga tsakani na Kotun Kolin ta yi.

  7. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa-kai tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar

    Abdullahi Bello Diginza ke fstaan kun wayi gari lafiya.

    Ku ci gaba da biyo domin samun labarai da rahotonnin abubuwan da ke faruwa a fadin duniya.