Labarin wasanni daga 08 zuwa 13 ga watan Fabrairu 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Lahadi 08 zuwa 13 ga Fabrairu 2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Sterling ya koma Feyenoord zuwa karshen kakar bana, Feyenoord

    Sterling

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Tsohon ɗan wasan Chelsea da Manchester City, Raheem Sterling ya koma Feyenoord mai buga babbar gasar tamaula ta Netherlands zuwa karshen kakar bana.

    Ɗan wasan tawagar Ingila ya bar Chelsea a bana, bayan da suka amince da soke kwantiragin wata 18 da ta rage da yake karbar albashi fam 300,000 duk mako.

    Sterling, mai shekara 31 ya tattauna da ƙungiyoyi da dama kafin ya yanke shawarar buga wa Feyenoord tamaula, wadda take ta biyu a teburin Eredivisie, wadda tsohon ɗan wasan Manchester United da Arsenal, Robin Van Persie ke horar wa.

  2. Ceferin ya soki buga lik din wata kasa a kasashen waje, Uefa

    Ceferin

    Asalin hoton, EPA

    Shugaban hukumar ƙwallon kafar Turai, UEFA, Aleksander Ceferin, ya nuna adawarsa da ra’ayin buga wasannin lig a kasashen waje, yana mai cewa bai kamata lig-lig na Turai ya zubar da kima da martabarsa ba, domin biya wata bukata mara ma'ana.

    Ceferin, wanda ya yi magana kwana ɗaya bayan da UEFA ta cimma yarjejeniya da Real Madrid ta kawo karshen takaddamar shari’a kan yunkurin kafa gasar European Super League.

    Ya kuma jaddada bukatar ƙwallon kafa ta Turai ta ci gaba da kasancewa a karkashin tsari ɗaya kan matakin da lik na kasashensu zai ci gaba da zama kan turba.

    A baya an shirya wasan La Liga tsakanin Villarreal da Barcelona a Amurka, sannan a Serie A tsakanin AC Milan da Como a Australia, amma hukumomin lig din sun soki shirye-shiryen a bara.

  3. Tuchel ya tsawaita yarjejeniyar ci gaba da horar da Ingila, Ingila

    Tuchel

    Asalin hoton, Getty Images

    Thomas Tuchel ya ƙuduri aniyar ci gaba da horar da Ingila har zuwa gasar Euro 2028, bayan da ya sanya hannu kan sabuwar yarjejeniyar ci gaba da horar da tawagar, kamar yadda hukumar ƙwallon kafar kasar ta sanar ranar Alhamis.

    Tuchel, wanda ya maye gurbin Gareth Southgate a 2025, tun farko an ba shi kwantiragin wata 18 ne domin kai Ingila zuwa gasar cin kofin duniya da za a yi a bana a Amurka da Canada da kuma Mexico, amma yanzu zai jagoranci kasar har karshen gasar nahiyar Turai da Ingila za ta yi hadakar shirya wasannin tare da Ireland a 2028.

    Kocin mai shekaru 52, wanda ya taɓa horar da Paris St Germain da Chelsea da kuma Bayern Munich, an yi ta alakanta shi da zai koma horar da Manchester United.

    Ingila ta samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya cikin da yin bajinta, bayan lashe dukkan wasa takwas a rukunin 11, ta ci ƙwallo 22 ba tare da ko ɗaya ta shiga ragarta ba.

    Wasan da Ingila ta yi rashin nasara shi ne a hannun Senegal a karawar sada zumunta.

    Ana sa ran Ingila tana cikin ƙungiyoyin da ake ganin za su iya lashe kofin duniya na bana, inda za ta kara da Croatia da Ghana da kuma Panama.

  4. Sakamakon damben gargajiya daga jihar Kano, Damben Gargajiya

    Sakamakon damben gargajiya da aka buga a jiya a gidan wasa da ke Ado Bayero Square a Kano, Nigeria.

    An tashi canjaras tsakanin Ramadan Garba da Dan Tabulet.

    Shagon Bahagon Yansanda ya buge Adamu Bahagon Dage da wanda Dogon Kyallu ya mangare Dan Hausa Shagon Shamsu har ya fadi kasa wanwar.

  5. Ko Arsenal za ta kara yawan tazarar maki tsakaninta da City?, Premier League

    Arteta

    Asalin hoton, Getty Images

    Ranar Alhamis za a kammala wasan mako na 26 a Premier League, inda Brentford ke karbar bakuncin Arsenal - a wasan farko a bana da suka kara a Emirates a gasar, Arsenal ce ta yi nasara 2-0.

    Gunners ce ta daya a kan teburi da maki 56, ita kuwa Brentford mai maki 39 tana ta bakwan teburi.

    Cikin wasa 12 da Arsenal ta buga ko dai ranar Talata ko Laraba ko Alhamis a Premier League ba a doke ta, wadda ta ci tara da canjaras uku daga ciki.

    Ita kuwa Brentford wannan shi ne karo na huɗu da za ta kece raini ranar Alhamis a babbar gasar tamaula ta Ingila – ta sha kashi 2-0 a hannun Tottenham a Disambar 2021, sai ta doke Nottingham Forest 2-0 a watan Mayun 2025 da yin canjaras da Tottenham a watan jiya.

    Manchester City ta rage tazarar maki ya koma uku tsakani da Arsenal, bayan da ta doke Fulham 3-0 ranar Laraba a karawar mako na 26 a Premier League.

  6. Forest tana neman koci na huɗu, bayan korar Dyche, Nottingham Forest

    Forest

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai ƙungiyar Nottingham Forest, Evangelos Marinakis ya sallami Sean Dyche — ya zama koci na uku da aka kora a kakar nan — a wani yunƙuri na gaggawa domin kauce wa faduwa daga Premier League.

    An kori Dyche ne da sanyin safiyar Alhamis, bayan ƙungiyarsa ta tashi ba ci 0-0 da Wolves a filin City Ground ranar Laraba a Premier League, sakamakon da ya sa suke da tazarar maki uku tsakani da ƙungiyoyi uku na ƙarshen teburi.

    Ana sa ran tsohon kocin Wolverhampton, Vitor Pereira, yana cikin waɗanda ake sa ran za a damka masa aikin kociyan Forest.

    Dyche mai shekaru 54 ya yi kwana 114 a kan aikin kocin, ya bi sahun Nuno Espirito Santo da Ange Postecoglou da aka kora tun farko a kungiyar da ta faɗa rikice-rikice a City Ground.

    Dyche ya bar Fores ne bayan samun nasara biyu a wasa 10 a baya-bayan nan a gasar Premier, sannan ya samu maki biyu daga wasa biyar a jere da ta kai an kore shi.

  7. Man City ta rage tazarar maki tsakaninta da Arsenal, Premier League

    Premier League

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester City ta rage tazarar maki tsakaninta da Arsenal mai jan ragama yanzu saura uku kenan.

    Ranar Laraba, City ta doke Fulham 3-0 a wasan mako na 26 a Premier League a Etihad.

    Liverpool kuwa ta kawo karshen wasa 12 da ba a ci Sunderland ba a gida, an doke ta 1-0 a Stadium of Light.

    Sai dai har yanzu ƙungiyar Anfield tana nan a matakinta na shidan teburi.

    Nottingham Forest da Wolverhampton raba maki suka yi bayan tashi ba ci –

    Burnley ta je ta Crystal Palace 3-2 a Selhurst Park da wanda Aston Villa ta yi nasara 1-0 a kan Brighton a Villa Park

  8. Djokovic ya hakura da shiga gasar Doha Open, Ƙwallon tennis - Doha Open

    Djokovic

    Asalin hoton, Getty Images

    Novak Djokovic ya janye daga shiga gasar ƙwallon tennis ta Doha Open, saboda yana bukatar hutawa, kamar yadda masu shirya wasannin suka sanar a ranar Laraba a kafar sada zumunta ta Instagram.

    Wannan labari ya zo ne kwanaki 10 tsakani da Djokovic ya sha kashi a hannun Carlos Alcaraz a wasan karshe a Australian Open..

    Alcaraz da Jannick Sinner ne za su kasance manyan ƴan wasa biyu a gasar ta Doha a bana, babban birnin Qatar.

    Ana sa ran Djokovic zai koma buga wasa a watan Maris a gasar Indian Wells Masters 1000.

  9. , Daga Jaridu

    Gosiif

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool na kan gaba wajen farautar matashin ɗanwasan Bournemouth mai shekara Eli Junior Kroupi. (Caught Offside)

    Leeds na son lale fam miliyan 30 domin ɗauko golan Manchester City mai shekara 23 James Trafford. (Teamtalk)

    Brighton ta amince da tayin Nottingham Forest a Janairu kan ɗanwasan baya na Ingila Lewis Dunk amma ya nuna ba ya son tafiya. (Sky Sports)

    Crystal Palace ta rage farashin ɗanwasan Faransa Jean-Philippe Mateta na fam miliyan 30 yayin da Manchester United ta nuna tana so. (Football Insider)

    Manchester United da Chelsea na hamayya kan ɗanwasan baya na Tromso da Gambia Abubacarr Sedi Kinteh. (Mail)

    Juventus da duk wata ƙungiyar Serie A sai suna fuskantar cikas kan albashin ɗanwasan tsakiya na Newcastle United Sandro Tonali. Kungiyoyin Italiya ne ke farautar ɗanwasan haɗi da Manchester United da Arsenal. (The Athletic)

  10. De Zerbi da Marseille sun amince da kowa ya kama gabansa, Marseille

    De Zrbia

    Asalin hoton, Getty Images

    Roberto De Zerbi ya bar aikin kocin Marseille bayan da bangarorin biyu suka amince da katse yarjejeniyar da ke tsakaninsu.

    Ya bar ƙungiyar ta Faransa biyo bayan shan kashi da ci 5-0 a hannun Paris St-Germain, da kuma fitar da su daga Champions League bayan sun sha kashi 3-0 a wajen Club Brugge.

    De Zerbi ya karɓi jan ragamar Marseille ne kafin fara kakar 2024/25, bayan da ya bar Brighton, inda ya shafe kusan shekaru biyu yana horarwa.

    A kakar wasan da ta gabata ya kai Marseille matsayi na biyu a Ligue 1, kuma ya bar kungiyar tana matsayi na hudu a teburin gasar Faransa – da tazarar maki 12 tsakani da PSG da ke kan gaba.

  11. , Daga Jaridu

    Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗanwasan tsakiya na Nottingham Forest Morgan Gibbs-White zai bar ƙungiyar inda Aston Villa ke ganin ya dace da ita. (Teamtalk)

    Ɗanwasan baya na Ingila Harry Maguire, mai shekara 32, ga alama sai sabunta kwangilar a Manchester United. (Mail - subscription required)

    Real Madrid na neman ɗanwasan baya kuma kaftin Tottenham Cristian Romero shi take farauta. Ana kuma alaƙanta ɗanwasan na Argentina mai shekara 27 da Barcelona da Atletico Madrid. (Mundo Deportivo - in Spanish)

    Kungiyar Al-Ittihad na son ɗanwasan gaba na Liverpool da Masar Egypt Mohamed Salah a wannan bazara. (Foot Mercato - in French)

    Bayern Munich ta fara tattaunawa da ɗanwasan gaba na Ingila Harry Kane kan sabuwar yarjejeniya kuma tana da tabbacin zai sanya hannu. (Sky Sports)

  12. Ronaldo bai buga wa Al Nassr Champions League ba, Babbar gasar tamaula ta Saudiyya

    Ronaldo

    Asalin hoton, Getty Images

    Cristiano Ronaldo bai buga wa Al Nassr Champions League ba shiyyar Asia da ta je ta ci Arkadag 1-0 a Turkmenistan, amma an gan shi yana atisaye a Riyadh.

    Ana kyautata zaton cewa kyaftin din Portugal din bai ji ɗadin yadda ƙungiyar ba ta sayi sabbin ƴan wasa ba a watan Janairu.

    Ɗan ƙwallon mai shekaru 41, bai buga wasa biyu ba a babbbar gasar tamaula ta Saudiyya a karawa da Al Riyadh da kuma Al Ittihad – kuma magoya baya sun nuna goyon bayansu ta hanyar ɗaga takardu masu launin rawaya ɗauke da sunan Ronaldo da lamba bakwai a minti na bakwai a filin Al-Awwal Park ranar Juma’a.

    Ko da yake bai je wasan na Arkadag ba, amma an nuna hotunan Ronaldo yana atisaye tare da sauran ƴan wasa a Riyadh a shafin sada zumunta na Al Nassr a safiyar Laraba.

    Rahotanni sun ce Ronaldo bai ji ɗadi kan yadda Asusun Zuba Jari na Saudiyya (PIF) bai zuba jari a ƙungiyar ba lokacin da aka buɗe kasuwar sayen ƴan ƙwallo, yayin da abokan hamayyarsu Al Hilal – wadda PIF ke da kashi 75% a cikinta – ta ɗauko tsohon abokin wasansa na Real Madrid, Karim Benzema, daga Al Ittihad.

    Saudi Pro League ta gargaɗi Ronaldo da cewa “babu wani mutum – ko da ya yi fice – da zai yanke shawara fiye da ƙungiyarsa.”

    Wasan lig na gaba na Al Nassr za ta buga shi ne ranar Asabar da Al Fateh.

  13. Autan Sama'ila ya buge Tanimu a damben Kano, Damben gargajiya

    Damben Gargajiya

    Sakamakon damben gargajiya da aka buga a jiya a gidan wasa da ke Ado Bayero Square a Kano, Nigeria.

    An tashi ba kare bin damo tsakanin Gudumar Autan Mamman da Shagon Danladi - Shagon Babba da Dan Tabulet, sai dai kuma Autan Sama'ila ya buge Tanimu

  14. Bayern tana ta tattaunawa da Kane kan tsawaita yarjejeniya, Bayern Munich

    Kane

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayern Munich ta sanar cewar har yanzu tana tattaunawa da Harry Kane, domin ya tsawaita kwantiragin ci gaba da taka leda a Bundesliga - amma ba su kai ga mika masa kunshin yarjejeniya ba.

    Ƙyaftin ɗin tawagar Ingila ya ci kwallo 24 a bana a babbar gasar tamaula ta Jamus, shi ne kan gaba a Turai a yawan zazzaga kwallaye a raga kawo yanzu a kakar nan.

    Kane ya koma Bayern Munich daga Tottenham a 2023, kuma yarjejeniyarsa za ta kare a karshen kakar badi.

    Kawo yanzu Kane mai shekara 32 ya ci kwallo 123 a wasa 129 da ya buga wa Bayern Munich tun bayan da ya koma Jamus.

  15. Bergkamp ya ce babu ƙungiyoyin da za su ɓaro da Arsenal a Premier, Premier League

    Arsenal

    Asalin hoton, ge

    Dennis Bergkamp ya ce baya jin abokan hamayyar Arsenal a kokarin lashe Premier League a kakar nan za su iya mata fancale –

    amma ya jan kunnen yan wasa kada su yi sakaci da wannan babbar damar da suka samu.

    Gunners wadda za ta ziyarci Brentford a gobe Alhamis a Premier League tana jan ragamar teburi da tazarar maki shida tsakani da Manchester City,

    Arsenal ta dauki Premier League a 2003/04 – tun daga lokacin shiru kake ji.

  16. Grealish ya gama buga kakar bana, saboda jinya da zai yi, Everton

    Jack Grealish

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan da yake taka leda a Everton, Jack Grealish ya tabbatar da cewa ya gama buga wasannin bana, sakamakon tiyata da aka yi masa bayan karya kafa da ya yi – hakan komawa baye ne a fatan buga wa Ingila gasar kofin duniya da za a yi a shekarar nan.

    Mai shekara 30, wanda ke buga wasannin aro daga Manchester City, ya ji rauni a wasan da Everton ta je ta ci Aston Villa 1-0 a Villa Park a watan jiya.

    Rabon da Grealish ya buga wa Ingila tamaula tun cikin watan Oktoban 2024 karkashin Lee Carsley.

    Za a fara gasar cin kofin duniya daga 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yuli a Amurka da Canada da kuma Mexico.

  17. Watakila Man City ta rage tazarar maki tsakaninta da Arsenal, Premier League

    Haaland

    Asalin hoton, Getty Images

    A yau Laraba za a ci gaba da wasannin Premier League karawar mako na 26 da za a yi tata burza biyar.

    • Aston Villa da Brighton
    • Crystal Palace da Burnley
    • Manchester City da Fulham
    • Nottingham Forest da Wolverhampton
    • Sunderland da Liverpool.

    City tana mataki na biyu a teburi, wadda da zarar ta yi nasara za ta rage tazarar maki ya koma uku tsakani da Arsenal, wadda sai a ranar Alhamis za ta je Brentford.

    Da yake Liverpool ta ziyarci Sunderland a Stadium of Light a yau Laraba, tana bukatar maki uku a wasan nan.

    Sai dai Sunderland ba a doke ta ba a bana a gida a karawa 12 da ta yi a Premier League da cin bakwai da canjaras biyar daga ciki.

    A wasan farko da suka fuskanci juna a Anfield kunnen doki suka tashi 1-1 cikin watan Disamba.

  18. Sakamakon wasannin Premier da aka buga ranar Talata

    West Ham

    Asalin hoton, Getty Images

    West Ham taga ta leko ta koma, bayan da ta ci Manchester United 1-0 a London Stadium daga baya aka farke a karin lokacin daf da busa tashi a wasan mako na 26 a Premier League.

    Kenan sun tashi 1-1 a karawar da suka yi a Landan Stadium ranar Talata.

    Sai dai Micheal Carrick ya kasa cin wasa na biyar a jere - amma West Ham ta kara cin karo da koma baya da ci gaba da zama ta ukun karshen teburin Babbar gasar tamaula ta Ingila.

    Ita kuwa Chelsea ta barar da damar hawa mataki na hudu a teburi, bayan da ta tashi 2-2 a Stamford Bridge, ita ce ta fara zura biyu a raga daga baya aka farkesu.

    Everton rashin nasara ta yi 2-1 a gida a hannun Bournemouth da wasan da Newcastle United ta je ta doke Tottenham har gida da cin 2-1.

    Ƙungiyar da Thomas Frank ke jan ragama ta yi kasa zuwa ta 16, kuma karo na 11 tana shan kashi a Premier League a kakar nan.

  19. Tottenham ta kori Thomas Frank

    Thomas Frank

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Thomas Frank

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham ta sanar da korar mai horas da ƴanwasanta Thomas Frank.

    A cikin sanarwar da ta fitar, Tottenham ta ce "ƙungiyar ta ɗauki matakin sauya mai horas da tawagarta ta maza, saboda haka Thomas Frank zai bar ƙungiyar a yau Laraba.

    "A watan Yunin 2025 ne aka naɗa Thomas, kuma mun ci alwashin ba shi taimakon da yake buƙata domin gina makomar ƙungiyar.

    “Sai dai, sakamakon da ake samu ya sanya jagorancin ƙungiyar sun yanke shawarar cewa ana buƙatar sauyi a cikin wannan kaka.

    “A tsawon lokacin da ya kwashe a ƙungiyar, Thomas ya zama mai mayar da hankali kan aikinsa, inda ya bayar da gudumawa kan yadda za a ciyar da ƙungiyar gaba.

    “Muna gode masa bisa gudumawar da ya bayar kuma muna masa fatan alheri a gaba,” a cewar sanarwar.

  20. Duran ya koma Zenith domin buga wasannin aro a Rasha, Babbar gasar tamaula ta Saudiyya

    Duran

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗan wasan tawagar Colombia, Jhon Duran ya koma Zenit St Petersburg ta Rasha a matsayin aro daga Al-Nassr ta Saudiyya ranar Litinin, bayan da ya kammala wasannin aro a Fenerbahce.

    Wanda ya zura ƙwallo uku a wasa 17 da ya ya yi wa kasarsa, ya koma Al-Nassr daga Aston Villa a watan Janairun 2025.

    A halin yanzu Zenit na matsayi na biyu a teburin babbar gasar tamaula ta Rasha da maki 39, maki daya kacal tsakani da mai jan ragamar teburin, Krasnodar.