KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sauran sassan duniya, Asabar, 25/04/2026

Wannan shafi ne da ke kawo mulu labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sauran sassan duniya, Asabar, 25/04/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Labarai da dumi-dumi, 'Ƴanbindiga sun ƙaddamar da hare-haren haɗin gwiwa a faɗin Mali'

    Mali

    Asalin hoton, Others

    Rundunar sojin Mali ta ce ƴanbindiga sun ƙaddamar hare-haren haɗin gwiwa a faɗin ƙasar, ciki har da Bamako babban birnin ƙasar.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasar ta fitar a ranar Asabar da safe, ta ce har yanzu ana ci gaba da faɗa tsakanin sojoji da ƴanbindigar.

    ''Yanzu haka dakarun tsaronmu na fafatawa da ƴanbindigar domin daƙile hare-haren'', kamar yadda sanarwar ta bayyana.

    Shaidu sun faɗa wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa sun riƙa jin ƙarar abubuwan fashewa da asubahin ranar Asabar a yankin Kati, wani babban sansanin soji da ke wajen birnin Bamako.

    Tuni aka girke sojoji domin toshe titunan yankin.

    An kuma samu rahotonnin hare-hare a yankin Gao da ke arewa maso gabashin ƙasar da kuma yankin Sevare da ke tsakiyar ƙasar.

    Ƙasar Mali na ƙarƙashin mulkin soji, wadda Janar Assimi Goïta ke jagoranta bayan ƙwace mulki a 2020, inda ya yi alƙawarin maido da tsaro tare da kawar da ƙungiyoyin ƴanbindiga, to amma har yanzu ƙasar na ci gaba da fuskantar hare-haren ƴanbindigar.

  2. Iran ta gabatar da tayi kuma za mu duba - Trump

    Turmp

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce Iran ta gabatar da tayi, amma kuma Amurka za ta duba ta gani, ko za ta iya amincewa da tayin.

    Mista Trump ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa ''kawo yanzu ba mu san abin da tayin nasu ya ƙunsa ba''.

    Yayin zantawarsa da kamfanin dillancin labaran ta waya, bai yi cikakken bayani kan yadda tattaunawar ɓangarorin biyu za ta kasance ba.

    Sai dai ya ce tawagarsa za ta ƙulla yarjejeniya ce da ''mutanen da ke riƙe da ikon Iran a hannunsu yanzu''.

    Shugaban na Amurka ya ƙara da cewa Iran na buƙatar tattaunawa domin kawo ƙarshen yaƙin.

    Ya ƙara da cewa Iran na shirin gabatar da tayin da nufin magance buƙatun Amurka.

  3. Isra'ila da Hezbollah na zargin juna da saɓa wa yarjejeniya

    Sojojin Isra'ila da ƙungiyar Hezbollah na zargin juna da saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta taimaka aka cimma tsakaninsu.

    Rundunar IDF ta ce saɓa yarjejeniya ta baya-bayan nan da Hezbollah ta yi, shi ne tura jirage marasa matuƙa ɗauke da abin fashewa zuwa kan sojojinta a kudancin Lebanon.

    "Wannan abu ya ƙara nuna saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma'', in ji IDF, inda ta ƙara da cewa ba a samu raunuka a lamarin ba.

    A nata ɓangar, Hezbollah ta ce ta aika jiragen marasa matuƙa ne har sau biyar kan sojojin Isra'ila a ranar Juma'a, a matsayin ''martani kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wutar da sojojin Isra'ilar suka yi''.

  4. Hotunan yadda Pakistan ta tsaurara tsaro gabanin tattaunawar Iran da Amurka

    Tehran ta ce ba za ta yi tattaunawar gaba da gaba da Amurka ba, amma wakilan ƙasar na birnin Islamabad domin tattaunawa da Pakistan.

    Yanzu haka dai tawagar Amurka na kan hanyar zuwa birnin na Islamabad .

    Pakistan ta tsaurara matakan tsaro, tun bayan da Donald Trump ya ce wakilansa za su koma ƙasar domin ci gaba da tattaunawar.

    Ga wasu daga cikin hotunan yadda ƙasar ta tsaurara tsaro a wannan safiya.

    jami'an tsaro a gaban shingen da suka kafa

    Asalin hoton, Reuters

    Hotunan jami'an tsrao

    Asalin hoton, AFP VIA getty

    Hoto

    Asalin hoton, AFP VIA GETTY

  5. Tawagar Iran ta gana da babban hafsan tsaron Pakistan

    Tawagar Iran

    Asalin hoton, Iranian Ministry of Foreign Affairs

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi na ganawa da babban hafsan tsaron Pakistan, Field Marshal Asim Munir.

    Araghchi ya ce bayan ganawar ta Pakistan, zai kuma yi bulaguro zuwa ƙasashen Oman da Rasha.

    Makasudin ganawar, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, shi ne ''tattaunawa da ƙawayenmu kan abubuwan da suka shafi ƙawance da ci gaban yankinmu.''

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin wannan shafi na kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku domin kawo muku halin da duniya ke ciki musamman batun ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙin Iran.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.