Labarin wasanni daga 9 zuwa 15 ga watan Agustan 2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Asabar 9 zuwa 15 ga watan Agustan 2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail da Abdulrazzaq Kumo

  1. Iyalan Digo Jota za su halarci wasan Liverpool na farko a Premier League

    Diogo

    Asalin hoton, Getty Images

    Iyalan tsohon ɗanwasan Liverpool da ya rasu a haɗarin mota, Diogo Jota za su hallara a filin wasan ƙungiyar domin kallon wasanta na farko a gasar premier league ta bana da za a fara a yau Juma,a, 15 ga watan Agusta, wanda ƙungiyar za ta fafata da ƙungiyar Bournemouth a gida.

    Iyalan mamacin za su halarci wasan ne domin karramawa ta musamman da za a yi wa tsohon ɗanwasan na gaba kafin fara wasan.

    Diogo ya rasu ne yana da shekara 28 a haɗarin mota a Spain tare da ƙaninsa, Andre Silva mai shekara 25.

    A game da shirin da suka yi, kocin ƙungiyar Arne Slot ya ce, "mun san tunawa kafin wasan zai ɗaga hankali matuƙa saboda wasan ne zai zama na farko a gasar tun bayan mutuwar Digo Dalot da Andre.

    "Ina da yaƙinin cewa matar Diogo da yaransa da sauran ƴanuwansu za su halarci wasan na farko, kuma za mu yi amfani da damar wajen nuna musu ƙauna da goyon baya."

  2. Tottenham ta yi tir da masu yi wa ɗanwasanta Tel kalaman wariya

    Mathys Tel

    Asalin hoton, Getty Images

    Tottenham ta ce "ba ta ji daɗi ba" game da kalaman wariya da aka yi wa ɗanwasan gabanta Mathys Tel bayan doke su da PSG ta yi a wasan ƙarshe na gasar Uefa Super Cup ranar Laraba.

    Ƙungiyar ta yi rashin nasara 4-3 a bugun finareti bayan ta kasa kare ƙwallo biyu da ta ci PSG ɗin.

    Ta ce waɗanda suka tura wa Tel kalaman cin zarafi a shafukan sada zumunta "matsorata ne kawai".

    Tel mai shekara 20 ya shiga wasan daga benci a minti na 79 kuma yana cikin 'yanwasan na Spurs biyu da suka ɓarar da finaretin.

    "Mathys ya nuna jajircewa da ƙoƙari da ya buga finaretin, amma masu zaginsa ba wasu ba ne illa matsorata," a cewar Tottenham cikin wata sanarwa.

    "Za mu haɗa kai da jami'an tsaro da shafukan sada zumuntar domin ɗaukar tsattsauran mataki kan duk wanda muka iya ganowa."

  3. Liverpool ta amince da sayen ɗanwasan baya Giovanni Leoni

    Giovanni Leoni

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool ta amince da ɗaukar ɗanwasan baya Giovanni Leoni daga kulob ɗin Parma, kamar yadda kociyan Liverpool ɗin Arne Slot ya bayyana.

    Slot ya daɗe yana neman matashin mai shekara 18 kuma yanzu ya samu abin da yake so kan kuɗi kusan fan miliyan 26.

    Ɗanwasan na tawagar Italiya ya fara taka leda a matsayin ƙwararre a ƙungiyar Padova, da kuma zama na ɗan lokaci a Sampdoria kafin ya koma Parma a shekarar da ta gabata.

    Ya buga wasa 17 a gasar Serie A da ta gabata, wadda Parma ta ƙare a mataki na 16.

    Ƙungiyoyin sun amince da cinikin amma bai saka hannu kan wata yarjejeniya ba tukunna. Da zarar ya yi hakan, zan bayar da ƙarin bayani," a cewar Slot.

    Sai dai kocin ya ƙi yarda ya yi wani ƙarin bayani game da shirinsu na sayen Marc Guehi daga Crystal Palace, yana mai cewa "ba ɗanwasanmu ba ne".

  4. United ba ta matsa wa Hojlund sai ya bar ƙungiyar ba

    Hojlund

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester United ba ta matsanta wa Rasmus Hojlund sai ya bar Old Trafford ba, amma za ta taimaka masa ya koma wata ƙungiyar idan yana da sha'awar hakan.

    Tun bayan da Hojlund ya gana da ƴan jarida a Chicago, bayan cin Bournemouth a wasan sada zumunta ya sanar yana son ci gaba da taka leda a United.

    Tuni United ta sayi Benjamin Sesko daga RB Leipzig kan fam miliyan 73.7 hakan ya sa Hojlund ya ɗumama benci a wasan da ƙungiyar ta yi da Fiorentina.

    Wata majiya ta ce tuni an sanar da Hojlund cewar United ba za ta yi amfani da shi ba a kakar nan, bayan da ta kashe sama da fam miliyan 200 wajen sayen masu buga gurbin cin ƙwallaye.

    AC Milan tana daga cikin ƙungiyar dake son karɓar aron mai shekara 22 da fatan zai sake komawa kan ganiya nan gaba.

  5. Carragher ya ja kunnen Liverpool kan sayen ƴan wasa barkatai

    Liverpool

    Asalin hoton, Getty Images

    Jamie Carragher ya ja kunnen Liverpool kan yawan kashe kuɗi da take wajen sayen ƴan wasa da cewar hakan ba shi ne tabbas ba da za ta samu damar lashe Premier League ba.

    Kawo yanzu Arne Slot ya ɗauki ƴan wasa biyar kan fara kakar bana da ya haɗa da Florian Wirtz da Milos Kerkez da Hugo Ekitike da Jeremie Frimpong da Armin Pecsi, haka kuma tana yin zawarcin Alexander Isak daga Newcastle United.

    Haka kuma ƙungiyar Anfield na fatan kammala cinikin mai tsaron bayan Crystal Palace, Marc Guehi, sai dai tsohon ɗan wasan ya ce ya kamata Liverpool ta yi taka tsan-tsan kada ta faɗa rudani a bana.

    Liverpool ce ta lashe Premier League a kakar da ta wuce na 20 jimilla irin yawan na Manchester United.

  6. , Fulham za ta sayi Kevin daga Shakhtar

    Kevin

    Asalin hoton, Getty Images

    Fulham ta tuntuɓi Shakhtar Donetsk, domin a sayar mata da ɗan wasan Brazil, Kevin.

    Ana sa ran ƙudin sayen matashin mai shekara 22 zai haura wanda ta ɗauki Emile Smith Rowa daga Arsenal kan fam miliyan 34 a bara a matakin mafi tsada a ƙungiyar.

    Marco Silva na fatan sayen mai buga gaba daga gefe, yana kuma fatan sake ɗaukar Reiss Nelson daga Arsenal, bayan da William ya bar Fulham a karo na biyu.

    Kawo yanzu Kevin ya ci ƙwallo biyu ya bayar da biyu aka zura a raga a wasa uku a neman cike gurbin shiga Europa League - wanda ya ci ƙwallo tara da bayar da huɗu aka zura a raga a karawa 35 a dukkan fafatawa a kakar 2024-25.

  7. Liverpool na shirin sayen Leoni daga Parma

    Giovani

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool na fatan sayen matashin ɗan wasa mai shekara 18 mai tsaron bayan Parma, Giovanni Leoni.

    Leoni yana buga wa tawagar Italia ta matasa ƴan kasa da shekara 19.

    Ya fara taka leda a Padova da Sampdoria daga nan ya koma Parma a bara.

  8. Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool ba ta da niyyar siyar da dan wasan baya na Faransa Ibrahima Konate, mai shekara 26, a wannan kasuwar musayar 'yan wasan, duk da kokarin da take yi na daukar 'yan wasan baya biyu don karfafa tawagarta.(Mail - subscription required)

    Bournemouth ta cimma yarjejeniya da Bayer Leverkusen kan dan wasan gaban Morocco Amine Adli mai shekaru 25. (Footmercato - in French)

    Bayer Leverkusen ita ce kungiyar ta baya-bayan nan da ta nuna sha'awarta kan Facundo Buonanotte na Brighton, inda Seagulls a shirye ta ke ta siyar da dan wasan na Argentina mai kai hari, mai shekara 20 a kan fam miliyan 39.(Kicker - in German)

    Borussia Dortmund ta fice daga cinikin Fabio Silva bayan Wolves ta kara farashin dan wasan gaba na kasar Portugal mai shekara 23.(Teamtalk)

    Dan wasan gaban Chelsea dan kasar Faransa, Christopher Nkunku, yana sha'awar komawa Bayern Munich, inda aka akwai yuwuwar cinikin dan wasan mai shekaru 27. (Florian Plettenberg)

  9. Liverpool na son sayen ɗan wasan Palace, Guehi

    Guehi

    Asalin hoton, Getty Images

    Liverpool na tattaunawa domin sayen dan wasan Crystal Palace, Marc Guehi a kakar nan.

    Ƙyaftin na Palace yana da sauran yarjejeniyar kaka ɗaya a ƙungiyar.

    Wata majiya ta sanar da BBC cewar Liverpool na fatan kammala sayen ɗan wasan mai shekara 25 kafin a rufe kasuwar cinikayyar ƴan ƙwallo ranar 1 ga weatan Satumba.

    Palace tana sa ran sayar da Guehi kan fam miliyan 40, wanda kwantiraginsa zai kare a karshen kakar bana.

  10. Roma na son yin zawarcin Sancho na Manchester United

    Sancho

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Roma mai buga Serie A na son yin zawarcin Sancho na Manchester United.

    Ita dai United na son sayar da ɗan ƙwallon tawagar Ingila, wanda ya koma United a karshen kakar da ta wuce, bayan kammala wasannin aro a Chelsea, wadda tun farko aka ce ta sayi Sancho kan fam miliyan 5, amma hakan bai yiwuba.

    Tun farko Juventus ta daɗe tana son sayen tsohon dan wasan Borussia Dortmund.

  11. Gossip

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester City na tattaunawa da Paris St-Germain kan cinikin golan Italiya Gianluigi Donnarumma, mai shekara 26, kuma ana ganin wasu bukatunsa ba za su kawo cikas ba. (RMC Sport - in French)

    Galatasaray ta nemi golan Manchester City dan kasar Brazil Ederson, mai shekara 3, wanda zai ba Donnarumma damar komawa filin wasa na Etihad. (Fabrizio Romano)

    Southampton ta ki watsi da tayin farko da West Ham ta yi, wanda ya zarce fam miliyan 30, kan dan wasan tsakiyar Portugal, Mateus Fernandes, mai shekara 21. (Athletic - subscription required)

    Real Madrid na ci gaba da sanya ido kan dan wasan Crystal Palace dan kasar Ingila Adam Wharton, mai shekara 21 (Mail - subscription required)

  12. Za a auna koshin lafiyar Calvert-Lewin a Leeds

    Lewin

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon ɗan wasan Everton, Dominic Calvert-Lewin zai je Leeds United domin a auna koshin lafiyarsa, bayan da ya amince zai koma a matakin mara yarjejiya da wata ƙungiyar.

    Mai shekara 28 ya kammala kwantiragin kaka tara a Everton a watan Yuni.

    Calvert-Lewin ya ci ƙwallo 71 a wasa 273 a Everton, bayan da ya koma ƙungiyar daga Sheffield United kan fam miliyan 1.5 a 2016.

    Calvert-Lewin ya yi fama da jinya, ya ci wa tawagar Ingila ƙwallo huɗu, sai dai rabon da ya taka mata leda tun 2021.

  13. Newcastle United ta ɗauki Thiaw daga AC Milan

    Thiew

    Asalin hoton, Getty Images

    Newcastle United ta kammala sayen mai tsaron bayan AC Milan Malick Thiaw.

    Ɗan ƙwallon tawagar Jamus ya koma St James Park kan fam miliyan 34.6 kamar yadda rahotanni ke cewa.

    Shi ne na uku da Newcastle ta ɗauka a bana kawo yanzu, bayan Anthony Elanga daga Nottingham Forest da mai tsare raga, Aaron Ramsdale da zai buga wasannin aro daga Southampton.

    Thiaw, wanda ya buga wa tawagar Jamus wasa ukui, ya koma AC Milan daga Schalke a 2022.

    Ya buga wasa 31 a dukkan karawa a ƙungiyar dake buga Serie A a kakar da ta wuce da cin ƙwallo ɗaya a karawa da Real Madrid a Champions League cikin watan Nuwamba.

    Newcastle za ta fara wasan makon farko a Premier League ranar Asabar da ziyartar Aston Villa.

  14. Za a fara Premier League ranar Asabar

    Transfer

    Asalin hoton, Getty Images

    Ranar Asabar 16 ga watan Agusta za a fara gasar Premier League kakar 2025/26 tsakanin ƙungiya 20.

    Liverpool ce ke rike da kofin kakar da aka kammala, kuma na 20 jimilla da take da shi irin yawan na Manchester United.

    Tuni ƙungiyoyin da za su buga gasar ke ta yin cefane, domin ganin sun taka rawar gani a bana.

  15. Na kusa komawa Manchester United a 2012 - Lewandowski

    Lewa

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya ce a shekarun baya saura ƙiris ya koma ƙungiyar Manchester United ta Ingila.

    "Manchester United ta nemi ni, har na amince. A lokacin ina a burin komawa ƙungiyar ne domin aiki da fitaccen koci, Alex Ferguson."

    Lewandowski ya ce lamarin ya faru ne a shekarar 2012, a lokacin da yake ganiyarsa sosai a ƙungiyar Borussia Dortmund ta Jamus.

    A cewarsa, "Dortmund ce ta hana ni komawa saboda a lokacin ba su shirya rabuwa da ni. Sun yi tunanin idan na ƙara tsayawa, zan ƙara daraja kuma za su samu ƙarin kuɗi. Amma lallai ni a lokacin har na amince da tayin Man United," in ji shi.

    Lewasdowski mai shekara 37 a yanzu, ya lashe kofuna da dama a ƙungiyoyin Bayern Munich da Barcelona inda yake cigaba da taka leda a yanzu.

  16. Isak ya dage sai ya koma Liverpool

    Isak

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar ƙungiyar Newcastle domin komawa Liverpool da taka leda a kakar baɗi.

    BBC Sport ta kalato daga majiyoyi da dama cewa ɗanwasan ɗan asalin ƙasar Sweden ya riga ya ƙudurci burin komawa Liverpool kafin kakar baɗi kafin a rufe kasuwar hada-hadar ƴanwasanni a ranar 1 ga Satumba.

    Tun da farko dai ƙungiyar Newcastle ta ƙi amincewa da tayin fam miliyan 110, lamarin da ya sa Liverpool ta yi barazanar ficewa da zawarcin ɗanwasan.

    Kocin ƙungiyar, Eddie Howe ya bayyana cewa, "mun fahimci cewa Isak ya fi sha'awar tafiya wata ƙungiyar," in ji shi, sannan ya ƙara da cewa ba zai ƙirga shi a cikin ƴanwasansa ba.

    Ana dai sa ran Isak ba zai buga wasan farko na ƙungiyar, wanda za ta kara da Aston Villa ba a ranar Asabar mai zuwa.

  17. Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun saya ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

    Sadiq

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded ta Spain, Sadiq Umar da ɗanmajalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kaduna ta arewa, Bello El-Rufai sun haɗa hannu domin mallakar ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna.

    Ƙungiyar Rancher Bees, daɗaɗɗiyar ƙungiya ce mai tarihi a jihar Kaduna, da ta yi tashe a arewacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya a shekarun baya, amma sai ta samu koma-baya, har aka daina maganarta.

    A wata sanarwa da ya fitar, Sadiq Umar ya bayyana farin cikinsa kan mallakar ƙungiyar, wadda ya ce za su iya ƙoƙarinsu domin dawo da martabarta.

    Ya ce, "zan haɗa hannu da Bello El-Rufai domin dawo da martabar ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna. Na taso ina kallon ƙungiyar nan, wadda ta fitar da zaratan ƴanƙwallo da suka yi fice a duniya. Wannan abun farin ciki ne a gare mu," in ji Sadiq Umar.

    Ya ce babban burinsu shi ne ganin ƙungiyar ta koma gasar firimiyar Najeriya, "ina farin cikin irin murnar da na ga magoya bayan ƙungiyar sun fara nunawa da ma mutanen Kaduna. Za mu dawo da harkokin wasa sosai a Kaduna," in ji Sadiq.

    A nasa ɓangaren, Bello El-Rufai ya ce yana farin cikin sa hannu a yunƙurin dawo da martabar ƙungiyar, lamarin da ya ce zai yi iya ƙoƙarinsa domin samun nasara,

  18. Akwai yiwuwar Barcelona da Villareal za su buga wasan La Liga a Amurka

    Barcelona da Villareal

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya ta amince a buga karawar Villareal da Barcelona a gasar La Liga a filin wasa na Hardrock da ke birnin Miami a Amurka a watan Disamba.

    Duk da haka, akwai buƙatar samun amincewa daga hukumar ƙwallon ƙafa ta Turai uefa, da hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA da sauran hukumomi.

    Idan hakan ya faru, wannan zai zama karon farko a tarihi da za a buga wani wasan gasar lig a wata ƙasa daban.

    A halin yanzu dai dokar hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA ta hana faruwar hakan amma a sherarar da ta gabata ta kafa kwamitin da zai duba lamarin.

  19. Kano Pillars ta lallasa Katsina United

    Kano Pillars

    Asalin hoton, Kano Pillars

    Kano Pillars ta lallasa Katsina United da ci 3-0 a wasan kusa da na ƙarshe na gasar wasannin share fage ta Gusau/Ahlan.

    Auwalu Ali Malam da Umar Sani Yakasai da Chiedozie Jude Okorie ne suka zura ƙwallo a wasan da aka buga a filin wasa na Lafia City da ke jihar Nasarawa.

    Ana buga gasar ne a cikin shirye-shiryen Premier League ta Najeriya mai zuwa da za a fara ranar 22 ga watan Agusta.

  20. Sunderland na shirin sayen ɗan wasa na 11

    Omar Alderete

    Asalin hoton, Getty Images

    Sunderland na shirin sayen ɗan wasan baya Omar Alderete daga Getafe ta sifaniya kan fam milian 10.

    Ɗan wasan mai shekara 28 zai yi gwajin lafiya sannan ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekara huɗu a ƙungiyar.

    Idan aka kammala cinkin, Alderete ɗan ƙasar Paraguay zai zama ɗan wasa na 11 da Sunderland ke saya kuma za ta kashe fam miliyan 150 kan sayen ƴan wasa ke nan.

    Cikin ƴan wasan da ta saya akwai Granit Xhaka da Simon Adingra, amma ta rabu da Jobe Bellingham da Tom Watson kan fam miliyan 37.