Jamal Musiala ya sake faduwa a fili karo na biyu a kwana huɗu

Asalin hoton, Getty Images
Bayern Munich ta bayyana cewa Jamal Musiala zai yi magana da kansa bayan da ɗan wasan tsakiyar Jamus ya faɗi a fili yayin wasa karo na biyu cikin kwanaki huɗu.
A ranar Talata, Musiala ya faɗi mintuna shida kacal bayan da ya shiga fili daga benci, a wasan sada zumunta da Bayern Munich ta doke Heidenheim da ci 4-2.
Ɗan wasan mai shekaru 23 ya bayyana kamar yana cikin ruɗani yayin da ma’aikatan lafiya suka ba shi kulawa kafin daga bisani aka taimaka masa wajen fita daga filin wasan.
Lamarin ya faru ne bayan ya kuma faɗi a wasan sada zumunta da Bayern ta doke RB Leipzig 3-1 a Munich ranar Asabar.
Da yake magana ranar Talata, daraktan wasanni na Bayern Munich, Max Eberl, ya ce:
"Jamal zai yi magana game da wannan nan ba da jimawa ba. Mun san abin da ya faru kuma muna da cikakken bayani kan halin da ake ciki."
"Jamal zai yi magana da kansa. Yana cikin ɗakin canza kaya a yanzu, yana shirin canzawa da yin wanka."
An yi zaton cewa tsananin zafi ya taka rawa a faɗuwar da Musiala ya yi ranar Asabar, inda yanayin zafin ya haura digiri 30 na Celsius.
Musiala ya rasa watanni shida na farkon kakar wasan da ta gabata bayan ya karya ƙafarsa a gasar Kofin Duniya na Kungiyoyi ta 2025. Sai dai ya dawo taka leda a rabin na biyu na kakar, sannan ya fara wasa a uku cikin wasanni huɗu da Jamus ta buga a Kofin Duniya na 2026.
Har yanzu Bayern Munich ba ta bayyana cikakken bayani kan musabbabin faɗuwar Musiala ba, amma ana sa ran ɗan wasan zai yi karin haske game da lamarin nan gaba kaɗan.
















