KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 23 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

  1. AU ta yi allawadai da kisan fiye da mutum 50 a Zamfara

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta yi allawadai da abin da ta kira munanan hare-haren ƴan bindiga da aka kai a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, inda aka kashe fiye da fararen hula 50 tare da sace mata da yara da dama.

    A sanarwar da shugaban hukumar ƙungiyar, Mahmoud Ali Youssouf ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana harin a matsayin babban take hakkin bil’adama da kuma barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

    Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru ne a ƙauyen Dutsin Dan Ajiya da ke ƙaramar hukumar Anka, inda ‘yan bindiga sama da 150 suka mamaye garin da yamma a kan babura

    Sun kuma tare hanyoyin shiga da fita domin hana mutane tserewa sannan suka riƙa harbi ba tare da kakkautawa ba kafin nan suka ƙone gidaje.

    Majiyoyin yankin sun ce maharan sun shafe sa’o’i suna kai farmaki tun daga daren Alhamis har zuwa safiyar Juma’a.

    Wasu mazauna sun bayyana cewa sun sanar da jami’an tsaro tun da suka hango maharan na tahowa, amma ba su samu ɗauki cikin lokaci ba.

    Ƙungiyar ta nuna cikakken goyon baya ga gwamnatin Nijeriya da al’ummarta, tare da jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu da kuma yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

    Ta kuma bukaci a saki mutanen da aka sace nan take ba tare da wani sharaɗi ba, tare da kira ga ƙarin haɗin gwiwar tsaro domin kare jama’a da hana sake aukuwar irin waɗannan hare-hare.

    Zuwa yanzu dai gwamnatin Nijeriya ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

  2. PDP za ta kai APC kotu kan zaɓen Abuja

    ....

    Asalin hoton, PDP

    Jam’iyyar PDP ta sanar da kafa wata ƙungiyar lauyoyi ta musamman domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a yankunan babban birnin tarayya, Abuja.

    Matakin na zuwa ne bayan sakamakon da INEC ta bayyana ya nuna cewa ‘yan takarar APC sun lashe kujerun shugabancin ƙananan hukumomi biyar cikin shida.

    APC ta yi nasara a ƙananan hukumomin Abaji da ƙaramar hukumar birni wato AMAC da Bwari Kwali da Kuje, yayin da PDP ta samu nasara a Gwagwalada kaɗai. An gudanar da zaɓen ne domin cike kujerun shugabanni shida da na kansiloli 62.

    Jam’iyyar ta ce zaɓen ya gudana cikin yanayi na rashin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da kuma rahotannin sayen ƙuri’u.

    A sanarwar da sakataren yaɗa labaranta na ƙasa, Ini Ememobong, ya fitar, jam’iyyar ta taya waɗanda suka yi nasara murna amma ta jaddada cewa akwai kura-kurai a sakamakon.

    Ta bayyana cewa ƙungiyar lauyoyinta za ta kasance ƙarƙashin jagorancin mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na ƙasa, Shafi Bara’u, tare da kira ga duk ‘yan takarar da ke da ƙorafi su gaggauta gabatar da su domin ɗaukar mataki.

  3. EFCC ta kama mutum 20 bisa zargin laifukan zaɓe a Abuja

    ...

    Asalin hoton, efcc

    Hukumar EFCC ta sanar da kama mutum 20 da ake zargi da aikata laifukan zaɓe yayin zaɓen ƙananan hukumomin babban birnin tarayya, Abuja da aka gudanar a ranar 21 ga Fabrairu, 2026.

    Ta ce an kama su ne a wurare daban daban saboda zarge zargen sayen ƙuri’u da sayar da ƙuri’u da kuma hana jami’ai aiki, inda aka gano kuɗi har Naira miliyan 17,218,700.

    A cikin sanarwar da mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale, ya fitar, an ce an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin da Naira miliyan 13,500,000 a cikin mota da aka ajiye kusa da rumfar zaɓe a yankin Kwali.

    Sanarwar ta ƙara da cewa an kama mutane biyu a Abaji, tara a Gwagwalada, huɗu a Kuje, sannan sauran huɗun a Kwali.

    Hukumar ta ce za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

    Hukumar INEC ce ta gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli a dukkan yankuna shida na FCT.

    Haka kuma an gudanar da zaɓukan cike gurbi a mazaɓun Ahoada East II da Khana II na Jihar Rivers.

    An kuma gudanar da zaɓe a mazaɓun Kano Municipal da Ungogo na Jihar Kano.

    EFCC ta jaddada cewa za ta ci gaba da sa ido domin tabbatar da gaskiya da adalci a dukkan matakan zaɓe.

  4. Putin na yunƙurin kafa sabon tsarin rayuwa a duniya - Zelensky

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya bayyana wa BBC cewa takwaransa na Rasha, Vladimir Putin, ya riga ya ƙaddamar da abin da ya kira yaƙin duniya na uku, yana mai cewa abin da ya dace a yi masa shi ne ƙara matsin lambar soji da ta tattalin arziki.

    A hirar da aka yi da shi gabanin cika shekaru huɗu da mamayar da Moscow ta kai wa ƙasarsa, Zelensky ya zargi Putin da yunƙurin kafa sabon tsarin rayuwa a duniya.

    Ya kuma yi gargaɗi cewa hare-haren ba za su tsaya kan ƙasarsa kaɗai ba idan ba a dakatar da shi ba.

    Ya ce ƙasarsa ba za ta yi rashin nasara ba domin tana yaƙi ne don kare ‘yancin cin gashin kanta. A cewarsa, duk da tsawon lokacin rikicin, har yanzu Ukraine na tsaye daram kuma ba ta rasa ikon mallakar kanta ba.

    Shugaban ya ƙara da cewa rikicin ya jawo asarar rayukan dubban daruruwan mutane, ciki har da fararen hula, tare da haddasa matsaloli ga tattalin arzikin duniya.

    Ya jaddada cewa dole ne ƙasashen duniya su ƙara haɗin kai wajen ɗaukar matakan da za su hana rikicin ya ƙara faɗaɗa, yana mai cewa matsin lamba na haɗin gwiwa shi ne hanya mafi inganci ta dakile barazanar.

  5. Mece ce makomar ‘dalaget’ bayan sauya dokar zaɓen Najeriya?

    ...

    Asalin hoton, BolaTinubu/X

    A makon da ya gabata ne, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanya hannu kan sabuwar dokar zaɓen ƙasar ta 2026, da aka yi wa gyaran fuska.

    Shugaban ya sa hannu kan dokar – wadda ta ƙunshi ƙa'idojin yin zaɓukan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomin yankin birnin tarayya.

    A lokacin sanya hannu kan dokar, Tinubu ya ce "babu batun siyasa a cikin wannan gyare-gyare, abu ne na tsari, ƙoƙari ne na cike giɓi da ƙarfafa tsari da kuma samar da tsaftatacciyar hanya ga masu tsarawa da kuma masu yin zaɓuka."

    Shugaban na Najeriya ya sanya hannu kan dokar ne bayan hargitsin da aka samu a zaurukan majalisar tarayyar ƙasar da ma zanga-zangar da ƙungiyoyin fararen hula suka yi game da gyaran da aka yi wa dokar.

    Ɗaya daga cikin manyan gyare-gyaren da aka yi wa dokokin zaɓen shi ne hanyoyin da jam'iyyu ke bi wajen zaɓen mutanen da za su tsaya musu takara a kujeru daban-daban, wato zabukan fitar da gwani.

  6. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.