Haaland Ya Soki Arsenal, Ya Ce Sun Sha Gazawa a Lokutan Baya, Premier League

Asalin hoton, Getty Images
Tauraron ɗan wasan Manchester City, Erling Haaland, ya yi wa Arsenal tuni da irin gazawar da suka yi a kakar wasanni da ta gabata da Liverpool ta lashe Premier League, bayan da ya taimaka wa kungiyarsa wajen samun muhimmiyar nasara a kan abokan hamayyarta na neman kofin Firimiya.
Dan wasan Norway ya ci kwallon na biyu da Manchester City ta doke Arsenal 2–1 a filin Etihad ranar Lahadi, hakan ya sa saura maki uku tsakanin Arsenal ta daya da kuma City ta biyu a teburin Premier League.
City na da kwantan wasa, kenan tana da damar hayewa kan teburin babbar gasar tamaula ta Ingila daga nan zai rage wasa biyar-biyar a kammala kakar bana.
Haaland ya amince cewa Arsenal ce ta fi nuna bajinta a yawancin kakar wasan nan, amma ya kara da cewa Manchester City ba za ta ja da baya ba wajen kalubalantarsu, domin hana su lashe kofin gasar Firimiya da rabon Arsenal da shi 2004.
“Mun san Arsenal kungiya ce mai karfi, amma mun ga a baya sun taba zuwa kusa ba tare da sun kai ga buri ba,” in ji Haaland bayan wasan.













