A karon farko cikin shekaru an tattauna Isra'ila da Lebanon gaba da gaba

Asalin hoton, Getty Images
Isra'ila da Lebanon sun amince su ci gaba tattaunawarsu ta kai tsaye, bayan ganawarsu ta farko ta gaba da gaba da suka yi cikin gomman shekaru, yayin yaƙin da ake yi tsakanin Isra'ila da Hezbollah.
Sai dai mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Amurka, wanda ya bayyana haka, ya ce zuwa yanzu ba a kai ga yanke shawarar lokaci da kuma inda za a yi zaman ba.
Wakiliyar Lebanon a tattaunawar ta Washington - wadda ita ce jakadiyar Lebanon din a Amurka, Nada Hamadeh Moawad, ta bayyana tattaunawar a matsayin mai amfani, yayin da takwaranta na Isra'ila, Yechiel Leiter, ya ce sun yi tattaunawa mai armashin gaske.
Sai dai babu wani ci gaba da aka samu kan batun dakatar da buɗe wuta da Lebanon ke neman a yi, inda Isra'ila ta kafe cewa lalle ilalla sai ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon ɗin wadda Iran ke marawa baya, ta zubar da makamanta.
Hezbollah dai ta yi watsi da tattaunawar.

