Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 10/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 10 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Majalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓe
  • NAFDAC ta ƙwace miliyoyin magungunan zazzaɓin cizon sauro na Bogi
  • Najeriya ba ta samu ci gaba ba a ɓangaren yaƙi da rashawa - Rahoto
  • Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da dakatarwar da majalisa ta yi wa Sanata Natasha
  • Rundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindiga
  • Majalisar Najeriya za ta yi zaman gaggawa kan gyaran dokar zaɓe
  • Ziyarar shugaban Isra'ila ta jawo zanga-zanga da kama mutane a Australia
  • Yadda APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. Fasinjoji 55 sun tsira bayan jirgin sama ya yi saukar gaggawa a cikin teku

    Starsky Airlines

    Asalin hoton, Starsky Airlines

    Wasu fasinjoji 55 na wani jirgin sama tsira da raykansu bayan jirginsu ya yi saukar gaggawa a cikin teku, jim kaɗan bayan tashi daga Mogadishu, babban birnin Somaliya.

    Ma'aikatar kula da sufurin jiragen sama ta Somaliya ta ce matuƙin jirgin na komawa ne zuwa babban filin jirgin sama lokacin da ya gano matsala a jirgin, inda ya ƙauce hanyarsa sannan ya kare cikin teku.

    Jirgin na Starsky ya yaba wa matuƙin jirgin saboda ƙoƙarinsa na karkatar da jirgin, kuma ya ce tuni ya fara bincike kan lamarin.

    Ba a dai bayyana dalilan da suka haddasa matsalar da ta kai jirgin ya yi saukar gaggawa a cikin tekun ba.

  2. Ƴan majalisar Zimbabwe na shirin tsawaita wa'adin shugaban ƙasa

    Shugaban Zimbabwe

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar ministocin Zimbabwe ta amince da wani ƙudurin doka da zai tsawaita wa'adin shugaban ƙasar daga shekara biyar zuwa bakwai.

    Dokar za ta kuma bayar da dama ƴan majalisa su zaɓi shugaban ƙasa a maimakon al'umma su yi zaɓe.

    Dokar - wadda za a buƙaci ƴan majalisa su yi muhawara kanta - za ta bai wa shugaba Emmerson Mnangagwa damar ci gaba da zama a mulki har shekarar 2030

    Sai dai Jamiyyun adawa sun soki matakin jamiyyar ZANU-PF mai mulki na tsawaita wa'adin mulkin shugaban mai ci.

  3. Abin da ya sa na ajiye shugabancin NAHCON - Abdullahi Saleh Pakistan

    Farfesa Pakistan

    Asalin hoton, NAHCON

    Tsohon shugaban hukumar Alhazan Najeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan ya bayyana dalilansa na ajiye aiki.

    Cikin sanarwarsa ta ajiye aiki da aka wallafa a shafin NAHCON, Farfesa Pakistan ya ce ya ajiye aikin en bisa dalilansa na raɗin kai.

    A ranar Litinin da maraice ne bayanai suka fara fitowa game da ajiye aikin Pakistan.

    Cikin wasiƙar ajiye aikin nasa, Farfesa Pakista ya ce ya aike wa Shugaba Tinubu wasiƙa tare da sanar da shi matakin da ya ɗauka na ajiye aiki.

    Farfesa ya gode wa shugaban ƙasar bisa ''alfarmar'' da ya ce ya ba shi na jan ramagar hukumar, alfarmar da ya ce ba zai manta da ita ba har abada.

    Pakistan ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓar ƴa'uwa da abokan arzikinsa.

    A watan Oktoban 2025 ne dai wasu jami'ai a hukumar alhazan suka yi zargin yawaitar cin hanci da rashawa a ayyukan hukumar, zargin da hukumar ta sha musantawa.

    A watan Agustan 2024 ne dai Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya naɗa Abdullahi Pakistan a matsayin sabon shugaban NAHCON, bayan sauke tsohon shugaban hukumar Jalal Arabi.

  4. Gwamnan Sokoto ya ƙaddamar da shirin Tinubu na bayar da tallafi a jihohi 10

    Gwamnan Sokoto

    Asalin hoton, Sokoto State Govt

    Gwamnatin Najeriya ta ƙaddamar da wani gagarumin rabon tallafin abinci da magunguna da abinci mai gina jiki a jihohin arewacin ƙasar 10 da ke fama da matsalolin jin kai.

    Yayin ƙaddamar da shirin Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu ya ce gwamnatin tarayya ta ɓullo da shirin domin tallafa wa al'umomin da ke fama da talauci a jihohin arewacin ƙasar 10.

    Yayin da yake jawabi a garin Kasarawa, inda aka ƙaddamar da shirin, gwamnan ya ce shirin wanda shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya ɓullo da shi, ya zo daidai da zuwan azumin watan Ramadan, lokacin da aka fi buƙatar tallafin.

    Kayan tallafi

    Asalin hoton, SokoTo State Govt

    Taron ƙaddamarwar ya samu halartar ministan ayyukan jin ƙai da kawar da talauci na ƙasa Dr. Yusuf Tanko Sununu.

    Gwamnan ya ce ƙudirin shugaban ƙasar ya yi daidai da muradin gwamnatin jihar na raba wa mabuƙata tallafi.

    Kimanin mutum 1,000 suka amfana da tallafin kamar yadda gwamnan ya bayyana.

    ''Haka a yanzu da watan Azumi ke gab da shigowa za mu raba buhunan masara da kuɗi naira 50,000 ga mutane 1,000 da suka ci gajiyar tallafin, da suka haɗa da mabuƙata da marayu da gajiyayyu da zawarawa da ƴangudun hijira da tsofaffi daga gwamnatin tarayya domin sauƙaƙa musu azumin'', in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

    Kayan tallafi

    Asalin hoton, Sokoto State Govt

    Tallafin da aka raba ya haɗa da buhunan shinkafa da jarakunan manja da man gyaɗa da wasu nau'ikan abinci masu gina jiki.

    Jihohi 10 da za su amfana da wannan tallafi sun haɗa da Borno da Adamawa da Yobe da Benue da Neja da Filato da Katsina da Zamfara da Sokoto da kuma jihar Kebbi.

  5. An soke shagali a kan Jeffrey Epstein a Masar

    Jeffrey Epstein

    Asalin hoton, US Department of Justice

    Ma'aikatar harkokin cikin gida a Masar ta ce an soke shirin yin wani shagali a gidan rawa na birnin Alkahira wanda ya ƙunshi jerin liyafa a kan mai laifin lalata Jeffrey Epstein tare da kama masu shirya ta.

    An yi ta tallata shagalin a kafafen sada zumunta da taken 'Ranar tsibirin Epstein' da kuma cewa kyauta mata za su shiga.

    Ma'aikatar ta ce an tallata shagalin ba tare da samun izinin da ya kamata ba.

    Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta wanda ya nuna wata mai fafutukar kare hakkin mata na nuna fushinta, ya janyo an yi ta sukar shagalin da aka shirya yi a yau Talata.

  6. An ji ƙarar harbe-harbe a babban gidan yarin Guinea

    Guinea

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni daga Guinea na cewa an jiyo harbe harben bindiga a babban gidan yari na ƙasar da ke babban birnin kasar Conakry.

    Mazauna yankin sun ce an yi ta harbe-harben na tsawon aƙalla mintuna talatin.

    Sun kuma ce an aika manyan motocin soji makare da jami'an tsaro da ke ɗauke da makamai, da wani mashinga zuwa yankin.

    Zuwa yanzu dai ba a san dalilin da ya sa aka yi ta harbe-harben ba.

    A watan Disambar bara ne dai aka gudanar da zaɓen shugaban kasa a Guinea da ke yammacin Afirka, inda janar Mamady Doumbuya ya yi nasara, wanda ya ƙwace ikon ƙasar a wani juyin mulki da ya yi shekaru huɗu da suka gabata.

  7. Ƴan Majalisar Burkina Faso sun goyi bayan a rusa jam’iyyun siyasa

    Majalisar riƙon ƙwarya ta Burkina Faso ta amince da dokar rusa dukkan jam’iyyun siyasa a ƙasar, matakin da ake ganin yana ƙara ƙarfafa ikon gwamnatin soji da ta karɓi mulki bayan juyin mulki.

    A zaman majalisa da aka gudanar ranar Litinin, ‘yan majalisa 69 da suka halarta sun kaɗa ƙuri’a baki ɗaya domin goyon bayan kudurin da gwamnati ta gabatar.

    Ƙudurin dokar ya kuma soke dokar da ke tsara yadda ake ba da kuɗade ga jam’iyyun siyasa da kamfen din zaɓe.

    Ministan Harkokin Cikin Gida na kasar, Émile Zerbo, ya ce an ɗauki matakin ne domin sake tsara yanayin siyasar kasa, bayan da ya zargi yawaitar jam’iyyu da haddasa rarrabuwar kai da tashin hankali a tsakanin al’umma.

    Matakin ya biyo bayan dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasa tun shekarar 2022, lokacin da sojoji suka kwace iko ta hanyar juyin mulki.

    Jim kadan bayan amincewa da ƙudurin a majalisa, Minista Zerbo ya ce jama’ar Burkina Faso za su yi maraba da wannan mataki, yana mai cewa an ɗauke shi bisa tsarin doka.

    Sai dai masana na ganin cewa wannan dokar ta buɗe wa gwamnatin soji damar gudanar da mulki ba tare da wata adawa ba, lamarin da ƙungiyoyin kare haƙƙin dan Adam da dama suka yi Allah-wadai da shi.

    A makon da ya gabata, Babban Kwamishinan Majalisar Dinkin Duniya kan Hakkin Dan Adam, Volker Türk, ya bayyana haramta jam’iyyun siyasa a matsayin mataki mara kyau, yana mai kira ga mahukunta su janye wannan hukunci.

    Ya kara da cewa maimakon haramta jam’iyyun siyasa da ɗaure mutane saboda fadin ra’ayoyinsu, ya dace gwamnati ta bude fili ga ƙungiyoyin farar hula, ciki har da kungiyoyin jin kai.

  8. Mata sun fi maza yin aikin baban-giwa a Najeriya

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani sabon bincike da hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta fitar ya nuna cewa mata a Najeriya sun fi maza nesa ba kusa ba wajen yin aikin tiƙi da kula da iyali ba tare da biyansu ba.

    Rahoton ya ce mata na shafe kusan kashi 21 cikin 100 na ranarsu, wato kusan sa'o'i biyar, suna yin irin waɗannan ayyuka, yayin da maza kuma kashi 4.1 cikin 100 ne kacal, kusan awa daya kenan suka shafewa.

    Binciken, shi ne karon farko da aka gudanar da cikakken bincike a matakin kasa don auna yadda ‘yan Najeriya ke raba lokacinsu tsakanin aikin yi da ake biya da aikin gida da kula da iyali, da kuma hutawa.

    Rahoton ya nuna cewa akwai babban giɓi tsakanin mata da maza a ɓangaren nauyin ayyukan gida, a birane da karkara baki ɗaya.

    A cewar NBS, ‘yan Najeriya masu shekaru 15 zuwa sama suna shafe kimanin kashi 12.5 cikin 100 na ranarsu, kusan awa uku kenan kan aikin gida da kula da iyali ba tare da biya ba.

    Sai dai rahoton ya nuna cewa mata ne ke ɗaukar mafi yawan wannan nauyi.

    A yankunan karkara, mata na shafe kashi 24.1 cikin 100 na lokacinsu, kusan awa shida kenan yayin da mazan karkara ke shafe kashi 3.7 cikin 100 ne kawai wajen yin aikin tiƙi.

    A birane kuwa, mata na shafe kashi 19.8 cikin 100, yayin da maza ke shafe kashi 4.3 cikin 100.

  9. Abin da Majalisar Dattawan Najeriya ta cimma a zamanta kan dokar zaɓe

    ....

    Asalin hoton, Godswill Akpabio/X

    Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da sashen dokar da ya wajabta aika sakamakon zaɓe daga rumfunan zaɓe kai-tsaye ta na'ura.

    Majalisar ta kuma ce aika sakamakon kai-tsaye ta na'ura zai kasance hanyar farko ta aika sakamakon, amma idan an samu matsalar intanet, INEC za ta yi amfani da takarda a rubuce wajen aika sakamakon kamar yadda aka saba yi a baya.

    Sanata Tahir Munguno ne ya gabatar da ƙudirin a lokacin zaman gaggawa da majalisa ta yi kan dokar, yayin da shugaban majalisar ya Godswill Akpabio ya amince da ƙudirin bayan amincewar sauran ƴanmajalisar.

    Daga nan ne kuma majalisar ta kafa kwamiti mai mambobi 12 domin yin aiki da majalisar wakilai don tsefe dokokin kamar yadda tsarin amincewa da dokoki ya tanadar.

    Majalisar ta kira zaman gaggawar ne bayan da ƙungiyoyin fararen hula da jam'iyyun hamayya suka mamaye harabar majalisar dattawan a ranar Litinin domin gudanar da zanga-zanga don nuna adawarsu kan ƙin amincewa da majalisar ta yi na wajabta aikata sakamakon zaɓe ta na'ura kai tsaye daga kowace rumfar zaɓe.

  10. Shugaban hukumar alhazan Najeriya Abdullahi Pakistan ya yi murabus

    ...

    Asalin hoton, NAHCON

    Shugaban Hukumar Alhazai a Najeriya NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya yi murabus daga muƙaminsa.

    Tun a ranar Litinin ne bayanai suka fara fitowa kan cewa shugaban ya ajiye aikinsa ne sanadiyyar wasu ƙorafe-ƙorafe da aka miƙa game da shi.

    A yau Talata ɗaya daga cikin jami'an hukumar alhazan ya tabbatar wa BBC da ajiye aikin shugaban, sai dai bai yi ƙarin haske kan dalin hakan ba.

    Bayanai sun nuna cewa wakilin kwamitin shugabancin hukumar ne ya tura ƙorafe-ƙorafe zuwa fadar shugaban ƙasa game da shugaban.

    A cikin shekaru uku zuwa huɗu da suka gabata, an rika samun sauye-sauye a shugabancin NAHCON, inda kusan shugabanni uku suka riƙe muƙamin amma suka yi murabus kafin cikar wa’adinsu.

    A shekarar 2024 ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naɗa Sheikh Abdullahi a matsayin shugaban hukumar bayan sauke tsohon shugabanta na riƙo Jalal Arabi.

    Daga bisani hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasar EFCC ta tsare tare da yin bincike kan tsohon shugaban, wanda aka zargi da almundahana.

    Hukumar ta yi iƙirarin cewa an gano kudin da yawansu ya zarta Riyal 300,000 a hannun shugaban da wasu manyan jami’an hukumar Hajjin ta Najeriya.

  11. Majalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓe

    ...

    Asalin hoton, Nigerian Senate

    Majalisar Dattawan Najeriya ta kafa kwamtin da za su yi nazari kan gyaran dokar zaɓe inda da naɗa mambobi 12 da za su yi aiki tare da Majalisar Wakilai.

    Wannan mataki ya zo ne a lokacin da majalisar ke fuskantar ƙarin matsin lamba kan amincewa da wajabcin tura sakamakon zaɓe ta na'ura kai tsaye daga rumfunan kaɗa ƙuri’a yadda mutane za su iya gani.

    Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya bayyana cewa an naɗa wadannan mambobi ne domin samar da kyakkyawar fahimta tsakanin majalisun biyu, da kuma tabbatar da cewa duk wani gyara da za a yi zai amfanar da dimokuradiyya a ƙasar.

    Ana sa ran waɗannan mambobi za su tattauna kan dukkan abubuwan da suka janyo ce-ce-ku-ce, musamman yadda za a tabbatar da gaskiya da sahihancin sakamakon zabe.

  12. Sojojin ruwan Amurka sun kashe mutum biyu a harin fataucin miyagun ƙwayoyi a tekun Pacific

    Rundunar sojin ruwan Amurka ta ce ta kai hari kan wani jirgin ruwa da ake fataucin miyagun kwayoyi a gabashin tekun Pacific, inda ta kashe mutum biyu da ke cikin jirgin.

    Rundunar ta ce ta buƙaci masu tsaron tekun akan su taya ta neman waɗanda suka tsira daga cikin jirgin.

    Aƙalla an kashe mutum 130 da ake zargi da fataucin miyagun kwayoyi a hare-hare kusan 40 da Amurkan ta kai.

    Tun da farko Amurka ta ce ta kama wani jirgin ruwan dakon mai da ke da alaka da Venezuela bayan da ta bi diddiginsa tun daga tekun yankin Karebiyan.

  13. NAFDAC ta ƙwace miliyoyin magungunan zazzaɓin cizon sauro na Bogi

    ...

    Asalin hoton, Nafdac/Facebook

    Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa, NAFDAC, ta ƙwace sama da magungunan zazzaɓin cizon sauro na bogi miliyan 10 tare da kayan kwalliya, waɗanda kimarsu ta kai kusan naira biliyan uku, a wani farmaki da ta kai kasuwar baje koli da ke jihar Lagos.

    Daraktan bincike da aiwatar da doka na NAFDAC, Dr Martins Iluyomade, ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a ofishin hukumar da ke Apapa a ranar Litinin.

    Ya ce an kai farmakin ne ƙarƙashin jagorancin shugabar hukumar, Farfesa Mojisola Adeyeye, bayan samun sahihan bayanan sirri a ranar 3 ga Fabrairu.

    A cewarsa, kayan da aka ƙwace sun haɗa da magungunan yaƙi da zazzaɓin cizon sauro da alluran cutar cerebral malaria da magungunan rigakafi da maganin tazarar haihuwa na Postinor, da Anagin kuma duk na bogi.

    Ya ƙara da cewa wasu daga cikin waɗannan magunguna an haramta amfani da su a Najeriya kusan shekaru 15 da suka wuce.

    Daraktan ya ce an adana magungunan bogin ne a wani gini mai hawa uku da aka ɓoye shi a matsayin sito na kayan gyaran mota, domin yaudarar jami’an tsaro da hukumomi.

    A yayin farmakin, an kwashe lodin manyan motoci guda takwas na magunguna da kayan kwalliya, tare da kama mutane huɗu da ake zargi da hannu a lamarin.

    Daraktan ya ce bincike na ci gaba da gudana, inda ya bayyana farmakin a matsayin ɗaya daga cikin manyan nasarorin da hukumar NAFDAC ta samu a baya-bayan nan wajen yaƙi da magungunan bogi a ƙasar.

  14. Najeriya ba ta samu ci gaba ba a ɓangaren yaƙi da rashawa - Rahoto

    ...

    Asalin hoton, PRESIDENCY NG

    Najeriya ta kare kambinta a matsayin ta 37 a cikin ƙasashen duniya masu fama da matsalar cin hanci da rashawa a duniya a shekarar da ta gabata.

    Rahoton shekara ta 2025 daga ƙungiyar yaƙi da rashawa ta Transparency Internation ya nuna cewa a tsawon shekara uku Najeriya ta kasance tana da maki 26 cikin 100.

    Hakan ya sanya Najeriya a matsayi na 142 daga cikin ƙasashe 182 da ƙungiyar ta yi nazari a kai.

    Rahoton hukumar ya nuna cewa tun daga shekara ta 2022, matsalar cin hanci ta ragu da maki biyu a Najeriya.

    Ana tantance matsayin rashawa a kowace ƙasa ne ta hanyar la'akari da makin ta suka samu, daga 0 zuwa 100.

    Maki 0 na nufin ƙasa na cikin matsanancin rashawa, yayin da maki 100 ke nufin ba ta da matsalar rashawa.

    A shekarar 2025 Najeriya ta samu maki 26 daidai da makin da ta samu a 2024, sama da abin da ta samu a 2023, lokacin da take da maki 25.

  15. Saudiyya na shirin kafa sansanin sojin ruwa a Somaliya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun bayyana cewa Somaliya da Saudiyya na cikin tattaunawa mai zurfi kan kafa sansanin sojan ruwa a arewa maso gabashin Somaliya, a daidai lokacin da ake fuskantar tashin hankali a yankin sakamakon ayyukan ‘yan tawayen Houthi a Yemen da kuma amincewar Isra’ila da Somaliland a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta.

    Rahoton gidan talabijin Aleunwan24 ya ce kafofin watsa labarai na Somaliya sun tabbatar da cewa ana tattaunawa mai nisa tsakanin Saudiyya da Somaliya kan kafa sansanin sojan ruwa a garin Las Qoray, bayan wata yarjejeniyar soji da aka ƙulla domin kare Tekun Aden da Bahar Maliya.

    Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa ta hukuma daga gwamnatocin ƙasashen biyu da ke tabbatar da wanzuwar wannan tattaunawa.

    Las Qoray, da ke yankin Sanaag na Somaliya, na kusa da mashigar Bab El Mandeb, wadda ke daga cikin hanyoyin ruwa mafi cunkoso a duniya ta zama wuri mai muhimmanci wajen sa ido da kula da zirga-zirgar jiragen ruwa, tare da tinkarar barazanar Houthi a yankin.

    A baya-bayan nan, Saudiyya da Somaliya sun sanya hannu kan wata yarjejeniya a Riyadh da nufin ƙarfafa dangantakar tsaro da soji tsakanin ƙasashen biyu.

    Masana harkokin tsaro na cewa Somaliya na ƙara karkata ga Saudiyya da Qatar a matsayin sabbin abokan hulɗar tsaro, bayan da ta soke dukkan yarjejeniyoyin tsaro da tsare-tsare da Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) a watan Janairu da ya gabata.

  16. Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da dakatarwar da majalisa ta yi wa Sanata Natasha

    ...

    Asalin hoton, Natasha Akpoti/X

    Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta tabbatar da matakin da majalisar dattawan Najeriya ta dauka na dakatar da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, bisa zargin rashin da’a, tana mai cewa Majalisar ta yi aiki ne cikin ikon da doka ta tanadar mata.

    Kotun, wadda alƙalai uku suka saurari ƙarar, ta yanke hukunci gaba ɗaya cewa babu wani take haƙƙin majalisa ko ƙundin tsarin mulki da aka yi wa Sanata Natasha sakamakon dakatarwar da aka yi mata.

    Alƙalan sun ce hujjojin da aka gabatar ba su nuna cewa an tauye mata wani haƙƙi na doka ba.

    Sai dai kotun ta soke hukuncin raina kotu da kuma tarar Naira miliyan biyar da aka yi wa Natasha wanda ya samo asali daga wasikar neman afuwa ta barkwanci da ta aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

    A hukuncin da ya jagoranta, Mai shari’a Abba Muhammed ya ce Shugaban Majalisar Dattawa bai yi kuskure ba lokacin da ya hana Sanatar damar magana a zaman majalisa na ranar 20 ga Fabrairu, 2025, kasancewar ba ta zauna a kujerar da aka ware mata ba.

    Kotun ta jaddada cewa dokokin Majalisar Dattawa sun bai wa Shugaban Majalisa ikon ware wa ‘yan majalisa kujeru, tare da tanadin cewa kowane ɗan majalisa zai yi magana ne kawai daga kujerar da aka ba shi.

    Wannan, a cewar kotun, ya sa matakin da Majalisar ta ɗauka ya kasance cikin doka da ka’ida.

  17. Rundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindiga

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin ƙasa ta Najeriya ta sanar da tura dakaru na musamman zuwa jihar Filato domin daƙile ayyukan ’yan bindiga da kuma fuskantar sabon ɓarkewar hare-haren rashin tsaro a jihar.

    Matakin ya biyo bayan amincewar da Babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayar na tura Rundunar ta musamman zuwa yankin.

    Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce, "dakarun, waɗanda tuni suka isa Jihar Filato, za su gudanar da ayyuka masu tsauri da farmaki kai tsaye domin murkushe ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka."

    Rahotanni sun nuna cewa rundunar na da horo na musamman da kayan aiki na zamani da ake sa ran za su taimaka wajen sauya yanayin tsaro a jihar.

    Yayin karɓar dakarun a hedikwatar Rundunar Soji ta 3 Division, babban kwamandan rundunar, Manjo Janar Folusho Oyinlola ya yaba da jagorancin gaggawa da Shugaban Sojin Kasa ya nuna wajen samar da muhimman kayan yaƙi da sauran kayayyakin aiki da za su ba dakarun damar aiwatar da aikinsu yadda ya kamata.

    Ya bayyana cewa wannan goyon baya zai taimaka matuƙa wajen cimma nasarar ayyukan tsaro a jihar.

    Haka kuma, ya yi kira ga al’ummar Jihar Filato da kada su firgita idan suka ga yawan motsin sojoji da manyan kayan aikin soja.

  18. Ziyarar shugaban Isra’ila ta jawo zanga-zanga da kama mutane a Australia

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaiministan Australia, Anthony Albanese, ya ce ya kadu sosai akan yadda ya ga ana tashin hankali a yayin zanga zangar nuna kin amincewa da ziyarar shugaban Isra'ila.

    'Yan sanda sun kama kusan mutane 30 a wajen zanga zangar da aka yi Sydney a jiya Litinin.

    Albanese, ya kare matakinsa na gayyatar shugaban Isra'ila, Isaac Herzog kasarsa, inda ya ce duk waɗanda ba sa son ziyarar ya kamata su bayyana dalilinsu cikin kwanciyar hankali ba wai ta hanyar tashin hankali ba.

    Herzog, ya fara ziyarar ta sa ne da zuwa bakin tekun Bondi inda aka kai harin bindigar da ya yi sanadin mutuwar Yahudawa da dama a watan Disambar daya gabata.

    Masu zanga zangar dai na zargin shugaban na Isra'ila da hannun a kisan kiyashin Gaza abin da ya musanta.

  19. Majalisar Najeriya na zama kan gyaran dokar zaɓe

    ...

    Asalin hoton, Nigeria Senate

    Majalisar Najeriya ta fara zama kan gyaran dokar zaɓe a lokacin da matsin lamba ke ƙara ƙaruwa kan ‘yan majalisa su amince da wajabcin tura sakamakon zaɓe ta na'ura kai tsaye daga rumfunan kaɗa ƙuri’a yadda mutane za su iya gani.

    Zaman ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafe da kira daga jama’a da ƙungiyoyin farar hula da jam’iyyun adawa, waɗanda ke neman a saka tilasta tura sakamakon zaɓe kai tsaye a cikin gyaran dokar zaɓen da ake ci gaba da tattaunawa a kai.

    Sanarwar kiran zaman gaggawar na kunshe ne a wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 8 ga watan Fabrairu, wadda aka rarraba wa sanatoci wanda magatakardar majalisar dattawa, Emmanuel Odo ya sanya hannu a takardar.

    A cikin wasiƙar, Odo ya ce ya ɗauki matakin ne bisa umarnin shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.

    Duk da cewa an yi gyare-gyare da dama a cikin dokar, hankalin jama’a ya fi karkata ne kan wani sashe da ya haifar da ce-ce-ku-ce, wato ƙin amincewa da wajabcin tura sakamakon zaɓe ta hanyar na'ura daga rumfunan kaɗa ƙuri’a yadda mutane za su iya gani.

  20. Yadda APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano

    ....

    Asalin hoton, BBC Collage

    Kurar rikici ta fara turnuƙewa a jam'iyyar APC mai mulki a jihar Kano, da ke arewacin Najeriya, makonni bayan sauyin sheƙar gwamna Abba Kabir Yusuf.

    An fara ganin ƙurar ne a tarukan haɗa kan 'ya'yan jam'iyyar APC tsoffi da sabbi a cikin wasu ƙananan hukumomin jihar.

    Shugabancin APC ne ya ba da umarnin gudanar da tarukan masu ruwa da tsaki na jam'iyyar a wani mataki na ɗinke duk wata ɓaraka gabanin babban zaɓen jam'iyyar da ke tafe.

    Dama dai tun da farko masana siyasa a Najeriya sun yi hasashen samun rikici a tsakanin ƴaƴan jam'iyyar APC musamman bayan shigowar gwamna Abba Kabir Yusuf.

    Rahotanni na cewa an samu musayar yawu da cecekuce a yayin taron masu ruwa da tsaki a matakin kananan hukumomi.

    Na baya-bayan nan shi ne taruka biyu da aka yi a karamar hukumar Kano Municipal inda ɓangaren da ke biyayya ga tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ƙarƙashin jagorancin Muntari Ishaq Yakasai da Baffa Babba Dan Agundi da Injiniya Sagir Koki, suka yi nasu taron.