Ƴar shekara takwas da aka yi wa fyaɗe a Bangladesh ta mutu
Jami'ai a Bangladesh sun ce yarinyar nan ƴar shekara takwas da aka yi wa fyade a lokacin da ta kai ziyara gidan ƴar uwarta ta mutu.
Likitoci sun ce yarinyar ta samu bugun zuciya ne a lokacin da ake yi mata aikin ciwon da aka ji mata.
Wannan lamari da ya faru ya janyo zanga-zanga a faɗin ƙasar inda masu zanga-zangar ke buƙatar a yi wa waɗanda aka kama da aikata wannan aika aika hukunci mai tsanani da ma yi wa duk wanda aka samu da aikata irin wannan cin zarafi ga mata hukunci.
An kama mutum huɗu da ake zargi da aikata wannan cin zarafi waɗanda wasu daga cikinsu ƴan-uwan yarinyar ne. Ƴan sanda sun dakatar da zanga-zangar a Dhaka.














