Ba za mu sake bude Hormuz ba duba da yadda aka keta yarjejeniyar tsagaita wuta - Iran

Asalin hoton, EPA
Babban mai shiga tsakani na Iran da ke tattaunawa da Amurka, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya ce ba zai yiwu a sake bude mashigar Hormuz ba, duba da yadda aka keta yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta.
Waɗannan “karya dokokin” sun hada da toshe jiragen ruwan Iran da Amurka ta yi - abin da ya ce ya jefa tattalin arzikin duniya cikin halin ƙaka-ni-ƙayi - da kuma “zafafa yaƙi” da Isra’ila ta ke yi “ta kowane ɓangare”.
A martaninsa kan Amurka da Isra'ila, Ghalibaf ya bayyana a shafinsa na X cewa "ba su cimma burinsu ta hanyar ƙarfin soji ba, kuma ba za su cimma hakan ta hanyar cin zarafi ba.
"Mafita ɗaya ita ce su mutunta ƴancin al'ummar Iran"
Ana hasashen Gahlibaf zai tattauna da mataimakin shugaban Amurka JD Vance a Pakistan a wannan makon - amma har yanzu ba a fara ba.
A daren jiya ne Donald Trump ya sanar da tsawaita wa'adin tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran da zai ƙare a yau.
A safiyar yau ne Iran ta ce ta kame wasu jiragen ruwa guda biyu da ke dakon kaya a mashigar Hormuz.












