An gargaɗi 'yan jarida kan walaƙanta baƙinsu - NBC

Asalin hoton, NBC
Hukumar kula da harkokin watsa labarai ta Najeriya ta gargaɗi masu watsa labarai da su guji cin zarafin baƙinsu yayin gudanar da shirye-shiryensu ko kuma amfani da shafukansu ta hanyar da ba ta dace ba, in da suke karya dokakin aikin, yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.
Cikin wata sanarwa, hukumar ta nuna yadda ake samun ƙaruwar karya dokar aikin jarida wanda hakan ya ci karo da ka'idojin yaɗa labarai wadda aka sabunta kashi na shida wadda ta hada da harkokin yau da gobe da na shirye-shiryen siyasa.
Ta nuna damuwa kan yadda kafafen yaɗa labarai ke sauka doron abubuwan da aka sansu akai na wayar da kan al'umma da kwarewa da yin labarai sahihai, NBC ta ce za ta ɗauki hukunci kan duk wanda ya karya dokar hukumar.
Tace dole abi a hankali yayin da ake tunkarar zaɓen 2027, a ba da bayanan da za su ƙarafafawa mutane gwiwa su kuma tabbatar da kwanciyar hanakali da haɗiin kai tsakanin al'umma.














