Najeriya na sa ido bayan abin da ya faru a Sudan
Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa tana sa ido kan lamarin da ke faruwa a Sudan bayan sojoji sun hambarar da Gwamnatin Omar al-Bashir.
Ministan harkokin wajen Najeriya Geoffrey Onyeama ya shaida cewa abinda Najeriya ta damu da shi, shi ne kada a yi rikici kuma a dawo da mulkin dimokradiya ba da dadewa ba.
Ministan ya shiadawa BBC cewa ''har yanzu muna samun labarai kan abinda ke faruwa duk da cewa ba mu da cikakkun bayanai da alkaluma amma abinda muke so a bayyane yake; abu na farko shi ne kada a yi rikici.''
















