Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida and Haruna Kakangi

  1. 'Yan sanda sun daƙile yunƙurin 'yan bindiga na tare hanyar Gusau zuwa Sokoto

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar 'yansan jihar Zamfara ta ce ta daƙile yunƙurin 'yan bindiga na tare babbar hanyar Gusau zuwa Sokoto a daidai ƙauyen Kwaren Ƙirya da ke yankin ƙaramar hukumar Maru.

    Cikin wata sanarwar da kakakin 'yan sandan jihar, ASP Yazid Abubakar, ya fitar ya ce hankula sun kwanta bayan yunƙuri 'yan bindigar na ranar Talata.

    Sanarwar ta yi watsi da jita-jitar da ake ta yaɗawa cewa a ranar Talata mahara sun rufe babbar hanyar Gusau zuwa Sokoto, tare da sace mutum 26.

    Rundunar 'yan sandan ta ce a ranar talata da safe ne jami'anta sun samu rahoton cewa mahara sun tare babbar hanyar, inda nan take rundunar ta tattara jami'anta da ke yaƙi da ayyukan masu garkuwa da mutane tare da haɗin gwiwar 'yan sandan kwantar da tarzoma zuwa wajen inda suka yi bata-kashi da maharan, inda maharan suka ranta a na kare tare da raunukan harbin bindiga..

    Haka kuma sanarwar ta ƙara da cewa labarin da ake yaɗawa cewa maharan sun sace matafiya 26 daga wasu motoci biyu a wurin, ba gaskiya ba ne.

    Rundunar ta ce tana ɗaukar matakan da suka dace don hana aukuwar makamancin wannan ala'amari.

    Jihar zamfara dai na daga cikin jihohin arewain Najeriya da ke fama da hare-haren 'yan bindiga da ke tare hanyoyin mota tare da sace fasinjoji domin neman kuɗin fansa.

  2. An buɗe wuraren ajiye kayan abinci da aka kulle a Kano

    .

    Asalin hoton, FACEBOOK/MUHUYI MAGAJI RIMIN GADO

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da karbar korafe-korafe ta jihar Kano, ce ta buɗe manya-manyan wuraren ajiya da ta kulle a baya bisa zargin an ɓoye kayan abinci.

    Hukumar ta ce ta tattauna da masu wuraren inda suka cimma matsaya a kan yadda farashi zai sauka.

    A ƙarshen mako ne hukumar ta a'Anti-corruption' ta kai samame manyan rumbunan ajiye kayan abinci da ake zargin an boye kayan abinci a sassan jihar Kano bayan ƙorafe-ƙorafen da suka ce sun karɓa daga jama’a.

    Shugaban hukumar Muhyi magaji Rimin Gado, yace bayan sun garƙame rumbunan ajiye kayan abinci a wurare daban-daban ciki har da kasuwar Dawanau a Kano, masu wuraren sun kai kansu hukumar inda suka zauna tare da cimma matsaya.

    Kawo yanzu dai an buɗe manyan rumbunan ajiya da dama bayan zaman da aka yi.

    Shugabannin kasuwannin jihar sun tabbatar wa da BBC buɗe manyan rumbunan ajiyar.

    Shugaban hukumar anti-corruption mai yaki da cin hanci a Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado yace ko yanzu sun cimma manufarsu kasancewar farashin ya fara sauka.

    Muhuyi Rimin Gado ya ƙara da cewa akwai sito-sito waɗanda suke maƙare da kayan abincin tallafi, sun kuma kyalesu bayan binciken da suka yi, ya tabbatar da cewa ba boye kayan aka yi ba, don a ci ƙazamar riba.

    Yayin da ‘yan ƙasa ke ci gaba da kiraye-kirayen a sassauta irin tsananin da ake fama da shi, hukumomi a matakai daban-daban na iƙirarin cewa suna iyakar ƙoƙarinsu wajen kyautata halin da ake ciki, amma masu nazari na cewa ya kamata gwamnati ta gaggauta shawo kan matsalar tun kafin al’amarin ya kazance.

  3. Babu gudu ba ja da baya kan zanga-zanga a Najeriya - NLC

    NLC

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugabannin ƙungiyoyin ƙwadagon ƙasa sun ce babu gudu babu ja da baya kan zanga-zanagar da suka shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.

    NLC na martani ne ga hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) bisa gargaɗin da ta yi cewa ƙungiyar ta yi dakatar da ƙudirin da ta gabatar na zanga-zangar da ta shirya gudanarwa a ranakun 27 da 28 ga watan Fabrairu.

    A baya dai hukumar ta shawarci ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC da takwararta ta TUC da su janye matakin da suka ɗauka, inda ta ce hakan zai tabbatar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

    Sai dai da yake mayar da martani kan gargaɗin na hukumar DSS, a wata sanarwa da ya fitar, shugaban ƙungiyar ta NLC, Joe Ajaero, ya ce bai kamata hukumar ta yi wa ƙungiyar barazana ba amma ta mayar da hankali kan kame waɗanda ke son yin amfani da damar zanga-zangar don haddasa rikici.

    Shugaban ƙungiyar ƙwadagon, wanda ya bayyana matakin da ke tafe a matsayin “ zanga-zangar lumana kan tsadar rayuwa”, ya kara da cewa ƙungiyar ba za ta naɗe hannunta ba yayin da ‘yan Najeriya ke ci gaba da rayuwa cikin ƙunci.

    Ya ce “Mun damu da shawarwarin da jami’an tsaron ƙasar nan suka ba mu na cewa mu jingine batun zanga-zangar da muka shirya yi kan tsadar rayuwa da ba a taɓa ganin irinta ba duk da irin wahalar da ƙasar nan ke fama da shi, da hauhawar farashin kayayyaki, da taɓarɓarewar darajar naira inda dalar Amurka ta kai N1,900’’.

    Ya ƙara da cewa "A cewar hukumar, ya kamata a jingine zanga-zangar da aka shirya" domin zaman lafiyar jama'a ", la'akari da cewa zanga-zangar na iya zama tashin hankali da rikici duk da cewa muna da tarihin gudanar da zanga-zangar lumana.

  4. Jiragen yakin Habasha sun kashe mutane da dama a Amhara

    Ethiopian Army

    Asalin hoton, AFP

    Wani hari da jiragen yaƙin ƙasar Habasha maras matuƙa suka kai ya kashe mutane da dama a yankin Amhara, a cewar shaidu da majiyoyin asibiti.

    Rahotanni sun ce harin ya afku ne a ranar Litinin a kusa da wani ƙaramin gari mai suna Sasit da ke tsakiyar ƙasar yayin da wata babbar mota ke sauke fasinjoji .

    Tun a watan Afrilun shekarar da ta gabata ne sojojin ƙasar Habasha ke fafatawa da wata ƙungiyar 'yan bindiga da ake kira Fano.

    Mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa fararen hula kusan 30 ne da suka haɗa da mutane 16 ƴan gida ɗaya da ke dawowa daga baftisma da wani jariri, suka rasa rayukansu a harin.

    Wani Likita ya tabbatar da cewa mutane 18 sun samu munanan raunuka kuma uku daga cikinsu sun mutu bayan isar su asibiti.

    Rikicin dai ya barke ne a shekarar da ta gabata lokacin da hukumomi suka yanke shawarar rusa wata ƙungiyar sa-kai tare da shigar da haɗe ta cikin sauran jami’an tsaron yankin da na ƙasa.

    Gwamnati ba ta mayar da martani kan rahotannin harin na ranar Litinin ba.Tun a watan Agustan shekarar da ta gabata ne yankin na Amhara ke ƙarƙashin dokar ta-baci

  5. An kashe sojojin Rasha a wani harin makami mai linzami

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun ce aƙalla sojojin Rasha 60 ne suka mutu bayan da aka harba wani makami mai linzami kan wani wurin atisaye a gabashin Ukraine da aka mamaye.

    Majiyoyin da ke da masaniya kan lamarin sun shaida wa BBC cewa sojoji sun taru a wurin da ke yankin Donetsk domin tarbar wani babban kwamanda.

    Hotunan bidiyo na lamarin da suka bayyana sun nuna gawawwakin sojoji da dama da suka mutu.

    Wani jami'in Rasha ya tabbatar afkuwan harin sai dai ya bayyana cewa rahotannin lamarin ‘sun wuce gona da iri’.

    Rahotanni sun ce an kai harin ne sa’o’i kaɗan kafin shugaban ƙasar Rasha Vladimir Putin ya gana da ministan tsaronsa Sergei Shoigu.

    A wajen taron, Mr Shoigu ya yi bayanin nasarorin da Rasha ta samu a yankuna da dama na fagen daga, ya kuma yi magana game da ƙwace garin Avdiivka a baya-bayan nan, amma bai ambaci komai kan harin yankin na Donetsk ba.

  6. Tinubu ya naɗa sabuwar shugabar hukumar shige da fice ta Najeriya

    ...

    Asalin hoton, FACEBOOK

    Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin Kemi Nanna Nandap a matsayin Kwanturola-Janar ta Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS).

    Cikin wata sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale, ya fitar, ya ce naɗin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga Maris, 2024.

    Misis Nandap za ta karɓi aiki daga hannun Mrs Caroline Wura-Ola Adepoju, wadda wa’adinta zai ƙare a ranar 29 ga Fabrairu, 2024.

    Kafin naɗa ta a matsayin Kwanturola-Janar, Nandap ita ce Mataimakiyar Kwanturolan-Janar mai kula da sashen hijira.

    Sanarwar ta ƙara da cewa, shugaban ya yi hasashen cewa sabuwar shugabar hukumar shige-da-ficen za ta faɗaɗa gyare-gyaren da ake yi a hukumar da samar da ingantacciyar hanyar yi wa ‘yan Nijeriya hidima cikin inganci da kwazo.

    ''Haka kuma sabuwar shugabar za ta karfafa tsaron ƙasa ta hanyar samar da ingantaccen tsaro a kan iyakokin ƙasa da kula da al’amuran baƙin haure'', kamar yadda sanarwar ta bayyana.

  7. Yakubu Gowon ya buƙaci Ecowas ta gaggauta ɗage wa Nijar takunkumai

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon shugaban Najeriyar kuma shugaba ɗaya tilo da ya rage cikin waɗanda suka kafa ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka ECOWAS, Janar Yakubu Gowon, ya yi kira da a gaggauta ɗage duk wani takunkumin da aka ƙaƙaba wa ƙasashen Guinea da Burkina Faso da Mali da Nijar.

    Uku daga cikin ƙasashen huɗu sun nuna buƙatar ficewa daga ƙungiyar.

    Janar Gowon ya kuma yi kira da a gaggauta kiran taron ƙolin da zai haɗa dukkan ƙasashen ƙungiyar ta ECOWAS, ciki har da makwabtansu na yankin Sahel.

  8. Majalisar dattawan Najeriya ta yi watsi da cire tallafin lantarki

    ..

    Asalin hoton, Nigerian Senate

    Majalisar dattawan Najeriya ta yi fatali da shirin gwamnatin ƙasar na janye tallafin da take bayarwa a harkokin wutar lantarki, wanda hakan ke nufin kuɗin da ake biya na wutar zai ƙaru.

    Majalisar ta dauki wannan matakin ne a zamanta na yau Laraba.

    Sanata Abbas Iya daga Jihar Adamawa ne ya gabatar da ƙudurin wanda ya samu goyon bayan sauran sanatocin da suka halarci zaman na yau.

    A tattaunawarsa da BBC Sanata Ali Ndume ya ce babu yadda za a yi a ƙara kuɗin wuta ba tare da sahalewar majalisa ba.

    "Wutar da ba ma a samunta ta yaya za a ƙara kuɗinta, a haka ma ni inajin ana karɓar kuɗaɗen da suka wuce iyaka daga hannun alumma'', in ji dan majalisar datawan daga jihar Borno.

    Ya ci gaba da cewa a yanzu an fi dogara da wutar sola maimaikon ta Nepa saboda rashin tabbas da kuma tsadarta.

    ''Don haka babu yadda za mu bari wannan yunƙuri ya tabbata'', in ji sanata Ndume.

    Sanatan ya ce dole ne a ƙyale mutane su ji da yanayin da suke ciki na rashin abinci da kuma matsalar tattalin arziki.

  9. Majalisar Dokokin Ghana ta yi watsi da ƙudurin sassauta hukunci kan ƴan luwaɗi

    Nana Akufo-Addo
    Bayanan hoto, Shugaban ƙasar Ghana Nana Akufo-Addo

    Majalisar dokokin Ghana ta yi watsi da wani ƙudurin kwaskwarima da aka gabatar na neman sauya hukuncin da ake yi wa masu neman jinsi daga tsarewa a gidan kaso zuwa hidimar al'umma da kuma bayar da shawarwari.

    Mataimakin shugaban masu rinjaye, Afenyo-Markin, wanda ya gabatar da gyaran, ya bukaci a kaɗa ƙuri'a a asirce don tabbatarwa ko kuma kin amincewa amma aka katse masa hanzari.

    Ƴan majalisa a Ghana na muhawara kan wani ƙudirin doka mai cike da ce-ce-ku-ce da ya haramta neman jinsi da kuma tallata ayyukan ƙungiyar LGBTQ+.

    A halin da ake ciki, an ɗage muhawara kan ƙudirin zuwa gobe.

  10. Zaɓen fitar da gwanin gwamnan Edo bai kammala ba - APC

    Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta ayyana zaben fitar da gwani na gwamna a jihar Edo a matsayin wanda bai kammala ba.

    Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na kasa Felix Morka ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Talata domin bayyana matsayar jam’iyyar kan zaɓen fitar da gwani da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata.

    Jam’iyyar mai mulki ta ce za a gudanar da wani sabon zaɓen a ranar Alhamis domin tantance wanda zai tsaya mata takarar gwamna a jihar a watan Satumbar 2024.

    Jam’iyyar ta kira taron gaggawa na kwamitin ayyuka na kasa a daren ranar Talata domin warware rikicin da ya kunno kai a zaben fidda gwani da kwamitin Sanata Hope Uzodimma ya jagoranta.

    Morka ya ce, "a taron gaggawar da jam'iyyar tayi a yau Talata, 20 ga watan Faburairu 2024 domin duba kan batun zaɓen fidda gwani na takarar gwamnan jihar Edo, kwamitin gudanarwa ta tattauna batun sannan ta yanke shawarar cewa zaɓen bai kammala ba sannan ta tsaida ranar Alhamis 22 ga watan Faburairu a matsayin ranar kammala zaɓen fidda gwanin a jihar."

    Hatsaniya ta biyo bayan zaben fitar da gwanin da aka gudanar yayin da wasu ƴan takara biyu su ka yi ikirarin cewa su ne suke da tikitin tsayawa takara a jam'iyyar bayan da shugaban kwamitin shirya zaɓen Uzodinma ya ayyana Dennis Idahosa a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

    Jami'in zaɓen Stanley Ugboaja daga baya ya fito ya ayyana Monday Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaɓen duk da Anamero Dekeri yayi ikirarin shi ne ke da tikitin.

    Uku daga cin ƴan takara sha biyu da aka zaɓa domin tsayawa takarar zaɓen fidda gwanin sun janye kafin lokacin. Sun haɗa da Osagie Ize-Iyamu da Lucky Imasuen da kuma Ernest Umakhihe.

    Ƴan takarar da ba su gamsu da sakamakon zaɓen ba sun yi zanga-zanga a babban offishin jam'iyyar na kasa da ke Abuja.

  11. Shugaban Sudan ya sake yin watsi da tattaunawa da dakarun RSF

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban hafsan sojin Sudan, Laftanar Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya sake jaddada matsayinsa na baya cewa ba za a yi tattaunawar zaman lafiya da dakarun RSF ba har sai an fatattaki kungiyar ta hanyar soji.

    "Ta ya ya za a ƙulla yarjejeniya zaman lafiya da wanda bai amince da ita ba, kuma yana da ra'ayi daban-daban a kowace rana? Don haka, mun ce ba za a samu zaman lafiya ba har sai bayan an kawo ƙarshen waɗannan ƴan tawayen," Burhan ya shaida wa sojoji da sojojin kawance a wani sansanin soji a Gedaref jiya.

    "Ba za a yi wani tsari na siyasa ba har sai an kawo karshen yakin," in ji shi, a cikin wani faifan bidiyo da aka buga a shafin Facebook na sojojin.

    Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji da dakarun haɗin gwiwa ke shirin kwato jihar Gezira da ke tsakiyar ƙasar daga hannun dakarun RSF.

    Ana ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da RSF, wanda ya ɓarke a watan Afrilun 2023 a sassa da dama na kasar.

    Ya zuwa yanzu sama da mutane 10,000 ne aka kashe a rikicin tare da raba wasu miliyoyi da matsugunansu.

  12. MNJTF ta halaka ƴan ta'adda a ƙasashen da ke fama da Boko Haram

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar dakarun ƙasashen da ke yaƙi da ƴan bindiga MNJTF ta sanar da kashe ƴan ƙungiyar Boko Haram biyu tare da ƙwace alburusai a garin Mora na ƙasar Kamaru.

    Bayanin na ƙunshe cikin wata sanarwa jami'in yaɗa labaran rundunar, Lieutenant Kanar, Abubakar Abdullahi ya sanya wa hannu.

    Sanarwar ta ce a ranar 10 da 19 ga watan Fabarairu kuma, wasu ƴan Boko Haram sun miƙa wuya ga sojoji da ke Litri a Chadi da Doron Baga a Najeriya. An kuma gano makamai da alburusai a hannun ƴan ƙungiyar da suka tuba.

    MNJTF ta ƙara da cewa ƙoƙarin dakarunta ya sa an dirar wa wasu ƴan ta'addan da ke Bagasola a Chadi tare da ƙwato kwale-kwale uku cikin wasu kayan da aka gani a hannun mutanen.

    A wani samame na daban kuma a ranar 19 ga watan Fabarairu, sojoji sun gano wasu fanko da ake amfani da su wajen haɗa abubuwan da ke fashewar, an kuma dakusar da ƙarfin da ƴan bindigar ke da shi a yankin.

    A ranar Talata kuma, sojojin saman Chadi sun kai hari kan mafakar ƴan Boko Haram da ke kusurwar tafkin Chadi ta kudanci kusa da iyakar Chadi da Kamaru da Najeriya, lamarin da ya kai ga kashe ƴan ta'adda da dama tare da lalata makamansu. An kuma ga ƴan bindiga da dama na faɗawa tafkin daga kwale-kwalensu kuma ana tunanin sun mutu.

    A jamhuriyar Nijar kuma, sojoji sun tarwatsa wani yunƙuri na safarar makamai a arewacin Nguigmi kusa da iyakar Nijar da Chadi. Samamen da sojojin suka kai kan lokaci ya sa an kama tarin makamai - bindigar AK47 guda shida da ƙunshin alburusai da kwanson zuba alburusan.

    Sanarwar ta ƙara da cewa duk da waɗannan nasarori, sojoji biyu - ɗaya daga Najeriya, ɗayan kuma daga Chadi sun rasa ransu yayin da uku kuma suka samu raunuka.

    Rundunar ta MNJTF ta yi wa sojojin da suka rasa ransu addu'a inda ta ce ta duƙufa wajen samar da zaman lafiya da tsaro tare da inganta abubuwan da suka kamata wajen bunƙasa tattalin arziki da shige da ficen mutane ba tare da shinge ba a tafkin Chadi.

  13. Somaliya ta amince da babbar yarjejeniyar tsaro da Turkiyya

    ...

    Asalin hoton, TURKISH NATIONAL DEFENSE MINISTRY

    Majalisar dokokin Somaliya ta amince da wata babbar yarjejeniyar tsaro da Turkiyya.

    Karkashin yarjejeniyar na shekaru goma, Turkiyya za ta bai wa sojojin ruwan Somaliya makamai da horas da su tare da tura jiragen ruwanta a cikin ruwan Somaliya.

    Manazarta sun ce babban mataki ne na inganta tsaron tekun Somaliya.

    Firaminista Hamze Abdi ya ce yarjejeniyar ta kawar -a fadarsa - tsoron ta'addanci da fashin teku da kamun kifi ba bisa ƙa'ida ba da kuma zubar da gurɓataciyar shara.

    Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar Habasha ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya mai cike da ce-ce-ku-ce da jamhuriyar Somaliland mai cin gashin kanta, wadda ta ƙara fargaba tsakanin Mogadishu da Addis Ababa. (Somaliya, wacce ta ɗauki Somaliland a matsayin wani yanki na kasarta, ta zargi Habasha da take mata hakkinta).

  14. Senegal ta saki ɗaruruwan fursunonin siyasa

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Ministar shari'a, Aissata Tall Sall ne ta sanar da sakin fursunonin siyasa kusan 400

    Ministar shari'a ta Senegal Aissata Tall Sall ta sanar da sakin kusan mutum ɗari huɗu da ke tsare a gidan yari bayan kama su suna zanga-zanga.

    An kama su tare da garƙame su lokacin wata zanga-zanga da aka yi a watan Maris ɗin 2021 da kuma watan Yunin shekarar 2023.

    Ms Sall ba ta yi magana kan sakin shugaban ƴan hamayya Ousmane Sonko da kuma ɗan takarar shugabancin ƙasar Bachirou Diomaye ba .

    Ta kara da cewa, "abinda zan iya cewa shine ba haka kawai aka sako mutanen da yawa ba, an yi wa kowannensu shari'a ta daban bisa bayanan dake cikin takardu".

    Ministan ta ƙara da cewa an saki fursinonin ne domin kwantar ta tarzomar da ke tashi a kasar.

    Zanga-zanga a Senegal kan kai ga kame da kuma mace-mace a mafi yawan lokuta.

    Mafi kusa kusa shine mutuwar mutum uku a zanga-zangar da aka yi kan ɗage zaɓen shugaban ƙasar da aka shirya yi a ranar 25 ga watan Faburairu na shekarar nan. Ministan shari'ar ta ce ana cigaba da bincike don gano waɗanda suka aikata kisan.

    • Yan takara a Senegal sun buƙaci a yi zaɓe cikin mako 6
    • ƙasashe shida da dakarun Ecowas suka taɓa kai wa yaƙi
  15. DSS ta gargaɗi NLC kan ƙudurinta na shirya zanga-zanga

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi kira ga ƙungiyar ƙwadago ta NLC da ta janye ƙudurinta na shirya zanga-zangar gama gari domin samun zaman lafiya a Najeriya.

    NLC ta tsara shiga yajin aikin ranar 27 da 28 ga watan Fabarairu a wasu yankunan ƙasar domin nuna rashin jin daɗinta ga halin matsin rayuwa da ƴan Najeriya ke fuskanta da wasu matsaloli.

    Wannan ya zo ne yayin da kwamishinan ƴan sanda a Abuja, CP Ben Igweh cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta fitar, ya ce rundunarsa ba ta da masaniya kan zanga-zangar da ake shirin yi a Abuja.

    Sanarwar ta DSS ɗauke da sa hannun Daraktan yaɗa labarai na hukumar, Dakta Peter Afunanya, ta ce DSS ta samu labarin akwai wasu mutane da ke shirin yin amfani da zanga-zangar wajen tayar da husuma da kuma rikici.

    Sanarwar ta ce "an ankarar da mu game da shirin da ƙungiyar ƙwadago ke yi na gudanar da zanga-zanga. Yayin da hukumar ta ce haƙƙin ƴan ƙwadago ne su yi zanga-zanga sai dai ta yi kira ga ƙungiyar ta soke shirin domin zaman lafiyar al'umma.

    "DSS ta kuma yi kira ga ƙungiyoyin su tattauna a maimakon yin abin da ka iya tayar da hankali. DSS ta ce ta samu bayanai cewa akwai wasu da ke son yin amfani da damar wajen janyo matsala da tashin hankali. Lamarin, ba tantama zai ƙara dagula yanayi da halin da ake ciki a sassan ƙasar.

    "Abin da aka sani ne cewa gwamnati a matakai daban-daban tana ƙoƙarin warware matsalolin tattalin arziki a don haka, a ƙara ba su dama. Zuwa yanzu, hukumomin da suka dace na aiki ba dare ba rana tare da masu ruwa da tsaki domin bijiro da dabarun magance ƙalubalen da ake fuskanta. A don haka a basu dama su magance matsalolin da ake fuskanta.

    DSS ta ce ya kamata masu son yin amfani da damar su sake tunani ganin cewa karkata ga irin waɗan nan munanan tunane-tunane ka iya kawo maƙarƙashiya ga zaman lafiya.

    • Abu bakwai da gwamnatin Najeriya ta cimma da 'yan ƙwadago
    • Zanga-zangar da 'yan ƙwadago suka yi a sassan Najeriya
  16. 'Yaron da ya harbi malamarsa na iya fuskantar hukuncin manya'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar da ke gabatar da ƙara a Afrika ta Kudu ta ce wani yaro ɗan shekara 13 da aka kama bayan zargin sa da harbi da kuma raunata malamar makarantarsa da bindiga na iya fuskantar shari'ar manya.

    An tuhumi yaron ne da ba a bayyana sunansa ba da laifin yunƙurin kisan kai.

    Malamar ƴar shekaru 51 a halin yanzu tana murmurewa a cikin kulawa ta musamman a asibiti.

    Harbin dai ya girgiza mutane da dama a Afirka ta Kudu, inda ake ƙara nuna damuwa kan tashe-tashen hankula a makarantu.

    An zargi ɗalibin da amfani da bindigar mahaifinsa a harbin da ya yi a ranar Juma’a a wata makarantar firamare da ke Germiston a gabashin babban birnin Johannesburg.

    An kuma kama mahaifinsa da laifin sakaci dangane da makami kuma ana sa ran zai gurfana a gaban kotu ranar Talata, kamar yadda kakakin ‘yan sanda, Kanar l Dimakatso Nevuhulwi ya shaida wa BBC.

    A wata ziyara da ya kai makarantar a ranar Litinin, Ministan Ilimi na lardin Gauteng Matome Chiloane ya yi zargin cewa yaron ya rubuta jerin sunayen malamai uku “waɗanda ke ba shi matsala a makaranta.

    “Yayin da muka zanta da abokansa, sun ce an daɗe ana shirin wannan abu, ga dukkan alamu suna da dandali na WhatsApp inda suke tattaunawa da shirya wannan mummunan lamari."

    Ya yi zargin cewa ɗalibin ya ɗauki harsashi zuwa makarantar a wani lokaci da ya gabata.

    Yaron ko mahaifinsa ba su ce komai ba kan zargin.

    A ƙarkashin dokar shari'ar yara ta Afirka ta Kudu, ana tsammanin yaro mai shekaru 12 ko 13 ba shi da "ikon aikata laifuka" sai dai idan jihar za ta iya tabbatar da haka.

    Dangane da wannan harbin, biyo bayan buƙatar da hukumar shigar da kara ta kasa NPA ta gabatar, wani alƙalin kotun ya bayar da umarnin a gabatar da rahoto kan yadda yaron ke iya tantance abin da yake daidai da marar kyau da kuma tantance halinsa na ɗa'a da tunani da kuwa zamantakewarsa.

    Bayan wannan ne alƙalin kotun zai yanke hukuncin ko za a iya yi masa shari'ar manya.

    An yi hakan ne domin sanin hanyar da ta dace a ci gaba da shari’ar, kamar yadda kakakin NPA, Phindi Mjonondwane ya shaida wa BBC.

    • An tsare dan shekara shida da zargin harbin malamarsa da bindiga a Amurka
    • Kasashen da aka fi zartar da hukuncin kisa a duniya
  17. MDD ta ƙaƙaba takunkumi kan jagororin ƴan tawayen Congo

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Dubban mutane sun ɗaiɗaita sakamakon rikicin da ake a gabashin Jamhuriyar Congo

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙaƙaba takunkumin hana mallakar makamai da yin tafiye-tafiye da ƙwace dukiyoyin jagororin ƴan tawaye shida da ke Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo daidai lokacin da ake rikici a gabashin ƙasar.

    Cikin waɗanda takunkumin ya shafa har da kakakin ƙungiyar ƴan tawaye ta M23 da soja mai muƙamin janar da ke ƙarƙashin ƙungiyar FDLR sai wasu manyan jagororin ƙungiyar ADF.

    Sauran sun haɗa da shugaban gamayyar ƙungiyar kare ƴancin al'ummar Congo da kuma wani kwamanda na ƙungiyar Twirwaneho.

    Sanarwar ta biyo bayan taron kwamitin tsaro na MDD na ranar Talata wanda aka yi domin tattauna taɓarɓarewar tsaro a Congo.

    Congo na zargin Rwanda da marawa kungiyar M23 baya yayin da gwamnatin Rwanda ta zargi maƙwabciyarta da haɗa ai da ƴan tawayen FDLR da ta ce tana da alaƙa da kisan kiyashin da aka yi na 1994.

    Yayin taron kwamitin tsaron, mambobi sun yi ta yin allah-wadai da harin da M23 ta kai a baya-bayan nan a garin Sake abin da ya ɗaiɗaita dubban mutane.

    • China ta ki yarda MDD ta sanya wa sojojin Myanmar takunkumi
    • Trump ya yabi MDD kan takunkumin Koriya ta Arewa
  18. Kalli yadda rashin abinci ke hana yaran Tigray zuwa makaranta

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Sama da mutum 100 ne yunwa mai tsanani ta kashe a yankin Tigray na ƙasar Habasha, lamarin da ke tursasa wa yara ficewa daga makarantu domin neman ƴaƴan itace a daji da ganyayyaki domin ci.

    Wasu daga cikin yaran kuma sukan yi tafiya mai nisa zuwa rafi domin neman zinare a ƙoƙarin nemo hanyoyin kauce wa yunwa.

  19. Najeriya ta miƙa cibiyar samar da lantarki ta Zungeru ga ƴan kasuwa

    ...

    Asalin hoton, @Dolusegun16/X

    Gwamnatin Najeriya ta miƙa ragamar harkokin cibiyar wutar lantarki na Zungeru zuwa ga wani kamfani mai zaman kansa na Penstock Limited.

    An bayyana haka ne a taron farko na hukumar NCP da ke tantance kadarorin gwamnati da suka kamata a sayar a bana da aka yi a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

    Ana sa rai matakin zai inganta harkar samar da wutar lantarki tare da bayar da gudummawa sosai ga biyan buƙatun ƴan ƙasa game da makamashi.

    An cimma yarjejeniyar ranar 13 ga watan Disamban 2023 tsakanin hukumar kula da kadarorin gwamnati BPE da kamfanin na Penstock Limited.

    Bayan amincewar hukumar NCP, kamfanin ya amince ya biya kashi hamsin cikin 100 na kuɗin soma aiki ranar 5 ga watan Janairu.

    Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima wanda ya jagoranci taron ya bayyana ƙudurin gwamnatin tarayya na sake fasalta bankin tallafawa ayyukan noma domin haɓaka ɓangaren noma da samar da abinci a ƙasa.

    Da yake magana a taron, Shettima ya bayyana irin rawar da bankin zai taka wajen samar da abinci a ƙasa inda ya yi magana kan rassan bankin da ke yankunan Najeriya.

    ..

    Asalin hoton, @Dolusegun16/X

    • Yadda cire tallafin wutar lantarki a Najeriya zai shafe ku
    • Mene ne babban layin wutar lantarki na Najeriya kuma yaya yake aiki?
    • Kun san mazauna birnin da ke kukan wutar lantarki ta musu yawa?
  20. An kashe mutane da dama a yaƙin Isra'ila da Gaza – Yarima William

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Yarima William ya yi kira da a kawo ƙarshen yaƙin da Isra'ila take yi a Gaza ba tare da ɓata lokaci ba.

    Ya yi magana kan irin mummunan tasirin da yaƙin yake yi ga rayukan mutane a Gabas ta Tsakiya tun bayan da Hamas ta kai hari.

    Yariman na Wales ya ce akwai buƙatar a ƙara yawan kayan agajin da ake kai wa Gaza sannan kuma a saki mutanen da aka yi garkuwa da su.

    Kalamansa na zuwa ne yayin da ya kai ziyara ofishin ƙungiyar agaji ta British Red Cross a birnin London.

    Bayanai na cewa an sanar da gwamnati game da kalaman na Yarima da kuma ziyarar da ya kai ta hannun ofishin kula da harkokin waje da ƙasashen Commonwealth da kuma samar da ci gaba.

    Yariman ya ce "an kashe mutane da dama," wanda ya samu bayanai daga ma'aikatan agaji game da ƙoƙarin da ake na tallafa wa mutanen da rikicin ya shafa a Gabas ta Tsakiya.

    Ya halarci wani taro da aka yi ta bidiyo da ma'aikatan ƙungiyar Red Cross a Gaza waɗanda suka ba shi bayanan ayyukan da suke yi.

    Yariman ya kuma saurari irin gargaɗin da aka yi cewa rashin kai magunguna da man fetur na iya sa asibitoci su koma kamar maƙabartu sannan rarraba kayan jin ƙai ya zama ƙalubale saboda yadda wasu ke wawushe kayayyakin.

    • Yadda rashin lafiyar Sarki Charles III za ta shafi yarima William da Harry
    • Na kasance ba zan iya amincewa da kowa ba – Yarima Harry
    • Yarima Harry na Birtaniya ya zargi yayansa Yarima William da dukan sa