Ɗangote da Bill Gates na ziyara a Jamhuriyar Nijar da Najeriya

Shugaban Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum ya gana da shugaban Gidauniyar Bill and Melinda Gates, wato hamshaƙin attajirin nan na duniya, Bill Gates, da kuma shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ranar Litinin a birnin Niamey,
Mista Gates da takwaransa na Afirka Dangote sun kai ziyara Jamhuriyar Nijar da Najeriya ne domin ganawa da shugabannin ƙasashen da kuma abokan hulda game da ƙalubalen harkokin kula da lafiya da ci gaban ƙasa.
Kafofin yaɗa labarai a Najeriya sun rawaito cewa attajiran biyu sun gana da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu a Abuja, bayan sun bar birnin Niamey duk dai a ranar Litinin.
Rrahotannin sun ambato sanarwar da gidauniyar Bill Gates ta fitar ranar Litinin na cewa ziyarar na cikin kudurin attajirin duniyar na yin aiki kafada da kafada da al’ummomi da shugabannin ƙasashe don tallafa wa kirkire-kirkire da za su iya taimakawa wajen hanzarta ci gaba da inganta rayuwa a fadin Afirka.

Asalin hoton, Mohammed Bazoum Facebook

Asalin hoton, Mohammed Bazoum Facebook

Asalin hoton, D.Olusegun Twitter

Asalin hoton, D. Olusegun Twitter

Asalin hoton, D. Olusegun Twitter












